Breaking News

ZAFIN KAI 22

 22



*_Arewabooks@Mamuhgee22_*


Dagowa Anne tayi ta kalli Benazir da sumayyah tsawon mintina tana rasa tinanin kamawa kafin ta tsaida tinaninta akan Sumayyah dake dauke da juna biyun zatafisu zama cikin hadari idan suka fara cin dukan azaba.


Benazir ma tinaninta akan Sumayyah dake dauke da cikin yake sbd tsoron hadarin da zata iya shiga idan Ababa ya kasa controlling kansa.


Suna nan zaune akai sallar ishai suka miqe sukayi ba jira sbd basu sani ba ko idan ababa ya dawo zasu samu lafiya ko kuzarin yi din.


Hande ma miqewa tayi ta shiga dakinta tayo sallar 


Tana gamawa ta sake fitowa ta zauna tana hadiye wani yawun tsinkewa sbd itama tasan tau balain sai Allah idan ba har akanta zaa dora laifinba tinda itace ya barwa saka musu ido akan kowane motsinsu ta sanar dashi halin dasuke ciki


Amma ace har sumayyah tayi gogewar sani wani namijin har yayi mata ciki bata fahimta ba kuma da alama ba fyade akai mata ba da bazasu boye ba kuma da tini Ababan ya qaddamarwa wanda yayi fyaden ko dan uban waye gashi ciki yanzu ya dauko hanyar girma suna gida daya basuda labari,


Ababa kafin tashin masifarsa mamaki ma kawai ya isa ya kashe masa jiki shi kansa.


Qarfe tara saura mintina shida Ababa ya turo kofar gidan ya shigo yana amsa waya hannunsa riqe da ledar lemu daya siyo zai sha.


Ganin hande zaune tsakar gidan tana kallansa tana masa barka da dawowa yasashi taqaita wayar yayi sallama ya kashe yana saka wayar aljihunsa yana amsa barkan datake masa yana gaidata itama.


Satar kallan dakinsu Benazir tayi tana jin shakkar fada masa itama sedai kuma dole ya sani dan idan bata fada ba ciki dai baya boyuwa 


Ranar daya gansa da kansa idan ya qara girma kilan wuta zai cinnawa gidan ya kona su duka.


Shima dakin nasu ya kalla tareda bude baki ya daga murya ya kira sunan Sumayyah.


Lokaci daya a tare gabaki dayansu har Hande kansu yayi mummunan sarawa tareda bugawar zuciyar data kusa sakawa hande hearts attack sbd bata saba da wannan tashin hankalin tsoro da fargabar ba.


Su kuwa acan daki take jini ya tsinkewa Sumayyah mummunan bugawar da zuciyarta tayi tareda sarawar kai mai qarfi.


Benazir da Anne ma kusan kowannensu daqyar ya samu yawun hadiyewa sbd makoshinsu daya bushe take qam hakama yawun sun kafe basu ma ankara da jinin daya fara zubowa sumayyah ba wadda itama bata tsars lura da jinin ba sbd zuciyarta data tsinke.


Cikin mamakin rashin amsawarta da fitowarta ya juyo ya kalli Hande wadda ta kasa kallansa tana dan dauke kanta zuciyarta na sake shiga wasi wasin fada masa.


Kallan kofar dakin yayi yana matse fuska ya sake qwala kiran sunan sumayyar.


Daqyar da wani irin mummunan yanayi ta iya bude baki ta amsa kiran nasa tareda miqewa tsaye qafafunta na rawa ta nufi kofar


Sai alokacin su Benazir sukaga jini a kayanta da sauri Anne ta miqe tayi gaba Benazir ta tsaya bayanta suka sakata tsakiya sbd dare ne duk da akwai wutar nepa amma idan suka dan kakkare ba lallai yaga cikin ba harma da jinin sbd ba hijab jikinta tinda basu saba zama da hijab cikin gidanba sbd basuda sitira da yawa shiyasa suke lallaba wainda sike da.


Yanda suka jero masa kaman kashin awaki yasashi tsayawa da kyau yana kallansu cikin sake tsuke fuska da mamakin sabon salon nasu na samun guri.


Sun zuwa suka tsaya gabansa dukkansu kansu a qasa 


Anne ce kawai ta dan kallesa tayi masa sannu da zuwa cikin girmamawa kafin suma cikin girmamawa mai tsanani sukai masa barka da dawowa.


Ledar hannunsa ya miqawa sumayyah yana cewa


"Ki gyaro lemu ne ki kawomin banason manyan yanka kuma kin sani......Maganarsa yankewa tayi ganin yanda hannuwanta ke tsananin rawa gurin karban ledar.


Janye ledar yayi yana kallan hannuwanta dasuka sake rikicewa da tsananta rawa,


Fuskarta ya maida kallansa fuskarsa na sauyawa da mamaki yaga fuskarta na hada wani irin gumi da kasa motsa idanuwanta dan kada su dago.


Kan Anne ya maida idanuwanta yana kallanta itama zufan take cikinsa sharkaf hakama hannuwanta rawa sukeyi harma da qafafunta.


Juyar da kallan yayi kan Benazir datake a kame batai gumin ba amma yanda kirjinta ke bugawa yana iya gani da kuma yanda takasa dogowar itama.


Wani numfashi mai zafi ya sauke bayan ya gama karance yanayinsu duka


Ya dawo da kallansa kan hande zaiyi magana yaga itama a jiqe take da zufan yau itama takasa dagowa ta kallesa da kyau.


Sake kallan kowa yayi acikinsu daya bayan daya


Gurin yayi tsit ko sautin numfashinsu baka ji


gyara tsayuwa yayi a hankali,


"Meyake faruwa zaa fadamun yanzu nan"...sukaji saukar muryarsa kai tsaye.


Idanuwansa akan Hande suke sbd daga bakinta yake buqatan ji menene dayasa take hada zufa itama.


Kallansa hande tayi kafin ta kalli sumayyah data riga ta saddaqar su dikan ma sun saddaqar din.


Maimaita tambayarsa yayi hakurinsa na qarewa sbd tini kansa ya fara daukan zafi.


Wani nannauyan numfashi hande ta sauke tareda kallan sumayyah a karo na farko dataji tausayinsu ya dan saukan mata a rai sbd tasan suma duk yanda akai mummunan kaddarar samunsu tayi bada son ransu sbd yanda suke tsoro da kiyaye dokokin Ababa bazasu taba irin wannan aikin da ganganba.


Muryarta ba qarfi da kuzari ta bude baki tace


"Ciki ne a jikin sumayyah gashinan harya fito".


Shiru gurin ya sake dauka wanda wannan karan har dashi Ababan ya dauke wutar ba zata sbd saukan zancen kaman tsawa me qarfi haka ya jisa.


Hande dataji shiru dagowa tayi ta kallesa taga yayi shiru kaman baiji abinda ta fada masa ba dan haka ta miqe tsaye tana kallansa cikin dan daga sauti takira sunansa tana cewa


"Kaji abinda na fada kuwa?


Nace Ciki ne a jikin sumayyah gatanan na haihuwa,


Da alama kuma zekai wata uku koma fiye,


Kuma wallahi tallahi bansaniba sai yau dinnan nake kamasu suna maganar,


Duk ciwon datake ta fama dashi duk tsawon lokacin nan ashe laulayin ciki takeyi bamu saniba daga uwarta sai yar uwarta suka sani sunata boyan abinsu da saidai idan an haihu munji kukan jariri a gidan mu ankara.....


Ledar lemun hannunsa data subuce masa ce yasata yin shiru tana kallan lemun dasuka watse tsakar gidan kowannen na ganganrawa nasa gefen.


Rintse idanuwansu dasukai jajir dukkaninsu sukai suna sauke numfashi mai dumi.


Ababa ma numfashin ya ringa jerowa yana kokarin sanyaya wutar data kunno cikin zuciyarsa tana cin jininsa sbd yasamu fahimtar komai daki daki akan abinda handen ke fada sbd yasan dai ciki a gidansa ba magana me yiyuwa bace sbd soyayyama ya fada musu sun sani bame yiyuwa bace haka hukuncinta me girma ne,yanzu kuma yaji ana maganar cikin haihuwar dan mutum a gidansa,


Wannan ba labarin da zai taba yarda dashi bane sbd bame yiyuwa bane acikin gidansa dai Kuma a tsakanin yayan nasa.


Gyara tsayuwa yayi yana sake calming kansa sbd Kai tsaye zancen Mai shigesa ba kafin ya kalli hande yaga lafiyarta kalau da alama ba soki burutsun zancen take ba,amma ai akwai tsufa a tareda ita Kuma tsufa nasaka zance mara kan gado,


Da Annensu ce ta fada masa da sai yace haukartace ta tashi.


Benazir dayasan gidan kaf ita kadai ce me cikakkiyar lafiyar qwaqwalwa ya kalla kai tsaye yace


"Ke Benazir fadamun meye hande take fada,kuma komai nakeson ji dalla Dalla ba irin wannan rikicin zancen data fada ba yanzu Kuma idan kika yiwa kowane zance kwaskwarima gurin fada wlh saina karya wuyan uwarki gatanan a tsaye gefenki."


Mutuwa jikin benazir yayi ta sake boyayyan numfashi mai zafi sosai ta dan dago kanta kadan batareda ta kallesa ba ta bude baki muryarta na rawa ba wahalarda Kai Kai tinda komai ya Riga ya fito Kai tsaye tace


"Eh ciki ne wata uku".


Shiru gurin ya sake dauka suna jiran wata tambayar saidai tsit ababan baice komaiba sbd har lokacin dai Bai yarda da abinda kunnuwansa suke jiba Dan kuwa ko Anne ta dauka cikinsa a yanzu dukan tashi Kisha ruwan gishiri zai mata bare,


Sai daya Dan gyara tsayuwa ya sauke numfashi Yace,


"Annen ce da ciki kuke magana kokuwa"??


Shiru sukayi zuciyar kowannensu na kokarin Faso kirjinsu ta fito har handen wadda take sake qarewa cikin na sumayyah kallo ranta na tafasa.


Jin shiru yasa shi dagowa kallo daya yayiwa Benazir tayi qasa da Kai qafafunta na sake daukan rawa tace,


"Aa ba Anne ba"


Cikin zafi da tafasan Rai a hasalce Yace


"Waye yake da cikin Dan a gidan Nan ita kadai Ce aure"


Saida Benazir ta fixgi numfashinta Dake Neman daukewa sbd tsananin tashin hankali da tsoron dasuke ciki na tinanin Ko Basu rasa ransu duka ba Kila sai daya ko biyu sun tafi lahira sun bar daya muryarta na fita da karyewa tace


"Sumayyah Ce ta.... Bata qarasa ba sai jin tayi ya shaqurota da hannuwansa biyu yana kokarin rabata da numfashinta da karfin gaske cikin wani irin zafi da fushin da basu taba ganinsa dashi ba da murya me qarfi da zafi yace


"Zaki fadamun komai danace kokuwa uwar taki kike jiran na balla,


Cikin mutane ne kokuwa na aljanu?


Dan kuwa sai dai na Aljanu suka shafeta sukai mata shi.


Cikin azaba da neman cetan ranta dayake neman rabata dashi tafara wintsila qafafu tana Neman barin duniya idanuwanta take suka firfito suna neman rufewa.


Wurgi yayi da ita qasa tareda saka qafarsa daya ya take cikinta cikin masifar data saka Sumayyah sakin qaramin fitsari jinin dayake zubar mata yana dan qara gudu sbd masifaffen masifar datafi qarfin balain da sika saba gani.


Cikin wahalalliyar muryar da bata fita sosai Benazir tace


"Na mutum ne a makarant ta hadu dashi,


Yace ze aureta,bamusan da cikin ba sai daga baya.... Marin daya saka bakinta fashewa da jini ya sakar mata na bayan hannu, take ta kife a gurin kunnuwanta na dauke ji kwata kwata haka idanuwanta na ganin wasu irin taurarin wuta jinin bakinta kuwa kaman wadda ta fasa kai.


Sumayyar ya damqo yana kallan cikinta zuciyarsa na wata irin tafasar da shi kansa bai taba jin wuta irin wannan na ci a jini da zuciyarsa ba,


Kallan cikin ya tsaya yi yana rasa me zai mata sbd zafin da kansa keyi bayajin idan ya daga hannunsa ya dora akanta zai barta da rai.


Wlh Bai yarda mutum yayi mata ciki ba saidai Aljanu Dan kuwa Wanda ya taba ta kawai ma bare ciki ai bindigarsa zaisa ya fasa Kansa wlh saidai yayi prison,


Jikin bango ya jefata da qarfi tareda binta ya rufe da masifaffen duka yana nanata kalman cikin tareda qin yarda da cikin mutum ne a jikinsa.


Dukan dayake mata ne shi kansa bayaji baya gani yasa Anne da hande yunqurawa dan cetan ta sedai suna isa ya kama Annan itama ya rufe da dukan yana nanata kalmar ciki har wata uku a cikin gidansa.


Hande data ga 'dan nata ya zauce da gudu cikin tashin hankali tayi cikinsa ta riqesa tana fashewa da kuka tana cewa Anne da 'yayanta sun zautar mata da 'da da baqin cikinsu.


Tinda yake a rayuwarsa bai taba ji ko haduwa da abinda yake neman sakar masa bugawar zuciya ya mutu ba sai a wannan ranar.


Rawa jikinsa keyi yana fizga kaman dan taurin da aka kadawa gangar kirari.


Kuka hande keyi sosai sbd ganin halinda yake ciki ga Sumayyah da Anne kaman sun mace ba rai a jikinsu.


Benazir kuwa har lokacin jinta bai dawo daidai ba sama sama take jin ihunsu da hayaniyarsu hakama ganinta bibbiyu take gani.


Daki hande tayi dashi ta zaunar jikinsa na wata irin rawa Kansa na Neman juyewa yana cewa wlh gobe asibiti zai kaita sai an auna yagani zai yarda da cikine a jikinta na mutum tukuna yasan ma kalan matakin da zai dauka akanta da duk Wanda yakeda sani akan cikin aka boye masa da yanda ma aka samu cikin,saiya kashe wanda yayi mata cikin nan ko dan uban waye,


Sai ya daure zuriarsu kaf a gidan yari,


Sai ya buga musu tambarin da har zuriar su qare a duniya sai sun ringa tinasa da abinda sukai masa.


Hawaye hande keyi tana tsinewa koma waye da zuriarsa tareda tsinewa karatun nasu Sumayyah da sanadinsa suka hadu da wannan muguwar kaddarar.


#MAMUH#


#BENAZIR ABABA#KAATES#DD#DAWOOD DAUDA#CONTRACT#HOTLOVE#ROMANCE


ZAFAFA BIYAR🔥


-ZAFIN KAI


Mamuhgee


-TABARMAR 'KASHI


Safiyya Huguma


-FURAR DANKO


Billyn Abdul


-BAKON MUNAFIKI


Miss xoxo


Duka hudu 1k


Uku 800


Biyu 600


Daya 400


Pay at


1487616276


Access Bank 


Bilkisa Ibrahim


Send your Shedan biya Anan👇


09032345899


MTN VTU/MTN CARD/AIRTIME TRANSFER👇👇


09033181070


Yan Nijar kuma ga inda zaku biya👇👇👇


+22799643131


Zafafa🫶🔥🔥


23


*_Arewabooks@Mamuhgee_

No comments