Breaking News

Tabarmar Kashi Book 2 page 54

 *HUGUMA*




* TABARMAR KASHI *



Book 02Page 54


_Assalamu alaikum warahmatullah_


_Zan danyi wani qarin haske game da hukuncin jinin b'ari_


_Duk cikin da akayi b'arinsa gasa da kwana tamanin da daya,ya zamana a b'arin gudan jini ne ko jini ba wasu alamu na halittar dan adam ana daukan jinin da ya biyo baya ne a mazaunin jinin cuta,zakiyi sallah da dukkan ibadunki,me gida kuma yana iya zuwa miki_



_Cikin da yayi sama da kwana 81 sannan akayi barinsa,ko kuma cikin barin anga was alamun halitta kamar hannu ko qafa ko yatsa da sauranu,to hukuncinsa hukuncin jinin haihuwa ne_


_Jiya na sha'afa cikin rubuta na,cikin sãahar yana qasa da wadan nan kwanakin,duka duka bazai wuce kwana talatin ba,so kunga kenan sallah da sauran ibadu zataci gaba dayi,sannan me gida na iya zuwar mata,saidai ya danganta,wani yana da tsantsamin da bazai iya aikata wannan ba,wannan zabinsa ne,yana iya jira har ya dauke,ina fatan an fahimceni_




*Wallahu A'alam*



Duk yadda taso ta boye hawayenta,ko don kada ta bawa maji damar ganin rauninta amma ta kasa,tana jin zucivarta kamar zata fita daga qirjinta,duk wahalar da tayi?,duk shekarun data kwashe tana tanadi?,duk shekarun data diba tana qullawa tana kwancewa yanzu ya tashi a banza?, tayi wahalar banza kenan tunda har gashi maji ta dawo cikin rayuwar dan uwanta? lallai matar nan,da wadanne irin manya manyan bokaye take aiki da suka tsaya mata haka tsahon shekarun?, taketa wahala bata samu nasara dari bisa dari ba? ‚guntuwar nasarar kuma da take ganin ta sameta yanzun lokaci guda ta shammaceta ta sanya hannu ta tankwabeta?.



"ita kuma me ya sameta haka?" Maji ta fadi tana duban Mahmud kai tsaye, shima ita ya kalla


"Ban sani ba shifa,muna cikin magana da ita naga tana shirin faduwa" idanunu maji ta mayar kan hajiya

qaraman,ta santa ba qaramin sani ba,kalar kuka da

hawayen da fauziyya ke zubarwa a yanzu tabbas bana

banza bane. Miqewa tsam maji tayi tana maida dan

madaidaicin hijab dinta


"Hala ka gaya mata wani abune daya tayar mata da

hankali ko kuma yayi mata zuwan ba zata?" Tayi

maganar da sigar tambaya saidai kuma bata kalli dr

jarma ba tana laluben jakarta, don a yanzu ji takeyi ya

kamata ta fita zuwa dakin jarma din ko don idanun

fauziyya su sake gane mata abinda take tantama a

kansa,don tayi imanin labarin gizo baya wuce qoqi


"Wannan family matter ne, Allah yasa kaffara ce" ta fadi tana ratsa tsakaninsu ta fice a dakin. Hajiya qarama na kallon sanda Dr jarma yabi maji da kallo,ya kuma sauke ajivar zuciya lokacin da ya tabbatar dakinsa ta nufa,wani sashe na hanakalinsa yaji ya kwanta dari bisa dari.


A nutse likitan ya cire abun awon bugun zuciya

dake wuyansa,ya kuma fara tattara abun gwajin B.P

dinsa yana rufewa


"Jininta ne yayi mugun hawa lokaci guda,kuma dole ta

kiyaye abinda zai sanyata bacin rai,idan ba haka ba komai zai iya faruwa da ita,zata iya samun matsala a zuciyarta,kuma zata iya haduwa da paralyse". 


Bayanan na likitan ba qaramin girgiza mata zuciya sukayi ba, abinda ya sanya hawayenta yaqi tsayawa kenan,ta sake saka Dr jarma a gaba da kuka


"'Indai farinciki na kakeso yaaya da kuma lafiyata dole sai idan ka rabu da maji, har yanzu shifa bata qaunata" duban nadeeya data zubawa hajiya qarama ido dr jarma yayi


"Jeki tava mamanki zama nadeeya,ina zuwa" tsam ta miqe tana jin wani daci cikin zuciyarta,karo na farko fuskar hajiya qarama na komawa baqiqqirin a idanunta,ta dauka ita din me lallashin abbansu ne akan ya maida musu majinsu suyi rayuwa tare da ita kamar kowanne d'a da mahaifansa,sai gashi abun mamaki a gaban idanunta mommy qarama din ke cewa a saki mahaifiyarta?,me maji tayi mata?, ita da duka duka ko awa hudu basuyi da haduwa ba a yau din.


A nutse ya maida dubansa ga fauziyya dake ci gaba da aikin kuka kamar wata qanqanuwar yarinya,zuciyarta ja sake cika da mamakin yadda a yau yaya Mahmud din yayi funfurus da kukanta,abinda a baya baya taba iya jurewa kukanta koda na minti daya ne


"Fauziyya,yanzu ke bakijin kunya a gaban yarinya ki dinga fadin a saki uwarta?" Tambayar ta sake gigita tunanin hajiya garama,ta yungura zata tashi don ta kalli yayan nata da kyau, amma yadda kanta ya sara ya hanata aikata hakan,sai daga kanta tayi tana daga kwance ta kalleshi


"Yaaya, matsayina baikai ka saki shifa ba saboda ji?" Kai ya girgiza


"Komai ana yinsa ne saboda dalili, banga dalilin da zai saka na saki shifa ba, abinda nayi mata a shekarun baya ma kadai ba tare da qwaqwqwarar hujja ba har yanzu ina nadamarsa"


"Ba zaka iya sakinta ba yaaya?"


"Fauziyya ki kwanta kisha magani,ki daina maganar sakin maji a gabana banaso,karon farko da zan nema abu nima daga gurinki kenan" ta qarasa maganar yana danna wayarsa yayi kiran nadeeya.


Idanun nadeeya saman fuskar maji data hade yatsun hannunta guri guda,har yanzu tana jiran amsar tambayar data yiwa majin.


"Maji,don Allah ki gayamin,me kika yiwa hajiya qarama haka a rayuwarki?" Maji ta daga kanta a nutse tana duban nadeeya


"Idan nace miki ban sani ba zaki yarda dani?" Kai nadeeya ta gyada


"Na yarda maji, saboda tunda kike damu baki taba yi mana qarya ba,koda qaryar wasa kuwa maji" nadeeya ta furta cikin gamsuwa tare da yarda da kowanne furuci da yake fita daga bakin maji din.


_K'alubale a gareku iyaye,babu abinda yake matuqar ruguza rayuwa,ya sauke maka dukkan wani kwarjini da kima taka irin K'ARYA, duk wata matsala da muke fama da ita a yanzun ta fara ne daga gidajen aure,matsalar shugabanni na gari, matsi da wahalar rayuwa, daya daga cikin jigon matsalar itace K'ARYA,muna wani kuskure na yiwa yara qaryar "idan naje guri kaza zan siyo maka mota,ungo (bayan babu abinda zaki bashi)yiwa wata ko wani garya idan kuna hira bayan ke kanki kinsan qaryar ne,ko yiwa mahaifinsu qarya don ki kubuta daga wani laifi da kika aikata masa,wallahi irin wadan nan qananun abubuwan da muke rainawa su yara sukafi dauka tare da qoqarin kwatantawa,kafin kace meye wanann sai a wayi gari yaro ya zama shahararren maqaryaci, tun yana qarami yana ganin ba komai bace, zuwa sanda zai girma sai ya zama gagara badau a fagen qarya,qarya masifa ce,qarya masifa ce,tana iya sanyawa a tsani mutum,kamar yadda gaskiya ke siyawa mutum soyayyar jama'a,iyaye mu kula,mu raini 'ya'yanmu a cikakkun masu gaskiya da fadinta da aiki da ita,mu nuna musu ita kadaice hanya mafi dorewa da sanya rayuwa tayi dadi nan duniya da ranar gobe, Allah ya bamu dacewa,ya bamu ikon tarbiyyantar da su bisa tafarkin addinin musulunci_.


K'arar wayarta ta katse tunanin da kowannensu ya shiga,ta daga wayar Dr jarma din sannan ta ajjiye tana fadin


"Gani nan zuwa abba" saita waiwaya ga maji


"Abba na kirana,sai da safe maji" murmushi tayi


"Ki kwanta kiyi baccinki, bance kuma ki tanka mata da maganar ba,kici gaba da addu'a da tsare kanki" abinda maji ta gaya mata kenan,wanda har ta isa dakinsu tana juya maganganun a ranta.


Nadeeya din na fita ta shirya kanta tayi kwanciyarta saman sofa bed tare da qudundunewa a duvet,lokacin da ya shigo kwarjini tayi masa,ya kasa cewa komai da ita,ya sani ya mata laifi a rayuwarta me girman gaske, da ya tashi dawowa da ita kuma zucivarsa

ta kasa daurewa ya tsaya lallabata,ya biyo ta ganin

kakanta suka tilastata suka maida aurensu,ya sani dole

ya lallabata ya gama wanke laifinsa fes sannan su dora

daga inda suka tsaya,don cikin zuciyarsa yana jin kamar

yanzu ya fara son shifa din.

Yana zaune daga saman gadon, qafafunsa a

miqe yayin da ya jingina bayansa da fuskar gadon. Duvet

ya jawo ya rufe qafafun nasa zuwa qugunsa, idanunsa

nakan wayarsa da yake rage saqonni na mutane, sannan

fiye da rabin hankalinsa yana kanta sanda take gaban

madubi tana shafe skin dinta da mai tare da gyara jikinta

da turarukanta tausasa. Dagowar qarshe da yayi ya kasa

dauke idanuwansa daga kanta,sai ya sauke wayar daga

cinyarsa ya miga mata hannuwansa yana daga

zaunen, murya can qasa yace da ita


"Come closer" wani abu ne ya saukar mata a take, irin

abun nan da ba'a rasa kowacce diya mace dashi,jan aji tare da jan rai, iya kallonsa a gareta ya saukar mata da

wata kasala da yanayi a jikinta,wani abu me qarfi yana

buda zuciyarta ta qarfin gaske,sai ta fara takowa cikin

jan aji da yanga fiye da yadda ainihin tafiyarta ta halitta take,wanda ita kanta batasan hakan na faruwa da ita a

daidai lokacin ba.


Kasa jura yayi,ji yayi kamar ba zata iso ba,sai

kawai va vaye duvet din ya sauko gaba daya daga kan

gadon ya tako ya risketa a hanya. Hannayensa ya sanya ya zagaye bayanta dasu tare da matsowa da ita dab dashi a zafafe, fuskokinsu sukayi kusa da juna sosai, ta yadda kowa na iya ganin fuskar dan uwansa fes. Kallon kallo suka fara yi a junansu tamkar yau suka fara ganin fuskokin juna. Daga kan kyakkyawan girarta zuwa dogon hancinta me dan tudu da ya zauna sosai akan tsararriyar fuskar dake da shinfidadden kyau,ya zarto a hankali zuwa zaman lips dinta dake hasken lip gloss data dan shafa masa. Tsigar jikinsa yaji ta tashi,ya miqa yatsantsa saman lips din nata a hankali yana kewayeshi da su


"You're super hot!" Ya furta a hankali kamar me rada


"Kinsan kiss guda daya yana burning around 6colories a jikin dan adam?, do you want to workout with me?" Yayi tambayar yana dage mata dukka girarsa guda biyun?.


Wani siririn murmushi ne ya kubce mata ba tare data sani ba,murmushin da ya qara mata kyau, kyan daya sake ingizashi,ba tare da ya jira ta bashi damar da yaso samu tun farko ba ya hade bakinsu guri guda,ya dora lallausan lebansa saman nata ya fara yadda yaso dashi.


Wani irin abu ya shiga aikawa jikinta,kowacce gaba tata ta amsa,ta kasa kowanne motsi tana jin yadda yake sarrafa bakinta zuwa lips dinta cikin qwarewa kamar ya samu sweet,tsahon wasu mintuna kafin ya janye a hankali yana maida numfashi. Kasa hada ido tayi dashi tana jin nauyinsa yana saukar mata, hannuwansa yasa ya kamo fuskar tata a tausashe da sautin da koda kana cikin dakin babu lallai ka iya jin me yake fadi


"Kinsan meye?" Kai ta girgiza masa a hankali


"A da banason abu me zagi sam sam,but when i tasted

your lips,sai na zama addicted to sweet, because your lips are the yummiest thing in the world" kunya ce ta kamata matuga da gaske, kalamansa suna da wani irin girma da ko yaushe ya furta su sai ta jita kamar a wata duniya ta daban take, kalamai ne da ba gama gari ba qwaqwalwarta da zuciyarta basu tana amsar kalamai masu tsada da girma irinsu ba tsahon rayuwarta, ta rasa inda zata boye kanta sai kawai ta cusa fuskarta tsakiyar qirjinsa tana boyeta. Murmushi ya saki yana dora hannunsa saman tattausar sumarta


"Good!, duk sanda na nema gurin fakewa nima i will bury my face in your boo.....


.." Saurin miqewa tayi daga

jikinsa,tasan yanzun sai sake mata zancan da zai kusa sanyata narkewa a wajen. Ko taku guda bai bari ta qara ba ya dagata cak ya nufi gadon da ita yana cewa


"Muie na karanta miki wani abu" adan tsorace tace


"Am still bleeding" bai kulata ba sai daya direta saman gadon,fuskarsa dauke da sirrintaccen murmushin nan da ita daya take samunsa yace da ita softly


"So?,all i want is to feel you close to me,tell you my story and at the end watch you fall asleep in my arms,ba wani can gurin zan je ba" ya furta yana zare rigar jikinsa,sai kuma yayi mata rumfa da qirjinsa. Kunya ta sanyata mirginawa,sai yasa hannunsa ya birkitota bayan ya kashe hasken dakin daga nan inda yake ta hanyar switch din dake kusa dasu. Bayanta ya koma ya kwanta tare jawota cikin jikinsa


"Sanyi sanyi nakeji kadan kadan,let's cuddle so i can steal your body heat" kafin tayi wani motsi sai ta jishi yana cusa kanta ta cikin oversized shirt din data saka,kafin tayi wani yunquri tuni ya shige cikin rigar,ya zagaya hannunsa ta saman plate tummy dinta ya sake janyota sosai kamar me shirin tsaga jikin nata su narke su zama abu daya.


Sanda dumin jikkunansu suka gauraya waje daya sai wata ajiyar zuciya ta subucewa kowannensu lokaci guda


"I know the real KHADIJA SÄAHAR,but har yanzu bakisan waye MUHAMMAD TAUFEEQ na gaske ba,i will tell you duk da baki buqata ba,zan gaya miki ne to clear all the doubt and negative think" kunya taji da abinda ya fada,ya akayi yasan tana masa wani bahagon kallo?. Bai fira ta bawa kanta amsa ba ya fara magana da nutsatsiyar muryarsa.


"Kinsan waye mahaifina, qanwata da mamana,na taso hannun mommy qarama fauziyya tun ban gama mallakar hankalin kaina ba har na zama mutum, a lokacin na dan fuskanci rigonmu a hannunta akwai qalubale da matsaloli, amma duka mun shanye na kuma kula da nadeeya fiye da yadda nake bawa kaina kulawa har muka kawo yanzu. Na girma wani mutum na daban bawai ina yabon kaina ba,dukiyar mahaifina bata a cikin lissafina,komai ina lissafin yadda zan mallaki nawa ne na kaina,sai kuma na fuskanci wani abu. Fauziyya bata qaunar na mori komai daga mahaifina,ko yaushe tana cewa da ni da shi 'ka tashi ka nemi naka na kanka' sannan tana cewa da dr 'ka barshi ya nemi na kansa yasan zafin nema', a haka na gina rayuwata, kusan komai nafi sha'awar na yiwa kaina".


Duk yadda naso boye kaina daga mutane su fahimci ni din waye hakan bai yiwu ba, daukan kamanni da mukeyi da abban da kuma ganina cikin was lamuran nasa ya sanya yake wahala na shiga guri ba'a san wayeni ba. Cikin hakan abban ya bada gagarumin taimako ga wata organization ta marayu da iyayen marayu, a nan gurin ne naga AMEESHA.


Tana cikin layin wadanda zasu karbi taimako da

suke cikin matsanancin hali na rashin muhalli da

abinci,acikin masu karbar tallafin duka ta fisu quruciya

da qananun shekaru,abinda ya fara jan hankalina kenan a kanta. Komai ina qoqarin yinsa akan tsari, don haka a sannan ban tunkareta ba kai tsaye,sai da aka tashi taron nabi address da komai nasu na isa gidansu. Na tsaya na tabbatar da halin da suke ciki din kafin na gabatar da kaina a wajenta.


Murmushi naga tayi bayan na gama mata bayani


"Na ganka a wajen taro, ba kaine d'an Dr mahmud jarma ba?" A zahiri banzo da nufin gaya mata waye ni ba,to amma kuma bazan iyayi mata qarya ba,don haka na amsa mata da "eh nine"



Zafafabiyar

🔥🔥🔥🔥🔥🔥

No comments