Breaking News

Tabarmar Kashi Book 2 Page 53

 "HUGUMA*



_TABARMAR KASHI-


Book 02 Page 53



Mintuna kusan talatin ya sake fitowa,saita sake bude idonta kadan tana ci gaba da satar kallonsa. Daure yake da towel yanzun a qugunsa, duk wata siffa da gira da Allah yayi masa ta bayyana,idan tace tsahon rayuwarta bata taba ganin namiji me qira koda kusan tasa ba batayi garya ba,inda za'a dauko adam a tsayar dashi a gabansa,tabbas zai tashi kamar siffar jikin mace ne da kuma wani ingarman namijin.


Zame towel din da yayi ya sanyata maida idanunta ta kulle da garfi harda juya kanta wani sashen. Murmushi me sauti ya saki yana sane yayi hakan, tun daga shigowarsa har yanzun da ya fito daga wankan ya fahimci tana satar kallonsa


"Idan kin gama qaremin kallon ki tashi kiyi wanka,ki fidda wadan nan kayan ko zakiji dadin bacci" ya fadi yana sanya short necker sannan ya fara feshe jikinsa da tattausan turarensa mai kwantar da zuciya. Har ya gama bata motsa ba. Bai sake ce mata komai ba,sai ya taka cikin kamewarsa ya isa gareta sai kawai ji tayi an dagata cak


"Na daina magana biyu daga yau, komai zan vishi ne a aikace". Bai saurari magiyarta kan ya sauketa ba


"It's too late" yace da ita yana isa toilet din, sai kawai ya tsumbulata gaba daya cikin bathtub. Qanqame jikinta tayi guri daya


"Pleaaaaaaaassssseee" ta fada murvarta na rawa.

Murmushi ya saka yana fasa shiga cikin kwamin kwankan da yayi niyya,yaja da baya yana nufar qofa sai-kuma ya tsaya cak yana kallon dustbin din data jefa pad, har zaice wani abu sai kuma ya fasa ya sanya kai ya fita.


A reception na hotel din sajjad ya karba musu keys na dakunan sannan suka haura zuwa floor na biyu.


Migawa Dr jarma key din nasa dakin yayi cikin girmamawa sannan yayi gaba yana cewa nadeeya 


"'Muje ga naki key din" afifa da nadeeya suka bi bayansa.


"Shifa" Dr jarma ya kira maji wadda sai yanzu ta iskesu ganin tana marawa su sajjad baya. Tsaiwa tayi cak sannan ta waiwayo tana duban idanunsa. Nauyinta kadan ya kama Dr jarma


"Ga namu dakin, naga kina shirin bin yara"


"Eh tare dasu zan kwana" ta amsa masa kai tsaye. Kai ya girgiza


"Kada kiyi haka don Allah shifa,tsahon shekaru talatin ba wani abu,yau dai ki yarda mu hada makwanci, koda kwanan zaune zamuyi ni dake,aqalla ko hira mayi,ko bitar bayan rabuwa mayi"


"Dakai da wa?"


"Da shifa dina" ya amsa mata kai tsaye yana kallonta. Ta fuskanci lagonta yakeson karyawa,sai kawai ta dauke kai tayi gaba ba tare da tace masa komai ba. 


Caraf ya kama luggage dinta ya riqe,nan ma bata ce mas komai ba ta sakar masa tayi gaba abinta

Zare ido nadeeya ta hauyi da gain maji ta shigo dakinta,daga ita sai afifa ne kadai sukasan yanzun maji tana amsa sunan matar Dr mahmud jarma a karo na biyu


"Maji ai munyi sallama ko?" Harara ta watsa mata, dole ta tsuke bakinta ta bata qofa ta shigo. Tana kintsa dakin tana satar kallon majin, amma bata da bakin magana dole ta qunshe abinta a ciki, saidai gasan ranta tausavin abban nata sai ya kamata.


Kusan minti biyar yayi a tsaye a gurin rige da luggage din shifa data bar masa,jiki a matuqar sanyaye yaja luggage din ya bude dakinsa ya shige da ita. Yana shirin zama kira ya shigo wayarsa,koda ya duba sai yaga fauziyya ce,ya daga kiran yana zama saman stool


"Fauziyya ya akayi?"


"Wai yaaya ina kuka shiga?"


"'Meye ya faru?" Wani abu me daci ta hadiye 


"Yaaya,wanne irin mutane ne marasa mutunci cikin asibitin da fadeela ke jinya? kodai yarinyar ta shirya wulagantani ne kawai?"


"Wai meye fauziyya ya faru?" Ya fada cikin qagauta da jin gorafinta.


"Yanzu yaaya kamar ni?..…... ni fauziyya za'a hana shiga ganin fadeela? bayan na gaya musu matsayina a gurinsu? wai ba'a basu izini ba? wallahi yaya muddin kana sona kana kuma gaunata saika binciko wanda yasa a hanani shiga ganin jikata" ta fada da murya mai rawa dake nuna hawaye takeyi


"Yanzu kina ina?"


"(na Mercure hotel"


"Ki saki wannan dakin ki samu taxi,zan turo miki address din hotel din da muke"


"Tom" ta fada cikin zafin da ita kadai tasan yadda takeji a zuciyarta. Wayar ta ajiye tana furzar da iska,ta fara fahimtar fissafinta na neman wagajewa ne,a yanzun kuma tana buqatar nutsuwa qwarai tare da takatsantsan wajen fidda sabon takunta


"Bansan wanne kaidi ne zaiyi dai dai da abinda kika

aikatamin ba säahar, maji…...maji....bazan taba bari kici gaba da rayuwa kusa da yayana ba bare gaddarar sake zamowa matarsa a karo na biyu ya afka min ba". 



Abindata furta kenan tana kallon fuskarta ta cikin

madubi, zuciyarta kamar zata fito ta bakinta saboda

zallar bacin rai.


Da kansa ya fito bayan isowarta hotel din,ya sauka qasa ya shigo da ita. Suna shigowa veranda din nadeeya na fitowa a dakinsu


"'Mommy ina kika shiga ne tun dazun?" Harara ta ballawa nadeeya din,saboda a yanzun dan sauran tausayin nadeeyan da takeji wanda shine silar da yasa take daga mata qafa bata sakata cikin budget yanzun ya fara ja baya


"Sai yanzu kikasan da ni,saboda kinga uwarki ko?" Yar

Daria kawai ta saki,dr jarma da yanzu bayason jin zancan maji daga bakin fauziyya yace


"Nadeeya,maza ki cewa ummanki ta fito muyi sharing dakina,ke sai ku kwana da mummynku"

"Toh abba" Nadeeya da hakan ya yiwa dadi ta juya zuwa dakin nasu.

Wani razanannen kallo hajiva garama ta sakarwa dr jarma

"Yaava? va zaka hada dakin kwana da matar da ba halalinka ba? ka manta ba aure a tsakaninku shekaru kusan talatin?" A nutse ya kalli fauziyya din,karon farko sai mamaki ya mamayi zuciyarsa saboda tsananin tashin hankalin da ya gani saman fuskar fauziyya

"Kinsan dai ni musulmi ne kuma babu ta vadda zan aikata abinda yake Haram, ko 'ya'yana yanzun ba zasu barni ba, bare na jima da mallakar hankalin kaina"

"Kanaso kacemin ka maida aurenka da SHIFA?" Hajiya qarama ta jefa masa tambayar cikin matsanancin tsoron amsar da zata fito daga bakinsa.


Kai ya jinjina mata, kafin yakai ga bude baki yayi mata bayani har ta fashe da kuka me sauti sannan ta juya cikin sassarfa tana nufar stairs da sassarfa.

"Fauziyya,meye haka?" Ya fada yana bin bayanta da sauri. Gabanta yasha yana kallonta, mamaki yana sake kamashi tare da irin kukan da takeyi,kuka ne irin wanda yake fita kai tsaye daga cikin zuciya kuma bilhaqqi

"Wanne irin kuka kikeyi haka fauziyya?, na dauka zakiyi farinciki ki kuma taya 'ya'yanki murna akan daidaito da muka samu da mahaifiyarsu bayan shekaru masu yawa bama tare?" Yayi mata tambayar idanunsa cike da ayar tambaya. Cikin rai da zuciyarta gangar jikinta ta bata muddin batayi da gaske ba zata fallasawa kanta asiri

"Ba wannan bane damuwata ba yadda yaaya a watannin nan kai da toufeeg baku daukeni a bakin komai ba, tamkar ma kuna shirin fara juyamin baya, kunata al 'amuranku ba tare da shawarata ko sanina ba, saboda kaga qasa ta lullube idanunsu ummee?, wayyo ni Allah fauziyya,sai da girma yazomin sannan zan fara ganin ainihin abinda maraici yake nufi?,said.....

" Bata garasa fadin abinda tayi niyya ba qirjinta taji ya riqe kamar ana sukarta,kadan kadan ta fara jin jiri da wani irin ciwo da wani sashe na kanta ya riqe dashi,sai numfashinta ya fara mata wahalar jaa,abinda yaja hankalin Dr jarma kenan,.ya fahimci akwai matsala va matsa kusa da ita vana rigeta tare da tambayarta lafiya?. Tuni ta fara wani irin haki,Allah ya taimakeshi a sannan daya daga cikin ma'aikatan hotel din yazo wucewa.

Shi va taimaka masa suka rigeta bayan yay kira zuwa clinic na hotel din, aka dace akwai likita,kai tsaye suka nufi dakin nadeeya da ita.

Sanda suka tura gofar suka shiga nadeeya na tsaye tana yiwa maji nacin taje abbanta yana kiranta

"Nadeeya,wai yaushe na zama kakarki ne? ki fita a idona fa?" Kafin nadeevan ta sake cewa komai suka shigo da hajiya qaraman a rirriqe,sai maji ta mige tsam tana dubansu har suka kwantar da ita saman gadon, ma'aikacin hotel din ya juya ya fita don ya garaso da likitan.



Zafafabiyar

No comments