Breaking News

Tabarmar Kashi Book 2 Page 45

 




Book 02Page 45


"Na dawo daga office a gajiye, ina jin yunwa,inaso nayi wanka,amma duk baki lura ba, sai kawai ki bini da wata sannu da zuwanki me kama da bada umarni umarni?" Ya qarashe maganar yana lashe lips dinsa,hankalinsa na fusga akan nata lips din zuwa qirjinta da yaketa son rudar masa da tunani, rigar jikinta din doguwace sakakkiya,amma duk da haka akwai wata tattara a qirjinta data sake yiwa halittunta mazauni da kyau. Sake fincikota yayi sosai zuwa cikin jikinsa yana ci gaba da ifanta da wani narkakken kallo cikin qwayar idonsa


"You know what?" Ya fada yana hadiye yawu,ba tare da ya jira amsarta ba ya bata amsa yana sake jawota cikin jikinsa da kyau


"I swear i straight up forget my name for a second duk

sanda na kalli wadannan qwayar idanun" ya qarasa fada yana sanya yatsarsa tare da yi mata yawo dasu softly saman idanun nata, abinda ya tilasta mata lumshesu, tana jin tsigar jikinta na neman fara tashi


"Hold me so close for some minutes your breath already become my oxygen" ya fada yana kama hannuwanta ya kuma sanyata ta zagaye bayansa da su,sannan ya kama fuskarta a tausashe ya rige suna musayar numfashi me dumi dake fita daga hancin kowannensu.


Qafafunta ne suka fara rawa, ta fara gogarin zamewa,bai hanata ba ya barta ta janye,saidai bai barta ta matsa duka daga jikinsa ba ya rige hannunta


"Wannan shine kalan gaisuwar da nakeso bayan na dawo a office,zan shiga nayi wanka, kafin na fito please i want something to eat....am starving" tuntuni ta juya masa baya,a haka ta gyada masa kai tana addu'ar ya fita a kitchen din, tana tunanin zai fitanne tunda ya gama abinda ya kawoshi saita tsinci muryarsa cikin karyar da murva a shagwabe


"Please,my lips are so lonely one kiss please" har cikin bargonta taji tasirin muryar tasa. Qarasa rudata yayi,har spoon din hannunta na faduwa qasa,ya tsugunna ya dauka yana miga mata


"Matsiyaciya" ya fadi yana sakin wani tattausan murmushi hadi da soma takawa a nutse yana fita a kitchen din.


Bayan ta tabbatar ya fita din sai data samu guri ta zauna saboda ta daidaita bugun zuciyarta,idonta ta lumshe tana mamakin yadda yake yawan sanyata faduwar gaba da rudewa, abinda a baya Sam ba dabi'arta bane?.


Komai ta zubawa fadeelan har furar ma tace tanaso, sanann ta dawo ta shirya masa nasa saman wani kyakkyawan tray bisa tsari,sai taji kaman ta aikata fadeelan takai masa,amma kuma tunda ya fuskanci ya zama dan garari me neman dalili galilan ya moreta son ranshi,sai ta haqura ta zura hijabinta ta dauki tray din ta wuce dakin nasa tabar fadeela na kallo a parlor.


A nutse ta bude bedroom din ta shiga gamshin da yake fitarwa da sanyi suka buso mata,first night dinta da tayi da ranar Allah shi ya fara dawo mata fes a kai,ta dauke kai daga kan bed din ta soma takawa da gaggawa,tanason ajiye masa ta fice kafin yakai ga fitowa daga toilet din da take jiyo qarar ruwa. Har ta kusa isa qofar fita ya bude qofar bandakin ya fito


"Wait mana" ya furta yana dubanta, kamar ta zura da gudu haka taja ta tsaya sannan ta waiwayo da nufin ta samu gurin zama. Kadan ya rage bata fadi ba saboda tsabar rudewa,murdadden jikin nan nasa dake dauke da curarrun muscle ya bayyana muraran, gargasar dake lullube da jikinsa da damatsensa da suke fadin yadda mamallakinsu ke yawan daga qarfe, ba komai a jikinsa sai wani gajeran towel da ko cinyarsa bai gama rufewa ba don tabbas idan yace zaya zauna ne to kana iya hangen jikinsa sosai.


"Come and serve me masallaci zaki shiga ne haka na ganki da hijabi?" Ya fada cikin gatse, don ba haka yaso ganinta ba,yaso ya morewa kallonta ne sosai. Bata tankasa ba ta dawo gaban tray din


"Stop madam,ki cire wanann hijab din kada kiyimin gazanta" magana ce fal bakinta takeson maida masa, amma kuma tana tsoron kada allura ya tono garma,abisa dole ta hadiye ta zare hijabin yadda ya bugata ta fara saving nasa pancake


"Furar is enough" ya fada yana duba wayarsa da ya samu da tarin miscalls


Gida biyu hankalinsa ya rabu,rabi yana kan wayarsa rabi kuma tana ta fusgar hankalin nasa,so samu ace yanzun tana jikinsa yana shan duminta bai taba tunanin akwai ranar da wata mace zata dinga wasa da hankalinsa haka ba.


A nutse ta mige ta isa gareshi, dai dai sanda ya daga kiran dava shigo wayar tasa, miqa masa cup din tayi,ya miga hannu da zummar karba, kawai sai ya hade hannuwansu guri daya ya kuma jawota a tausashe yayi mata masauki saman cinvarsa tare da manneta da qirjinsa ya riqeta tsam. Ko motsi hanata yayi,cikin tattausar muryarsa din nan da yau tayi kusanci sosai da kunnenta taii ya ambaci sunan maji yana kuma gaidata.


A galla ya kusa minti talatin suna magana da majin,ita kuma tana zaune zaman cinyarsa,wata muguwar kunya na dawainiya da ita,duk sanda ta motsa zai zake maidata jikinsa va manneta gam, har ya kammala wayar sukayi sallama,ya aje wayar gefansa sannan ya tattara hankalinsa a kanta. Tallafo hannayensu dake riqe da cup din yayi ya matso dashi saitin bakinsa,sannan ya kamo daya hannun nata ya aza saman cokalin dake cikin furar, murvarsa gasa gasa cakude da alamun damuwa yace


"Oya...feed me please" ya furta kamar wanda ke tsoron wani ya jishi. Shi ya taimakawa hannun nata ta hanyar rigeshi, yana tayashi debowa tare kaiwa bakinsa. Wani irin shiru ya ratsa tsakaninsu,ba wanda ke cewa komai a tsakaninsu,sai jikkunansu dake hade,dumin fatar cinyarsa da towel din bai gama rufewa ba tana ratsa


saahar tare da haifar mata da wani irin vanayi a cikin jikinta. Shima baice komai ba har suka gama,sai ya sanya daya hannun ya sake dafe tafukan hannayenta yana kallon cikin idanunta tare da sauke wata ajiyar zuciya me nauyin gaske


"Na gode, Allah yayi miki albarka" har ciki tsakiyar ranta tali dadin addu'ar, batasan cewa shi ya fita jin dadin samun wannan kulawar ba, duk da sai daya tilastata kusan ya samar da ita


"Ameen" ta furta can gasan ranta amma kuma labbanta sun motsa


"Amma....kin saka an dakeni kuma an hanani kuka?" Ya fada yana langabe kai cikin wata shagwababbiyar murya data sanyata daga kai ba shiri, idanunsu kuwa suka hade guri daya,sai ya dage mata gira abinda ya sanyata saurin mai da kanta qasa


"Yes maji tace zakuyi tafiya tana neman alfarmata na barki ki tafi, batason kuma doguwar tambaya ita tasan inda zakin keda angel" ya qarasa fadi cikin yanayi na nazari.


"'Nima ina sake neman alfarma tare da rogon kauda duk wata tambaya daga ranka shakka ko kokwanto, khairan in sha Allah" har cikin bargonsa sautinta ya ratsashi, karon farko data masa magana da irin wannan salon, hashi kuma kusancin dake tsakaninsu ya bashi damar jin tone dinta tarrr


"Oh my god,repeat please,sake fadi" fuska ta tsuke,ta kuma shammaceshi ta mige da zafin nama,saidai ya rigata ta hanyar cafko hannunta


"Waye yace ki tashi?, haka kawai kin ciremin towel,oya mayarmin da abuna" sulalewa kawai tayi a wajen ta tsugunna tana curewa guri guda,ko kallonsa a haka ba zata iya sake yi ba bare ta gyara masa munafukin towel din daya dauro. Magiya ta hau masa


"Tashi kije" ya fada yana danne dariyar dake qasan ransa,da gaske yarinyar ta horu yadda ya kamata,inda dane da tuni yasha tsiwa da musu sau babu adadi. Koda ta fita waiwayawa tayi ta ballawa dakin harara tana jan awafa sannan tayi gaba


_niko nace a banza,ihu bayan hari kenan,idan yarinya ta isa tayi a gabansa mana ????

[04/10, 8:52 am] Mimah Yusuf: "HUGUMA*


No comments