Breaking News

Tabarmar Kashi Book 1 Page 65-66

  65

*HUGUMA*




* TABARMAR KASHI_*8



DON MARTABAR MANZAN ALLAH ME

FITARWA KIYI HAKURI KIYI HAKURI.


Hankalinta kwance tama manta da wani abu da ta yiwa labiban,ta gama shirinta tsaf ta canza kava,tana duba saqon afifa a waya da take gaya mata mahmud nason a bashi dama yazo ganinta,sai taji sallamar hajiya qarama cikin matsakaicin parlor din da daga shi sai hallway na dakunansu,don ba kasafai take fita babban falonsu ba indai ba kitchen zata ta shiryama fadeela abinci ba.


A nutse ta daga kai tana amsa

sallamar,kamar kullum hajiya qaraman cikin shigar alfarma dake nuna zallar alfaharinta take,labiba ce da tayi firgai firgai ke take mata baya,ta zamu daya daga cikin kujerun ta zauna idanunta akan sãahar tana karantar yadda yarinyar sam wani abu baya mata kwarjini ko va tsoratata


"Barka da safiya" ta gaidata cikin salon data saba gaisuwa,sai data gyara zamanta sannan tace


"'Barkanki,ya kwanan uktie?"


"Alhamdulillah ta amsa mata tana qogarin katse kiran dake shigo mata waya.


"Ya akayi kikayi gudun wuce sa'a haka da labiba.har kina shirin hallakata?" A nutse ta sake kallon labiba sannan ta maida kan hajiya garama


"Ni din?"


"Kefa" ta amsa kai tsaye tana kallonta,tare da mamakin yadda take bada amsa lokuta da dama kanta tsaye,kamar ba wadda ke aiki a qarqashinsu ba,ita din kuma sai ta gaza daukan kowanne hukunci koda da zazzafar magana ne,abinda bai taba faruwa ba tsakaninta da duk wani me hidima dake qarqashin ikonta.

Ajiye wayarta sãahar din tayi sannan tace


"To bansan sanda akavi haka ba,don normal driving nayi yadda na saba,saidai ko a idonta ne ya zamana gudun daya wuce qaida,asalima a waie na sauka nabar mata motarta ta qarasa shigowa da ita,kina iya tambayarsu idrith dake bakin gate" yadda tayi maganar a miqe kai tsaye yasa hajiya qarama duban labiba


"Wallahi qarya takeyi,jini na saura kadan ya hau" labiban ta furta kamar zata saki kuka


"Bansan waye me gaskiya a tsakaninku ba,sai kiyi haquri, tunda bakison hudu next time karku sake hada mota" baqinciki kamar zai kashe labiban haka ta juya ta fita, sãahar kuwa ko daga kai ta kalleta bata sake yi ba.


"Ina fatan magungunan nan sun qare kamar yadda na irgasu?" Hajiya garama ta fada bavan ficewar labiba,wayar ta kuma ajiyewa,ta dora idanunta duka cikin na hajiyan. Wani abu me qarfi hajiyan taji tattare dasu,sai ta zame ganinta tana cewa


"Kin zubamin ido baki amsamin tambayata ba" 


"Sun qare‚na yau kawai ya rage"


"Kin tabbatar?" Saita jinina kanta kawai ba tare data ce komai ba. Tsam hajiyan ta miqe tana mata wani kallo


"Yayi kyau,cikin satin nan ganwar mahaifin fadeela zata dawo rayuwa damu cikin gidan nan,banason komai ya canza daga cikin sharudan dana gindaya miki,and then....magungunanta duka zasu dawo hannuna,duk lokacin da zata sha ki kaimin ita tasha sannan ta taho,wasu lokutan tafiye tafiye na kasuwanci na suna kamani,idan hakan ta taso zan damqa su a hannunki ta yanayin daya dace" daga haka ta juva tana fita daga falon.

Kasa dauke kallonta sãahar tayi daga kanta,haka kawai a yau din wani qaqqarfan zargi ya taba zuciyarta,sai taji gaba daya zuciyarta tayi mugun matsewa da takurar son jin wanne matsayi hajiya qaraman ke dashi a gurin fadeelan.


Kusan zaman banza tayi a gurin,ta kasa tabuka komai,zuciyarta da kwanyarta nata jujjuya mata al'amura masu dama game da rayuwa,hango kanta ta dinga yi shekarun baya,lokacin da adam ya maidata mahaukaciya tuburan,ya dinga shayar da ita gubar allurai da magungunan da suka kusa sanyata amsa sunan mahaukaciyar me license ma,tsoro ya shigeta bayan wata zuciyar ta ayyana mata.

.. hajiya garama na

daya daga cikin masu wanna hali da dabiar.

Wani gumi ne ya karyo mata,ta yaya zata bari hakan ya faru da zuciya da ruhin da suke da rauni,salihar zuciya da kyakkyawan ruhin da basusan sabo ko cuta ba,sam sam....ba zata taba bada wannan damar ba,zata yi dukkan me yiwuwa ta katange fadeela daga dukkan wata cuta muddin ranta matugar ta samu kuma tabbaci da yaqinin abinda take zato din,sai inda qarfinta ya qare.


Sau uku baaba ramatu na wuceta,tun batayi magana ba harta tambaya


"Antyn fadeela lafiya kike yau kuwa?" Dan garamin murmushi ta saki tana gyara kwanciyarta cikin sofa


"Lafiya lau nake baaba, kasala kawai nakeji"


"Jiki da jini dama,to Allah ya garemu da lafiya"


"Ameen ya hayyu ya gayyumu" ta amsa mata tana maida idanunta ta lumshesu


Dawowar fadeela daga makaranta ne ya tasheta a wajen,yau gaba daya zancanta na dawowar sister nadeeya ne(haka take kiranta kamar yadda taji abby dinta wani lokaci yana kiranta da shi),ta hana sãahar yau sakat,alamu sun nuna akwai qaqqarfar shaquwa a tsakaninsu,bata samu hutu ba sai da suka kammala komai,ta hau google meet ta kira mata abby dinta,ta ja mata qofar dakin ta barta a ciki. Tun wancan ranar bata sake bari nasu take barin parlor din ko gurin,har sai ta

kammala sannan ta biyota tana bata labarin hirar da sukayi da abby dinta.


Tana kitchen tana hada mata abinci ta

shigo da gudu da tab din a hannun ta


"'aunty,don Allah sister nadeeya zaki kiramin" ta

fada a marairaice,murmushi ta saka ta ajjiye

wuqar hannunta,ta goge ruwan hannun nata

jikin towel,ta koma ta watsapp din da aka

budeshi saboda ita kadai ta kira matan,cikin

sa' a tana online sai ta miga mata ta koma aikin

nata,ita kuma ta juya da gudu ta fice.


Tun daga kitchen din take jiyo hirarsu da

dariyarsu,allai nadeeyan uwa ce da fadeela keyi da ita sosai. Har ta gama abincin ta

baro zuwaira hirar bata qare ba,sai ta wuce

dakinta ta daura alwalar sallar la'asar. Tana

idarwa fadeelan na shigowa rungume da tab

din,murya qasa qasa tace


"Sister nadeeya tace na kawomiki ku gaisa,nace abby ya hana sai an fara tambayar mutum tukunna,don Allah aunty nanny zaki gaisa da ita?" Murmushi ya subuce mata, fadeelan badai jin magana ba,saita miqa hannu ta kamota jikinta,ta karba tab din ta ajjiye a gabansu,fuskar nadeeya ta fito sosai a screen din.

Murmushi ya wadaci fuskar nadeeya, okaci daya da idanunsu suka gauraya waje daya kowa yaji wani abu game da dan uwansa


"Barkaaa" nadeeva ta fada tana waving hannayenta wa sãahar


"Barka kadai" sãahar ta maida mata itama cikin murmushi


"Yamma ne nan ko? to kin yini lafiya auntynmu?" Murmushi ya sake subucewa


sãahar tare da jin nauyin kiranta anty da nadeeya tayi tunda ko a ido kana ganinta zaka san sun kusa sa'anni da ita idan ma zata girme mata to da kadan ne

"Lafiya alhmdlh sister nadeeya,ya karatu?"


Cikin jin dadin sunan data ambaceta dashi da qaramar dariyar farinciki tace


"Karatu ya qare, in sha Allah nan da kwanaki uku ina tare da ku,nazo naga the world talented nanny dinmu" murmushin sãahar ta sakeyi


"Ma sha Allah,to Allah ya amince sisternmu" matsowa fadeela tayi tana sake zayyano mata dame dame zata taho mata da shi. Saahar din zata matsa don ta basu guri nadeeya tace 


"Don Allah karki tafi,yanzu kin fini iya ji da rigimammiyar 'yar nan,ki zauna kya tayani lissafa wadan nan kavan wasan da taketa fadi,ta dauka ni abbynta ce da zan mata tawagar kaya?" Ta fada tana dariya. Murmushi saahar ta saki,sai ta koma ta zauna,wayarta na hannunta ta hau watsapp tana duba kwantan sagonni;,lokaci lokaci takan daga kai ta kallesu cikin ban sha'awa da burgewa idan sukayi wani abun,duk sanda zata daga kan sai sun hada idanu da nadeeya,saidai su sakarwa juna murmushi.



******Washegari aka bude daya dakin da tun zuwan säahar din yana rufe,saboda me dakin wato nadeeya din bata nan. Dukka furniture din din ciki aka fidda,aka shirya sababbi,sannan aka maida mata kayanta ciki aka sake gyara dakin da kyau. Fadeela da suke tare da sãahar din ta kasa sukuni saboda murna,dole karatun ranar da ba'a yi ba kenan,sai ta barta.


*******Karfe hudu da rabi na ranar lahadin motar da take mallakin nadeeya ta shigo da ita katafaren farfajiyar gidan mahaifin nata.

Seatbelt dinta ta cire tana duban ilahirin harabar gidan,ita sam banda Dr jarma din yace lallai ta sauka a nan din,da sai ta gama kwanakinta a gida sannan zata zo gaidasu,sam zama a gidan koda na minti daya ne bai taba mata dadi ko kuma ya burgeta ba,bawai don bata samun kulawa ko wani abu na jin dadin rayuwa ba.


Oofar motar ta bude da kanta ba tare data jira tarin ma'aikatan dake yungurin mata hakan ba,fuskarta a sake,kasancewarta mutum itama me fara'a da haba haba da al'umma cikin kuma kulawa take amsa barka da dawowar da kowa keyi mata,bayan tafiyarta karatun data shekara hudu tana yinsa,wanda a shekara hudun sau biyu kacal tazo gida bisa tsarin yaa toufeeq da yace baison yawo,idan karatun zatayi tayi basai tazo musu gida ba


A haka ta gama gaisawa kaf dasu,sannan ta tuqe ga hajiya mansura dake tsaye tana faman doka mata murmushi


"Lale maraba da dawowar diyata cikin aminci"

ta furta tana yunqurin kamo nadeeya zuwa

jikinta. Kadan tadan zame tana murmushin

itama


"'Na sameku lafiya?"


"Wannan gaisuwar sai a ciki za'a yita,abbanku

yana toilet yana qarasawa shiryawa,muje cikin

tukunna" waiwayawa tayi tana bawa masu

aikin umarnin shigowa da jakankunanta


"A'ah,ai basai sun shigo dasu ba,zan wuce

gidan yaa toufeeq ne" fuska tadan bata


"Me zakiyi a can nadeeya?‚ga gidanku?"


"Fadeela nacan na jirana,zanfi jin dadin can

din" ta bata amsar tana takawa zuwa cikin

gidan rungume da wata jaka data sako kaya masu muhimmanci a mazaunin tsaraba wa mahaifinta. Baki galala da kallo hajiya mansura ta bita dashi, cikin ranta tana jin wani irin kishi yana kamata,a fakaice kamar anaso ne ayi wining a kanta,bayan tarin nasarorin da akaci a kanta,har yanzu wannan matar...

..wannan

mutum dayar ta gagara cimmata yadda ya kamata,tsakaninsu kar rasan kar ne, amma har yanzu qudurinta bai isa ga inda taso ya qarasa ba,MUTUM DAYA TAK! Ita ta samu dukka wasu damarmaki da taso ace ita ta samesu,duk da tayi musu nisan zangon da suke da imanin kasantuwarta a cikinsu abune mai wahalar yiwuwa,wannan ya rage garfi da kaifin wasu damarmakin nata ainun WACECE?!



AMSARKU TANA GABA_.



Juya cokali kawai takeyi cikin abincin da hajiya mansura ta gabatar mata,tana kuma amsa tambayoyin dr jarma. Gaba daya hankalinta bai waien, Allah Allah kawai takevi a tashi daga zaman cin abincin da akace an shirya da sunanta don tayata murnar dawowa,cikin ranta tana fata da addu'ar kada Allah yasa dr din yace ta zauna tare da su.


Yana tsame hannunsa itama ta tsame nata tana gogewa da tissue,haiiya mansura ta kalli plate din nata


"Ya haka kuma?,banga kinci komai ba"


"alhamdulillah ‚naci abinci a jirgi"


"Abincin jirgi wani abinci ne? ki zauna ki garasa ci, yanzu zan yiwa su taiba magana su sake gyara miki dakinki" tana gama maganar nadeeya na miqewa,ta goya jakarta tana duban dr jarma


"Abba zan wuce gidan yaa toufeeq,fadeela tun ina hanya tasa ake kirana"



"Alright,ki mintsinemin kumatunta ja'ira,tunda tayi sabuwar nanny ta rabu da zuwarmin, kullum kuma nayi kiranta cikin bani labarinta take,ki gaya mata nayi mata garin salary akan abinda ake biyanta,ina mata godiya da kyau da kyau,don da alama tasan aikinta sosai" murmushi nadeeya tayi,tana jin dadin yadda Dr bai hanata tafiya ba,sanann kuma ita kanta tana jin sãahar har ranta,duk da basu dade da sanin juna ba,amma tana jin tamkar ta dade da saninta.


Sai da taga sun dau hanyar barin gidan ta sauke ajiyar zuciya,koda ta yiwa dr alqawarin zasu zo suyi kwanaki da fadeelan,batajin zata iya wuce kwana daya ko biyu.


Guri hajiya mansura ta samu ta zauna bayan fitar nadeeya 


"'Dr inason magana da kai" kansa ya cire daga wayarsa da yake dannawa,daya hannun nasa kuma yana sakace da toothpick


"Nikam nace ba,bai kamata ace kana raye ba amma dukka yaran da Allah ya baka basa rayuwa tare da kai,ka tattarasu ka barsu a wani guri na daban,ni kaina da nake matsayin uwa a waiensu sam babu wata shaquwa a tsakaninmu" a nutse ya ajjiye tsinken sakacen yana dubanta


"Tohhhh...


...yau kuma wajen qarama dinne

ya koma wani guri na daban?,kin manta suna rayuwa ne garqashin gidan da toufeeg ya gina da kansa? nadeeya da ita tafi sabawa,a hannunta ta garasa girmanta, taoufeeq dinma kusan hakane,sannan shi namiji ne wanda banda gaddara da a yanzun yana qarqashin kulawar matarsa ne,so a ciki bansan meye matsalarki ba" ya qarashe maganar yana kafeta da idanu.


Ajiyar zuciya ta sauke,dama tayi zaton hakan daga gurinsa,yadda qarama ta tattare yaran gaba daya ta maidasu qarqashin mulkinta ita kadai yana mugun ci mata tuwo a qwarya,wanann dalilin ya sanya ta tattara labiba ta miga mata ko hakan zai sanya a samu wani sauyi,amma dai jiya i yau babu wani abu da ya canza


"Shikenan" abinda ta fada kenam cikin suyar zuciya ta miqe tana tattare gurin,zuciyarta kamar zata fito ta qirjinta. Binta shi kuma yaci gaba dayi da kallo,yana mamakin yadda har zata iya gaya masa wannan maganar akan qarama,ko ta mance cewa ta silarta ta sanshi?,ta silarta ta zama abinda take a yanzu take kuma amsa sunan da take amsawa na matarsa.


Dukka wannan shi ba damuwarsa bane,abu daya ya sani,duk abinda zai takura yaran ya sakasu cikin qunci zuciyarsa ko qangani bata so,muddin dai wannan abun bai kaucewa hanyar addini da al'ada ba,can qasan rai da zuciyarsa yasha kasa runtsawa cikin dare,he have feeling of guilt akan TOUFEEQ da NADEEYA,saidai har yanzu kwanyarsa ta kasa gaya masa meye ainihin tagamaimen laifin?,idan ya matsa da bincikar kansa kuma sai matsanancin ciwon kai ya saukar masa.


_uhmmmmm hmmmmm_


Turus ta tsaya cikin mamakin ganin cewa ba wani mummunan abu bane ya sameta sanadiyyar ihunta data jiyo tun daga toilet din dakinta. Suna rungume da juna ne ita da nadeeya kamar wadanda suka bace tsahon shekaru sal yau suke ganin junansu.

Nadeeyan ta daga fadeela tayi juyi tayi juyi da ita har babu adadi sai kawai sãahar din ta saki murmushi ta juya ta koma ta garasa abinda takeyi,saboda taga basa ganin kowa sai kansu,masu aikin gidan nata wucewa da kayan nadeeya din zuwa cikin dakinta



"Ya zaki tafi?,ki tsaya mana mu gaisa" muryar

nadeeya ta ratsa kunnensa sãahar dake

yunqurin komawa ciki. Waiwayowa tayi tana

murmushi


"Ai naga baku gama ba" ta fadi tana duban

nadeeva da take sake ganin wasu kamanni

saman fuskarta,tana ji a jikinta kamar ta santa

a wani guri daban kafin wannan lokacin.

Karamar dariya nadeeya ta saki tana

takowa zuwa inda säahar ke tsaye


"Indai nida ukhtie ne wallahi bakiga komai ba"

saita buda hannuwanta tayi hugging säahar

kadan tana murmushi yadda larabawa ke

marabtar 'yan uwansu


"'Fatan na sameku lafiya" ta fada tana janye

jikinta,fuskarta cike da fara'a



"Alhamdulillah"


"Tambaya ta farko,don Allah me uktie takeci ta fara kumatu?" Dariyar da sãahar bata shirya ba ta subuce mata,yadda nadeeya tayi tambayar tana riqe habarta da yatsarta,da alama da gaske abun yana bata mamaki,ko ba'a gayawa sãahar ba alamu sun nuna mata nadeeya mutum ce me barkwanci da faran faran da yawan surutu


"Ki nutsu ki huta,zaki ganewa idanunki" baaba ramatu ta bayar da amsar tana dariya


"En lallai to nima ko dole aci dani, bari na garasa" nadeeya ta fada tana daukar garamar suitcase din data rigo suka wuce ciki tare,saahar ta koma kitchen,fadeela tabi bayan nadeeya.

[06/09, 7:21 pm] Mimah Yusuf: 66


*HUGUMA*


* TABARMAR KASHI_*


DON MARTABAR MANZAN ALLAH ME

FITARWA KIYI HAKURI KIBAR MANA

KAYANMU


To kusan yinin ranar fadeela na tare da nadeeya,har sai da sãahar tayi mata dan biki


"An samu sister nadeeya an manta da ni ko?"

Dariya tayi,ta taho da gudu ta rungume sãahar din ta baya tana fadin


"A'an Aunty,sorry".


Duk da säahar din na dan basu guri tana Kame kanta a dakinta,amma duk da haka nadeeyan bata qyaleta ba,komai saita sanyota a ciki,kota biyota dakin ta fiddota,da dare ma sai gata da dalleliyar kaftan abaya ta mata me kyau da sulbi 'yar saudiyya


"Ga tsarabarki aunty nanny" sosai kyautar ta burgeta,ta kuma yaba tare da yi mata godiya.


Cikin sati guda kacal da dawowar nadeeya sukayi wani irin sabawa da sãahar,sabon da ita kanta sãahar batasan lokacin da ya faru ba,kafin cikar sati biyu sai suka zama tamkar wasu 'yan uwa. Abubuwa da yawa na kula da fadeela tare suke yinsa,idan tayi wani abun,wani abun nadeeya ce zata karba.

Wani irin qaunar sãahar nadeeya takeji har cikin ranta,bata sani ba,ko don bata taso da

'yar uwa sa'arta kamar sãahar din bane? to amma kuma akwai LABIBA da HASEENA,SU din kusan zata iva cewa sun dan rayu tare,to saidai ko kadan bataii abinda takeji game da sãahar ba,ko don ita din tana da wasu dabi'u

da kuma halaye tare da wasu qualities da bata

taba ganinsu daga gurin su biyun da suke

kamar sune dolenta ba?.


Zuwan nadeeva sai ya sanya itama ta dan

sake,takan fita zuwa gida tayi wasu awanni ta

dawo,a nan ne afifa ke tsokanarta,wai nadeeya

nason qwace mata faada,tayi maganar tana

dariya. Afifa tasan labarin nadeeya kaf daha

bakin säaharduk da basu taba ganin juna ba.

Murmushi kawai säahar ta saki


"Bestie,da alama har yau bakisan matsayinki a

guri na ba" hararar wasa ta jefa mata


"Na sani mana,tunda gashi har yau kingi

amsar mahmud yadda ya dace" zancan da ya

sanyata miqewa kenan,ta lalubi mayafinta tana

maida rolling din kanta 



"An ambato maqiyin naki ko?"


"No,kawai inason na biya a wankemin kaina sannan na wuce gida,yau na yiwa fadeela algawari zan dafa mata burabusko ita da nadeeya....tashi don Allah ki kaini,saiki saukeni a gida" gyara kwanciyarta afifa tay!


"Bazan iya ba,ki dauki motar ki kawai ki dinga amfani da ita"


"Kin manta ni din nanny ce?" Ta fada tana murmushi,don zuwa yanzun ita dadin sunan ma takeji,hakanan rayuwar da takeyi din tana bata wani irin nutsuwa,ta kauce daga idanun maza kwata kwata,gidan ya zame mata kamar wata mafaka


"Kina sauri ne kawai ki gudu kada ku hadu da abba" murmushi tayi tana maida agogon hannunta


"Duka koma meye zakice bazan musa ba,tashi don Allah kafin ya dawo mu hadu" hakanan afifa ta mige,ta dauko abaya ta dora saman kayan jikinta tanata mita,ta dauki key din motar tabi bayan sãahar din.


A kitchen ta tadda maama,tayi mata sallama,sai ta waiwayo tana dubanta


"Zo nan sãahar" ta kirata tana tsame hannunta daga ruwan da take wanke alayyahu,ta yiwa baaba rabi sign saita fita a kitchen din,ta barsu su uku


"Zauna" tace da ita bayan ta jawo kujeru guda biyu dake kitchen din ta zauna a daya.


Cikin mutuwar jiki kamar wadda aka yiwa tayin zama bisa garwashin wuta ta zauna


"Wannan rayuwar ba ita nake da muradin ganin kinayi ba,nafi bugatar ganinki a dakin mijinki kamar kowacce mace,kije ki sauya tunani ki kuma canza shawara" iya abinda tace kenan da ita.


Duk da kalmomin da tayi amfani dasu ba masu yawa bane amma nauyinsu ya cika mizani taf,jiki a salube ta mige ta sake iaddada mata sallamar sannan ta fito.


Tuni har afifa ta tayar da motar ta kuma barta a kunne saita shige seat din gaba ta maida murfin ta rufe,afifan tadan juya kadan ta kalleta,saita dauke kai ba tare da tace mata komai ba ta motsa motar zuwa gaba,ta saki hon kadan,baaba habu ya taso ya bude musu yana musu fatan sauka lafiya.


Suna gogarin fita a layin motar Dr mamman girema na shigowa,ya kuma gansu,don haka yasa driver dinsa yin slow da motar har suka hade a tsakiya,ya sauke Glass din motar yana duban afifa da idanunsa dake saye da gilashin garawa ido qarfin gani


"Sannu da dawowa abba"


"Yauwa sannu,ku dawo ciki,inason ganinku" hantar cikin sãahar ce ta kada,don bata manta da awa gudan da suka share dashi a waya ba wancan satin,yau din sai da tayi kamar ba zatazo gida ba,so amma zuciyartat a damu dason ganin maamanta,wannan dalilin ya sanyata fitowa.


A gofar gate afifa ta faka motarta kalli sãahar da gaba daya takejin wani rugugin tashin hankali yana sauko mata


"'Muie ko?"


"'Na shiga uku afifa,wallahi zancan mahmud ne" wani duba afifan tayi mata


"'To ai yayi kyau" da kallo tabi afifan,ganin yadda tayi hankalinta kwance bata ma wan damu ba,ga furta sunan Allah da qarfi tana runtse idonta da sauraron bugun da zuciyarta takeyi,ta bude murfin motar tabi bayan afifan.


Tuni har ya isa falonsa yana cire hularsa ya ajiye yana zare agogon hannunsa. Kamar kaiin da aka watsawa ruwa suka samu guri qasan carfet suka zauna,yanayin fuskarsa shine ya fadar musu da gaba tun baikai ga cewa komai ba,a yadda yake da sauqin kai da kuma haba haba da iyalansa,dole yanayinsa a yau ya sanyasu a fargaba.


Sosai ya zauna saman sofa yana maida bayansa ya jinginar da kujera yana dubansu daya bayan daya


"Aishatu" yayi kiran afifa da ainihin sunanta,kai tadan daga kadan sannan ta amsa


"Na'am abba"


"Me kike jira har yanzu baki gabatar min da mijin aure ba?" Shuru ta danyi tana dawurwura,saita rasa me zatace da abban. A halin yanzu tana da samari da a qalla sun kusa mutum hudu,kuma dukkansu da aure suke sonta,saidai babu wanda ta maida hankalinta a kansa


"Na sani nasan komai,saboda haka kije na baki wata uku ki karancesu ki fitar da wanda kikeso a cikinsu"


"' In sha Allah abba" dauke dubansa yayi ya mayar kan sãahar,a jikinta taji irin duban da yayi mata,wasu daga cikin maganganunsa kuma suka dawo mata


"Na miki alfarma na kuma daga miki qafa saboda banason na matsanta miki,na kashe miki gishirwar yin aikin duk da sam aikin bai dave dake ba,amma na barki kinje kinvi saboda babu haramci sai tarin lada a cikinsa..

... okaci yayi da zaki tsaya ki fuskanci

wanda yake sonki da gaskiya.


"Ummee,a ina maganarmu ta kwana? ya muke ciki?" Yayi mata tambayar da a waienta tamkar gatse ce.


"Abba‚bamu gama fahimtar juna ba" gafarsa daya ya dora kan daya


"Ta yaya zaki fahimci juna bayan akwai nisan tazara a tsakaninku?,to ni na gama nawa,na gama fuskantarsa,hatta bincike nayi a kansa,babu wata matsala tattare da shi,abinda kawai ya rage shine ke ki fuskanceshi,don haka daga yau yana da lasisin zuwa gurinki zance a duk lokacin da ya buqaci baka,sannan damar fuskantarsa da kike da ita wata daya ne kacal,daga lokacin duk abinda naga ya dace zan iya yankewa" sanda ya sauka a zancan yayi daidai da jin tsargawar gumi me dumi daga kowanne sashe na jikinta,sai take jinta kamar ba'a zaune take dai dai ba,batu fa abba yakeyi na aure a karo na biyu cikin rayuwarta,bayan ko shekara hudu cikakku batayi ba daga fita daga siradin data afka ba,tayi zaton saita debe shekara koma ma babu wanda yayi mata sha awar yin aure bare akai ga batun yi mata tayinsa


"Ku tashi kuje,Allah yayi muku albarka,banason kuma kowacce takai magariba a waje ba tare data nufi inda ta dosa ba"


"To abba" afifa ta samu damar fadi,yayin da sãahar keta qoqarin ganin ta mige ta fita a falon ba tare da an samu matsala ta fadi qasa

ba.


"Kaini nasarawa kawai,na fasa wankin kan" abinda sãahar ta fadi kenan tana kwantar da kanta jikin kujerar tana jin toro da fargabar hukuncin da abban zai iya yankewa a wata gudan daya deba mata


"Aure fa kenan,aure da mahmud,ta karba sadakinsa.ta amsa sunan matarsa,har ta hada shimfida dash.


"A'uzu bi kalimatillahit tammati min sharri ma khalag" taji bakinta yana furtawa bayan runtse idanunta da tayi. Kadan afifa ta waiwayo ya dubeta,sai ta mayar kan titi,a irin wannan yanayin ba kasafai ta fiya son yiwa sãahar din magana ba,don haka batace komai ba har sai da suka iso katafaren gate din gidan,tana shirin fita afifa tace da ita "Take care of yourself.... kada kie ki zurafafa tunani,kinsan dai kina da ciwon kai" kai kawai ta gyadawa afifan,ba tare dat waiwayo ba ta wuce kai tsaye zuwa qaramar qofar dake manne da gate din daha gefe ta fara knocking da wani irin sanyi da mutuwar jiki kamar wadda aka yiwa mugun duka.


Allah ya taimaketa sanda ta shigo gidan nadeeva tana tare da fadeela,ta jiyo kakacinsu a dakin nadeeyan,kamar ma game suke bugawa ita da ita,sai ta sulale ta wuce dakinta ba tare data bari sun ankara da dawowarta ba,don a yanzun kadaici kawai take bugata,batason hayaniya ko doguwar hira.


Kwance kawai tayi tana saqa da warwara,ba tabbatuwar aure a kanta ba,'ah....ambatar kalmar kadai tana sanyata fargaba da razani,wai ta yaya zata iya hada muhalli da wani d'a namiji kuma wai a kirata matarsa? iya wannan tunanin kadai juya mata kwanya yakeyi tare da gara sanyata a wata dimuwa da kuma damuwa.


Gab da magariba ta shiga wanka,ta fito ta shirya cikin wata lallausar riga me hade da wandonta,ta sanya hijab tayi sallar magariba,taci gaba da zama saman abun sallar,tana jin motsi da gilmawar nadeeya da fadeela,wani lokaci harda baaba ramatu.

Tasan ba lallai su san ta dawo ba,saboda duk wani qwan lantarki me haske ta kasheshi,sai dim light kawai.


Har nadeeya ta gota dakin ¡ilkinta ya bata kamar akwai mutum,saboda kana iya jin gamshin turaren sãahar me sanyi da baya buya yana ratsa qofar zuwa hallway din.

Komawa tayi da baya ta murda qofar,sai ta bude,ta sanya kai cikin mamaki bakinta dauke da sallama,sãahar dake shirin tayar da sallar isha'i ta dakata tana amsawa


"Antvn fadee,har yaushe kika dawo haka?,muna can muna jajenki,i called you several times amma ban sameki ba? mutuniyar tana can tana dakon dawowarkita kasa zaune ta kasa tsaye tun dazun‚bakinta da labari" dan lumshe ido tayi cikin murmushi


"Nafi awa da dawowa,na shigo ne banjin dadi shi yasa na kebe"


"Ya salam! me ya sameki?" Nadeeya tayi maganar sautin muryarta na nuna tsantsar kulawa damuwa da qauna


"It's not something serious,i felt relieved"


"Really?" Kai ta gyada tana murmushi,saboda ta hangi wani irin damuwa da kulawa da ita shigen na afifa


"Bazan gayawa faadee dinki ba,if not ta zama itace patient din,please zakiyi joining dinmu muyi dinner?" Kai tadan yada gefe 


"Banajin yunwa,amma zanyi qoqari ko ban fito dinner ba,zamu hadu kafin animan"


"Is okay,Allah yasa kaffara ne'ta fadi cikin mutuwar jiki ta juya ta fice tana jawa sãahar qofar. Ajiyar Zuciya ta sauke me qarfi,tana mamakin yadda suka damu da ita da al'amuranta a lokaci guda haka.


Sai wajen Tara na dare,dai dai lokacin kwanciya baccin fadeela sannan ta shirya ta fita don tayi mata shirin bacci,aikin kulawar ya rage mata sosai tunda ko yaushe nadeeya na kula mata da ita koda bata a kusa. Qaramin hijab ta zura ta fito a dakin.


Kasancewar qofar dakin bata kammala rufewa ba tun bata gama shiga ba ta fahimci video call sukeyi,duka ita da fadeelan na samon gado sunyi rub da ciki,sun sanya system din nadeeya din a gaba suna faman surutu.

[07/09, 4:25 pm] +234 703 451 7171: *HUGUMA*


No comments