Breaking News

Tabarmar Kashi Book 1 Page 63-64

 



Page 63


Sasai wuyanta ke cike da wani qatoton abu,sashen hajiya qaraman taso wucewa amma saita kasa,ta samu kujera ta zauna a nan farfajiyar gidan tana jan numfashi tana fesarwa,ba abinda ke gilma mata cikin idanunta sai kyakkyawar surarta,kamewarta da uban kwarjin da zai hana ta takata yadda taso. Ta yaya zaman wannan cikin gidan zai yiwu?,kuma a matsayin me kula da halittar da toufeeq yafiso duk duniya fiye da komai da kowa?,ta yaya zata bari su dinga gwama numfashi tare dashi?,anya idanun hajiya garama ba rufewa yayi ba kuwa harta amshi wannan surar a mazaunin nanny?.


Qafa daya kan daya tana kadata makeken gate din gidan dake da rassa biyu daya daga cikin reshen(enter) wato shigowa ya bude,ta zubawa gun idanu tana fatan hajiya qarama dince ta dawo. Ita dince kuwa,bata iya haqurin jumurin tsaiwar motar bama ta miqe ta bi bayan motar har zuwa parking lot na gidan,dai dai sanda motar ke tsaiwa,tasa hannu ya bude seat din baya wanda tasan a nan hajiya qarama din ke zama driver yana tuqata,ta shiga ta zauna idanunta akan hajiyan dake amsa waya da dukka hankalinta

"Nooo. karki damu MY BABY,duka duka watannin guda nawa ne? ki kwantar da hankalinki ki kammala karatunki,na miki algawarin duk lokacin da nazo bikin yayeku dake din zan taho,na miki wannan algawarin" girjin labiba ne ya buga,a duk sanda taji tana waya da BABY din,sai ta samu fargaba irin wannan,sunan da ita kanta me sunan ba qaramin barazana bane ga kunnuwanta da rayuwarta


"Alright.....kada ki damu da wannan,ki maida hankali kiyi karatu sosai ki fita da result din da yafi qarfin raini... okay,bye,i love you" saita katse wayar murmushi me kama da dariya kwance akan fuskarta,soyayyarta tana sake ratsata,burinta a kanta yana sake hauhawa,lokaci kawai take jira,kuma mutuwa ce kadai zata shiga tsakaninta da cikar wannan burin nata

"'Ya akayi labiba?" Ta waiwaya gareta bayan ta saka wayar a jakarta, numfashi ta ja ta hadiye yawu

"Mommy, nazo na samu andauki wata me kama da aljanu wai a mazaunin nanny"

"Shine me?" Tavi tambayar hankalinta kwance 


HA

"Mummy bakiga irin kyau da halittarta bane?,bakya tsoron ta rudi yaa toufeeq da kyan nata?" Qaramar dariya hajiya qarama ta saki

"Toufeeq..

. toufeeq dai? ke bakisan halinsa

bane halan har yanzu?,kin taba ganin idanunsa bisa fuskar wata mace da zummar so ko sha'awa?,bare har yaji tayi masa? inama yake toufeeg din?" Shuru labiba tayi tana juya maganar mommy din. Tabbas ko ita din iya tsahon rayuwarta zata iya irga sau nawa ya daga kai ya kalleta,kallon da mafi yawan lokuta yana mata shine don hukuntata idan tavi wani abu daya saba da nasa ra'ayin,sai taji wannan case din kamar ya mutu ne

"Mommy haseena zata dawo ne?" Sai data buda murfin motar ta saka qafarta waje sannan ta amsa mata ??

"Ba yanzu ba" ta fara qoqarin fita sai kuma ta dakata,shuru tayi kamar me nazarin wani abu,sanann ta fara magana da labiban a hankali

"Toufeeq allura ce cikin ruwa,me rabo ka dauka,so ki dinga sassautawa kanki wasu abubuwan kinji daughter" daga hakan ta saka gafafunta waje ta fita a motar tabar labiba a ciki.

Shuru tayi gumi na dan tsatstsafowa daga goshinta,mommy din tayi magana cikin kwantar da murya da kuma nuna kulawa,to amma kalaman dake qunshe cikin maganarta....sunyi mata wani iri,me rabo ka dauka?,allurar cikin ruwa?,duka me hakan yake nufi?. Shuru ta sakeyi tanason lallai saita fahimtar da kanta,amma ta gaza gano komai,tunda tace dawowar HASEENA ba yanzu ba,ta toshe duk wani kafa ta tunaninta,dole ta jawo qafafunta ta fita a motar don ta bawa driver din damar rufe motar,saidai a ranta tana jin ya kamata ta kira


hajiyarta ta gaya mata ko ita din zata gano abinda ta gaza ganowa.

Da daren ranar suna saman gadon fadeelan,bayan ta tabbatar ta bata magungunan da afifa ta rubuta ita kuma ta fita da kanta ta siyo. Ta shiryata cikin kayan bacci,kan fadeela na kwance saman cinyarta,gashinta me tsaho da santsi irin na saahar din ya baje saman gafafun sãahar din,ta nace wai sai sãahar din tayi mata kitso.

Itama ba iya kitson tayi ba sai kalba,don haka kalbar taketa qoqarin kitsawa amma tana warewa, kunnuwanta suna kan fadeelan daketa complain din rashin kiranta da Abby din nata baiyi ba. Kusan duk wayar da zaiyi matan tana gurin baaba ramatu,a can suke wayarsu su gama

"Abby yayi busy ne tabbas,amma ayi masa uzuri kinji,ki daina complain da yawa fadee,he cares about you fadee,you have to appreciate his efforts kinji" ta fadi ne don kawai kwantar mata da hankali tare da nuna mata muhimmanci haquri da kau da kai. Kai ta gyada a sanyaye,bata sake cewa komai ba.

Kamar jira kuwa akeyi tayi shurun sai tab din ta fara gara, zamewa tayi da gudu ta dira a gadon ta nufeta,ta iya karatu sosai,don haka ta karanta sunan me kiran

"Aunty,budemin google meet dina,abby ne a nutse ta sauka a gadon,ta dauko mata headphone da fold up stand,ta fara bata headphone din ta saka a kunnenta,sannan ta ware fold up din ta dora mata tab din a ciki don taji dadin amsa wayar,ta koma daga bayan camera din ta saita mata Google meet din.

Cikin qawatacce kuma tsararren balcony din nasa yake a zaune,wanda aka rabashi sassa biyu lounge and eating area qawace yake da wasu irin stone tiles da kuma couch masu tsananin laushi hade da table din dake da kujerunsa guda hudu,sai swing bench daga can gefe guda daya dake mahadin furniture din. Da wasu irin fitilu aka yiwa gurin ado,hakanan aka wadatashi da potted plants a kowanne sago da kuma qasan gurin,tsirran dake iva garawa gurin kyau iska me dadi da kuma qamshin furannin dake magale dasu.

Pajamas ne a jikinsa,farare tas tas dasu,rigar me gajeran hannu ce qwarai,v shape neck dake iya baka damar hango lallausar gargasar dake kwance lambam a girjinsa,hakanan gajartar hannun rigar yasa kake iya ganin dantsensa dake da wasu irin muscles,daga can gasa zuwa tsintsiyar hannun kuma gargasa ce itama me santsi baga sidik.

Wandon jikinsa iyakarsa gwiwa,yayi crossing gafafunsa yana jiran kiran da ya yiwa halittar mafi soyuwa a gareshi ya shiga,hannun damansa coffee dinsa yake sipping kadan kadan. Duka duka bai cika awa guda da dawowa daga office ba,ya sake maida kansa busy qwarai da gaske da tunanin hakan shi zai zame masa abokin debe dukka wata damuwa da kewa.


Miskilin murmushi ne ya subuce a labbansa sanda innocent face din fadeela dake zaune tsakiyar gado da hargitsatsen gashinta ta bayyana

"Assalamualaikum abby" sallamar tata ta ratsashi qwarai,ta kuma dace sosai da muryarta

'Waalaikumus salam,daddy's angel ta girma da gaske,an iya sallama da kyau‚barakallahu fiik"

"Abby,aunty nanny ce ta koyamin" sai ya jinjina kai yana murmushi

"Tace min tafi lada akan ace hello"

"'Da gaske ne" ya amsa mata yana gyara zamansa,ya buda baki zaice wani abu,saidai kafin yace komai din ta rigashi,ta barke da bashi labarin aunty nanny,abubuwan da take koyamata,abubuwan data hanata yi da wadanda ta gyara mata,karatunta da sauransu. Shuruuu kawai yayi yana bin bakinta da kallo tare da sauraren bayananta,yana tsintar abubuwa masu yawa game da labarin nanny din da take bashi,a hankali ya samu kansa da furta

"Alhamdulillah" a gasan zuciyarsa,tana sake gaya masa abubuwan da suke gudanarwa nutsuwa na sake saukar masa game da hannun da diyar tasa ta fada a wannan karon,abinda yake ta taraddadi kenan,sai ya gara sakewa sosai ya bata dukka hankalinsa yana sauraronta,cikin ransa yana jin mai yiwuwa Allah ne ya dubeshi ya share masa damuwarsa ya hada sanyin idaniyar tasa da nanny ta gari

"Kanason ka ganta? daddy na nuna maka ita?" Tayi gasa gasa da muryarta harda dan sunkuyowa screen din wayar alamun quima,tana maganar kuma tana satar kallon säahar dake tsaye bakin mudubi tana

taje kanta tare da gogarin hadeshi cikin

ribbon,fadeelan ce ta watsa mata kan a dasu garin cewa lallai saita koyi kitso itama a kanta.

Yadda tavi maganar da sunkuya da yin qasa qasa da murya ya bashi dariya,ya daga hannu yana shirin dakatar da ita,amma

inaaa... bata tsaya jin ta bakinsa ta juyar da screen din zuwa sashen da sãahar din ke tsaye tana daure gashinta da ya zuba har bayanta.

"aunty na juyo miki da camera kizo ku gaisa da abby na..." Wani muguwar faduwa gaban sãahar din yayi,tamkar wadda aka dasa taci gaba da baiwa camera din baya ba tare data juyo ba,ba abinda take tunawa sai kayan jikinta,inda Allah ya taimaketa doguwar rigace sakakkiya a jikinta,amma duk da hakan tasan tudun mazaunanta da kuma gashinta dake sake a baya yana lilo bazai kasa ganuwa ba,lallai ta yarda quruciya na damun fadeela sosai, banda haka ba wanda zaiyi irin abinda tayi.


Da sauri ya janye idanunsa daga kallon abinda baiyi niyyar gani ba,ya dunqule hannunsa sosai yana fadin

"Angel,move the camera,basai mun gaisa ba" kasancewar akwai headphone a jiki ya sanya ita daya take jin abinda yake fada,saita kyabe fuska tana fadin

"Anty na dauke camera din,yace basai kun gaisa bama" ido ya zubawa fadeelan sosai yana kallonta,can qasan magoshinsa yana qogarin harhada abinda zai fada mata,saboda ta sanyashi kallon abinda bai shiryawa ganin ba,dole ya mata bayani cikin hikima yadda zata fahimta,don ya fahimci ita kanta matar batasan zata juyar mata da camera ba. Zama yayi sosai yana fuskantarta,ya maida fuskarsa serious da zummar mata bayani da kyau,kada wataran ta sakashi ganin abinda baiyi niyya ba


"Fadeela"


"Abby"


"Kina iina?"


"En daddy"


"Daga yau idan na kiraki,idan bance ki bawa wani waya ba kada ki sake yin hakan kinji?" Kai ta gyada a sanyaye


"Kome zaka yima mutum saida izninsa,kinga yanzun ba hijab ko dankwali a jikinta,kuma ba kyau aga mutum a haka,kin saka mata camera,kinga ba zataji dadi ba ko?" Kai ta sake gyadawa da alamu jikinta ya mutu


"Good girl,idan mun gama waya ki bata haquri" 


"In sha Allah" sai murmushi ya sake subuce masa,in sha Allah din kamar a bakinta aka radata,bai taba jin ta fadi ba,kamar wata babba,amma yanzun data fada sai yaji wani sanyi a ransa


"Khairan in sha Allah" ya fada a ransa yana jin hope sosai akan sabuwar nanny din fadeelan.


Tunda ta fahimci ta janye camera din sai ta koma gefe ta zauna tana maida numfashi, wani abune da bata taba zata ba shi yasa ta razana,wayarta ta jawo ta buda don rage zaman da bugawar da zuciyarta keyi akan abun,tana danne danne tana kiran sunan

Allah,har batasan fadeela ta kammala wayar ba,saijin mutum tayi tsugunne gabanta


"Aunty,am sorry,abby yace na baki haquri,na juya miki camera without your permission" ido ta zuba mata,sai ta murmusa ta sanya hannunta ta dagota ta dorata kan cinyarta 


"Abby yace babu kyau kada na sake" kai ta jinjina


"Abby dinki is a good person,gaskiya ya fada,na haqura nasan kema ba kina sane bane ko?" 


Kai ra gyada mata tana murmushin jin dadin yabon da ta yiwa mahaifinta,riqe hannunta tayi suka miqe

"Oya,muje a kwanta,gobe da school,next week kuma zaku fara revision,sai C.A then exams ko?


"Yes" ta fada tana murmushi


"Abby yamin alqawura da yawa,yace ya gaji da ganin third position,da second yakeson ganina,if possible ma first,idan na kawo first din kuwa,sai ya gyada kai,nasan abby naidan ya gyada kai baice komai ba.....hmmmmm,zai baka mamaki ne,anty ki tayani addu'a na samu first position" ta garasa maganar tana

marairaicewa dai dai sanda sãahar ke lullubeta

da duvet.

Murmushi ta saki,ta kama hannunta ta rige

cikin nata

"Kiyi karatu sosai kiyi addu'a da yawa,you will pass in sha Allah, kuma duka zan tayaki fadee"


qanqameta tayi tana dariya cikin jin dadi

"Na gode aunty nanny"


Shuru yayi idanunsa akan system dinsa

bayan sallama da fadeelan,hannunsa rige da

dan qaramin spoon yana ta juya tea din da

already ya riga ya gama juyuwa,ya rasa me

yake tunani,hirarsu da fadeela....abubuwan

da yaji.

.ko abinda ta nuna masa bai shirya

gani ba?, Sai kawai ya zame hannunsa daga

tea din,ya mige yana zuba hannuwansa dukka

biyu a aliihun wandonsa yana furta "La haula wala quwwata illa billah" tattaki yayi kadan ya matsa gaban balcony dinsa,ya zube idanunsa a gurin yana kallon jerarrun tsirran dake gurin suna rayuwarsu hankali kwance,duhun dare da hasken fitilu suna sake qawata ganin mutum. Qarar wayarsa ta sanyashi waiwayowa,ya zubawa wayar ido yana karanta sunan NADEEYA cikin ransa,sai data kusa katsewa sannan ya daga ya sanyata a kunnensa yayi shuru ba tare da yace komai ba.

[05/09, 6:07 am] +234 902 488 9500: *HUGUMA*


64


* TABARMAR KASHI_*


Page 64


"barka da warhaka yaa toufeeg" daga can daya sashen aka fada cikin d'ari d'ari,kamar me tsoron yin magana


"Barka" ya fada a dake kuma a taqaice


"Ya aiki yaa?"


"'Alhamdulillah" ya sake amsa mata a taqaice,duk sai taji ba dadi,saboda ba haka suka saba yin waya ba,ba kuma da irin wannan yanayin yake magana da ita ba,duk da ta saba da miskilancin sa,amma yanayinsa na yanzu ba dashi suka saba magana ba


"Yaaya upper week zan dawo gida,finally na gama exam dina,zaman canada ya qare"


"Good.....ina miki murna" ya sake amsa mata a taqaice. Marairaicewa tayi zuciyarta na karyewa,tamkar tana a gabansa


"Am sorry yaaya"


"Sorry for what?" Yayi tambayar hankali kwance kamar dai da gaske baisan abinda yake faruwa din ba


"Yaaya,nasan kasan nayi maka laifi,amma wallahi it was not my fault,tanata sakamin pressure akan tanason ganin FADEELA..


"Ki gaya mata,ta sanya a ranta bata haifi wata 'ya ba a duniya kwata kwata,fadeela a yanzun ba jininta bace" yayi maganar cikin zafi tamkar itace a gabansa. Laqwas NADEEYA tayi cikin toro da firgicin jin sautin muryarsa mara hayaniya lokaci guda ta cika da kauri.

Iska yadan furzar yadda nadeeya din tayi shuru ya tabbatar masa ta tsorata da yadda yay maganar ne,sai ya lumshe idonsa yana gogarin yiwa kansa saiti,bayan ratsawar shuru na wasu sakanni sal yace

"Ticket din wacce rana kikayi booking?"


"Sunday" ta fada a sanyaye


"Alright,zan dawo miki da abinda kika kashe,don nayi fushi bashi zai baki lasisin yiwa kanki wata hidima ba,don't tray to buy anything da kudinki,as long as iam alive"


"In sha Allah" ta amsa masa a sanyaye, zuciyarta cike fal da qauna da kuma soyayyarsa,irin zallar soyayyar yan uwantaka,wadda babu algus a ciki. Labarai kadan ta bashi suka katse kiran,don ta fuskanci yanayinsa kamar he's not in mood.

Ya jima da wayarsa a hannu yana jujjuyata ba tare da iya yin komai ba,haka kawai wasu abubuwa na rayuwa suke dauko kansu suna kawo kansu da kansu gabansa,rayuwarsu yadda ta gudana shi da

'yaruwarsa,shekara kusan ashirin da biyar baya.


Ajiyar zuciya hade zazzafar iska ya fesar,ya sake juya wayar a hannunsa sannan ya lalubi number hajiya qarama.


Tashi tayi ta zauna sasai tana cire hankalinta daga lissafin ribar kayan data kawo daga china da suka samu qarewa,ta


bada dukka hankalinta akan wayar ganin me sunan,tayi gyaran murya sannan ta saka wayar a kunnenta.


"Barka da dare"


"Barka kadai,yanzu yanzu na shigo daga gurin mutuniyar,suna can ita da nannynta suna shirin bacci"


"Ummm,yayi,batun nanny dinne dama na kira,nawa ta buqaci albashinta?" Wuyan rigar lace din jikinta ta gyara


"Har yanzu taqi fadin nawa,ni bansan kalar nanny din da muka samo ba wannan karon,nayi mata zancan kudin amma sai tacemin ba komai,aikin yafi kudin muhimmanci" gyara zamansa yayi,shima maganar ta dan bashi mamaki


"'Noo,ta fadi ko nawan ne,sai a yiwa elyas magana,a dinga cire mata on time " yayi maganar ne har qasan zuciyarsa, yana lua hangen canji qarara daga fadeela,a yadda zuciya da ransa sukayi masa dadi,yana ganin ko nawa ne ta bugaci a biyata baiyi tsada ba


"Okay,i will talk to her'


"Yayi' ya amsa a kasalance,tanaso su tattauna wasu abubuwa amma ya bata uzurinta,sai tayi masa addu'a sosai sannan ya katse wayar,ya jefara gefe yana jin dukka gabban jikinsa suna sake zama weak,don haka sai ya kwashe wayoyinsa yabar dukka sauran tarkacen a gurin, saboda akwai wadanda xasu gyara gurin,komai kuma su sanyashi a muhallinsa.

Wanka yasoyi daya dawo amma saboda ya kira fadeelan baiyi ba,don haka yana shiga ya zare kayan jikinsa,ya lullube murdadden jikinsa da babban lallausan towel. Minti talatin kacal ya fito yana qamshin shower gel,da hair shampoo dinsa me tsada da yake amfani dashi waien wanke sassalkan gashinsa da ko yaushe yake cikin daukar idanu da hankulan tarin matan da shi kansa baisan adadinsu ba,saboda mafi yawansu bashi da masaniya akan fadawar da sukayi cikin matsananciyar soyayyarsa. Mintuna sha biyar ya gama shirinsa,a hakan yayi sauri akan yadda ya saba,don shirinsa yana daukar lokaci,sosai yake bawa jikinsa da fatarsa kulawa da mayuka da turaruka masu shegen tsada,ko nawa yana iya kashewa ya siya turare zuwa mayuka,ko a yanzun kudin wasu turarukan nasa sun isa jari a waien mutane da dama. A gurguje ya feshe gashinsa da turaren ka,hakanan beard dinsa da nasa turaren na musamman tamkar wani mace haka yake a wannan bangaren.


Guri na musamman da yake gabatar da ibadunsa ya shimfida lallausar dadduma,cikin daidaituwa da miga dukka tunanin damuwar duniya izuwa bayanka ya fuskanci alqibla,cikin cikakkiyar tsaiwa da daidaito ya kabbara sallarsa.


Dukka raka'o'in daya saba yi babu wadda ya rage a ciki,ya dade saman abun sallah yana addu'o'in sa,bayan ya kammala yana nade abun sallar akayi masa knocking,sai ya waiwaya yana duban wata maqalalliyar na'ura dake nuna masa fuskar wanda ke knocking din. Jibril ne,matsawa yayi gaban bedside drawer ya ciro wasu files,sannan ya zura wasu lallausasan takalma da aka yi da wani gashi me laushi ya buda gofar da zata sadashi da setting room na gidan.

Cikin girmamawa ya rusuna yana gaidashi


"Sir... bakaci dinner dinka ba,ina fatan lafiya" kai ya girgiza yana miga masa files din


"Am too tired,ina bugatar hutu,gobe inaso mu fita da wuri,zan kwanta yanzun,ko meye please kada wanda ya tasheni,zan nemeka idan ina da buqatar hakan" hannu biyu yasa ya karba cikin girmamawa


"Yes Sir,have a goodnight"


"Allah ya tashemu lafiya" sai ya juya a nutse yana komawa dakin.


Saman lallausan carfet din dakin ya yada pillow,ba kasafai yake iya kwana samam shimfida me laushi ko katifa ba,yayi rigingine idanuwansa na kallon roofing din dakin cikin dim light din daya saki,ya kammala addi' o'insa ya shafe jikinsa,ya koma riginginen ya kwanta yana sauraren zuwan bacci.


A hankali jinsa da ganinsa ya fara nisa da wannan duniyar da muke ciki,ya haurawa zuwa duniyar bacci,irin baccin da kake tsakanin wannan duniyartamu da duniyar baccin,zuciya da ruhinsa suka fara haska masa wani abu da ya faru zahiran dazu dazu cikin rayuwarsa ta ainihi. Tana tsaye ta basu baya kamar yadda ya gani a mafarkinsa, dogon gashinta me tsananin duhu da sheqi daya raba tsakiyar bayanta,hips dinta da mazaunanta da suka fita ainun ta shape din doguwar rigar.

A mugun firgice ya bude

idanunsa,sannan yayi wani irin tsalle ya miqe ya zauna sosai saman carfet din,hannunsa ya sanya ya tallafi goshinsa da ya dan fara hada zufa,a hankali labbansa suka motsa da fadin


"Hasbunallahu la'ilaha illa huwa,alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem" ya maimaita ta kusa sau goma,sannan a hankali zufar ta fara ragywa tana bushewa da kanta,sai ya daga kansa yana bude idanunsa a hankali


"Meye hadin sa da nanny fadeela da har zata biyoshi cikin mafarkinsa?,me yasa duk yadda yakai ga kame kansa da idanunsa daga kan kowacce diya mace,amma hakan bai rabashi da tarin mafarkan kasancewa da wata diya mace dako fuskarta bai taba samun nasarar

gani ba? mafarkinsa na yanxun ya kusa yin

dai dai da yarinyar dake yawan zuwa debe

masa kewa,duk da baisan saurin murya ko ta

fuskarta ba,ya tsani wannan mafarkin da ko

yaushe idan ya yishi take sake haukatashi ya

maidashi mabuqacinsa,lalurar da ya dauka

yayi adabo da ita,ya tasa ta gofar da zai yaqi

hakan,yawan nauye nauyen da yake dorawa

kansa da ayyuka babu ji babu gani,ya dauka

sun isa su cire wannan buqatuwar daga

jikinsa. Yasan yayi nasara da idanunsa da

kuma zuciyarsa,ta yadda duk tarin matan dake

kai kawo a gabansa dama bayan idanunsa,bai

taba daga kai ya kalli wata yaji shaawar

kasantuwa da ita ko kuma ta burgeshi

ba.amma ta bayan fage, wata mace guda daya

tal da baisan wace ba na neman matsanta

masa,cikin watannin da duka duka basu gaza

biyar na.


Siririn tsaki yaja shi daya cikin dakin,ya

miqe cikin matuqar mutuwar jiki ya nufi toilet.

Alwala ya daura,ya dawo ya tsaya gaban

wardrobe ya cire qaramin towel ya goge lemar

jikinsa,ya saki towel din ya koma makwancinsa na dazu. Duk da bayason kwanciyar rub da ciki ko kadan,amma yau din ta zame masa dole haka ya kwanta a rub da cikin yana qangame dukka pillows din dake kewaye dashi.


****Tsam fadeela dake sanye da uniform dinsu,cikin tsafta kulawa da kuma tsaarin sãahar ta rige hannun sãahar din tana langabar da kai


"Ni ba itace zata kaini ba Allah kece zaki kaini" ta gadi a mugun shagwabe tana daf da sakin kuka. Waiwayowa hajiya qarama tay,tadan hade fuska


"Me yasa bakiji uktie,ta yaya nanny zata kaiki school,shin tama iya mota da kike zancan ta kaiki makaranta? idan kuma kinaso ki makara ne shikenan" labiba dake tsaye riqe da key din tata motar da zata miga fadeelan makaranta,saboda driver dinta da hajiya garama ta aika ta jefawa fadeelan harara,sannan tace


"Ta ina zata iya mota? bayan ba itace dasu ba a gida?‚an saba hawa motor din kasuwa?" A nutse säahar ta dag kai,kallo daya tayi mata ta bawa banza ajiyarta,don tun zuwan labiba gidan ta gama karantarta,ta kuma yi aji guda ta sanyata a ciki.


"Allah mommy ta iya,Allan kuwa"


"Ke ko ta iya bazan bayar da motata ba,saidai ku ira a wanke wata cikin motocin gidan nan sannan a kaiki" ta fada cikin fushi ta juva da zummar komawa cikin gidan


"Zo nan labiba" hajiya garaman ta kirayeta,ta dawo a fusace ta tsaya tana huci


"Bata key din ta tuqaku,saiku tafi tare ki dinga monitoring dinta kada ayi miki barna" fuska ta hade cikin fada take magana


"Allah kune kuke sangarta yarinyar nan,sai abinda takeso sannan za'a yi mata?"


"Waishin ba daga jikin kakanta da mahaifinta kudin motar suka samu ba?" Haiiya garama ta jefawa labiba tambayar. Sak labiba tayi tana duban tsakiyar idanun hajiyan,itama kafeta tayi da kallo. Sometimes kamar yarinyar tana manta waye ita,har suso wuce gona da iri a wasu lokuttan,shi yasa takanyi hakan,saboda makaho yasan cewa fa ana ganinsa.


Jiki a sanyaye ba tare kuma data sake cewa komai ba ta migawa saahar key din.

Kamar ba zata karba sannan tasa Hanna ta karba,tana ji a ranta wasu lokutan wasu mutanen suna da bugatar a koya musu hankali,a kuma basu darasin rayuwa.


Jikinta ta kalla babu buqatar sai ta koma ta canza kaya,doguwar riga ce da hijab dinta madaidaici duka golden yellow,sai wani adon wani abu me kama da lace da akayi daga qasan hijab da rigar sai slippers dake qafafunta.


Juya muqullin tayi tana duban

motar,qirar motar ba baquwarta bace duk da tana da tsada,ta saki boyayyen murmushi,tana rige da hannun fadeela daketa tsallen murna sukayi gaba,labiba dake cika tana batsewa ta biyo bayansu.


Kafin labiban ta iso tuni ta bude front seat ta sanya fadeela,ta zagaya sashen driver ta bude ta shige,dole da tazo back seat ta bude ta shigan tana qwafar raina mata wayon da sãahar din tayi


"Ko ba komai yau mun samu new driver" ta fadi don ta baiwa sãahar din haushi


Sarai ta jita,amma saitagi nuna hakan,murmushin da ya subuce mata ma kauda kanta tavi gefe don kada ta gani


"Zakiga new driver gain idonki" ta furta gasan zuciyarta.


Hira sukeyi da fadeela irin wadda suka saba,daga yadda suke hiran kadai zai gaya maka zallar shaquwar dake tsakaninsu da kuma gaunar juna,labiba na zaune a baya kamar zata fashe,ita taso samun wannan damar, amma kuma bata sameta ba koda quater dinta,yanzun ga wata banzan nanny daga sama tazo ta mamaye rayuwar yarinyar.


Sai data tabbatar fadeela ta shiga class,ta kuma sanya hannu akan kawota sannan ta fito. Zata tada motar mrs sadeega ta sanvo kan tata,dole ta tsaya suka gaisa "Kina aiki me kyau miss säahar, kowa ya kalli fadeela yasan tana samun canji garara,hatta da performance dinta a class ya qaru,tiny baby ta fara komawa chubby ma sha Allah"


"Alhamdulillah" sãahar ta fada,ita kanta tana jin dadi ko yaushe yadda yarinyar ke wayar gari da goshin lafiyarta da kuxarinta suna garuwa,basu jima ba sukayi sallama,mrs sadeega ta wuce su kuma suka fice.


Ta cikin mirror ta dubi labiba dake zaune a bayan ta toshe kunnuwanta da earpiece tana bin waqoqin turawa tana gyada kai,murmushin mugunta ta saki, saita take motar ta qara mata gudu. Da sauri labiban ta daga kai,ta zare earpiece din daga kunnenta


"Ke meye haka? ki rage gudu da Allah" tana kaiwa nan ta maida earpiece din. Da kadan kadan ta sake garawa motar gudu fiye da dazun,tuni labiba ta cire earpiece din harma da wayar duka ta ajjiye,cikin fada da tashin hankali take magana


"'Wai bakya gani ne,wanne irin gudu ne

wannan?,kashemu zakiyi ne,dake fa nake

magana!" Kunnen uwar shegu tayi da ita,salma

sake qara gudun da tayi,ta shiga kurdawa

tsakanin motoci tana overtaking,ta tuna

da tsohuwar dabi'arta na mugun gudu a

hanya,don a baya saida yaa Saifullahi yasa aka hanata mota na wasu watanni sannan ta bari.

Tun labiba na hayaniya har ta fuskanci

hayaniyar ba zata kaita ba,ta koma lallashi

da kwantar da murya,amma sãahar kam ko

a jikinta,ta dinga shimfida gudu da ita,sai ga

labiban tana sakin hawaye,kowanne sashe a

jikinta rawa yakeyi,don babu abinda ta tsana a

mota irin gudu.


Daga bakin gate din gidan ta tsaida motarta bude ta fice abinta tare da bar mata

key din a jikin motar,tayi knocking gofar gate

din,daya daga cikin security din ya taso ya duba wacece sannan ya bude mata. Baya yaja cikin rusunawa,saboda sosai Allah ya sanya ma ma'aikatan gidan gaba daya gain wani irin girmanta. Yadda suke mu'alama da masu aikin gidansu haka ta dauki kowa cikin gidan,tana girmamasu qwarai, irin girman da duka cikin gidan ba wanda ke basu irinsa,bugu da qari me hannun kyauta ce ita,a hakanma afifa tace mata saita rage,don kada su lura da ita din wace,su sanya ayar tambaya a kanta.


"Madam ya na ganki a qasa?" Ya fada da 'yaf gaurayayyiyar hausarsa da bata fita tarr

"Daga waje na sauka"


"Welcome" ya sake fadi yana dage gate din don yasan yana jinkirin budewa labiban yau shine mutum na farko da zata fara saukewa kwandon rashin mutuncinta na safe.

[06/09, 7:21 pm] Mimah Yusuf:

No comments