Breaking News

Tabarmar Kashi Book 1 Page 57-58

 



Page 57


      Kamar yadda tayi tsammani mahmud ne,ajiyar zuciya mai nauyi ya fara saukewa


"Kiyi haquri,duk yadda naso nayi miki yadda kikaso,zuciyata ta gaza bani hadin kai,na mugun jarrabtata da sonki har bansan iyaka ba" bakinta ta tabe,tana jin kamar ta saki wayar ta tarwatse,da wadan nan kalaman nasa gwara ya sakar mata ihu a kunnenta yafi mata sauqi,amma hakanan ta daure ta amsa a taqaice


"Is okay,bana dan jin dadi ne,that's why na kashe wayar"


"Ya salam" ya fada cikin nuna kulawa


"Me ya sameki?"


"Noo,lite headache ne,amma i feel better"


"To alhamdulillah,kibar wayar a kashe ki samu ki huta sosai,idan inason jinki zan kira ta line din afifa,bata wayar zamuyi magana" batace komai ba ta zare wayar ta miqa mata tana harararta,tana danne dariya ta karba,batasan me ya gaya mata ba,taga ta miqe ta fita,ta bita da kallo tana tabe baki taci gaba da shiryawa.


      Tana cikin saka kaya afifan ta dawo,ta koma ta zauna tana ci gaba da cin abincinta,saita fasa daurin dankwalin da tayi niyya,dama can dankwali asara ne cikin dinkunanta,ta qaraso gaban afifan bayan ta jawo stool ta zauna ta sanya hannu suka fara ci tare. Har suka danyi nisa babu me cewa da dan uwansa wani abu,afifa ta karanci yau mutanen ne a kusa,ita kuma bakinta magana ce fal,don haka ta koma ta zauna sosai tana kallon sãahar


"Na baki shawara?" Dubanta sau daya tayi sannan tace


"Bani mana,is ether na dauka ko na bar miki kayarki"


"Alright,ammm......magana ta gaskiya na jima banga soyayya me zafi irin wadda mahmud yakeyi miki ba....."


"Tam, contract din kuma da kika karba kenan da safen nan,ko azahar batayi ba?" Dole ba tare data shirya ba dariya ta qwace mata sosai


"Allah ya isa bestie,wait......wai me kika mayar dani?"


"Me dalili,naga alama sana'ar da kikeso ki koma kenan" wannan karon ma saida wata dariyar mai sauti ta kufce mata har tana shirin qwarewa,a nutse sãahar din ta tsiyaya ruwa ta miqa mata


"Maza karba kisha kada ki wuce gana ya rasa campaign officer dinsa" tana dariyar tana sha,har taji dai dai ta ajjiye,tayi gyaran murya kadan tana dubanta da idanunta da suka tara hawaye


"Seriously nake miki magana,amma naga kinason ki maida abun wani joke,don Allah bestie ki manta da komai,ya kamata kiyi moving forward mana,kina tunanin zamanki a haka adam bazaiyi tunanin shi kike jira ba?,har yanzu soyayyarsa ta hanaki kallon kowa bare ki aureshi?"


"Soyayya?" Ta furta kalmar kamar ranar ta fara jinta,kai afifa ta jinjina


"Yes" wani qaramin murmushi me ciwo sãahar din ta saki,sai kawai ta miqe


"Banda bayan soyayya dake tsakanin namiji da mace,kawai nau'ikan soyayya kala kala, kamar wadda ke tsakanin 'yan uwa da iyaye,da nace Allah ya tsinewa soyayya albarka" ido afifa ta zaro,ta kuma hangame baki yana kallon sãahar,wadda tayi furucinta hankalinta kwance,saima ta gyada kai ta juya tana nufar qofa


"Naga alama tunda kika samu annual leave din nan rashin aikin yi ya sameki,shi yasa kika amsa contract daga wajen gana,to wallahi ke dashi ba wanda zaya matsamin" tana kaiwa qarshe ne dai dai sanda take fita a dakin gaba daya.


     Gurin ummee tayi tafiyarta,wunin ranar gaba daya taqi tsaiwa sauraron bayanan mahmud. Saidai wani abun mamaki,duk bayan wasu mintuna sai yarinyar da ko sunanta bata sani ba ta fado a ranta,hakanan maganar da sukayi da mrs sadeeqa,wunin ranar har yamma,batayin minti arba'in cikakke bata fado mata a rai ba.


      Ta idar da sallar la'asar tana yiwa ummee din gyaran wardrobe dinta kiran yaa Saifullahi ya shigo wayarta,cikin girmamawa ta daga kiran ta kara a kunnenta,ta gaidashi a aladabce,saboda shine babba duka gidan,kuma hatta da yaa muhyi yana bashi girma,duk da cewa shike binsa,akwai girmama na gaba sosai a tsakaninsu


"Kina gidan inna ummee dinne?,akwai baqo da zayazo ya sameki,abba yace a shaida miki" gabanta ne ya fadi,rudewa kuma ta sameta lokaci guda,har ta kama sunansa ba tare data shirya ba


"Mahmud?"


"Eh fa,da wani abu?" Ya tambaya kai tsaye da seniority din nan nasa


"A'ah,daman.....dama munje therapy saloon ne" 


"Alright,zai kiraki yanzun saiki gaya masa" daga haka ya yanke wayarsa abinsa.


     Wayar ta jefar gefe kamar zata saki kuka,da qyar ta tsara qaryar gashi kuma da alama haqanta bai cimma ruwa ba. Bata gama wannan tunanin ba kiran mahmud din ya shigo,kamar ta dora hannu aka tayi kuka haka ta daga kiran.


      Akwai wani irin farinciki sosai cikin muryarsa


"Can I get the address?,saina sameku a can?"


"no,mu hadu a gida kawai after one hour" kamar zai zuba ruwa a qasa yasha haka yaji,cikin madaukakin farinciki yace


"Thank you,thank you so much" bata tsaya jin qarashen godiyar tasa ba ta yanke kiran tana gunaguni,ta ajjiye wayar gefe tana dafe kanta.


      Ko kwalli bata sanyawa idanunta ba haka ta fito,afifa tayi tayi amma tayi biris da ita,daga baya ma cewa tayi


"Idan kika matsamin Allah sai na fasa fita"


"Allah ya baki haquri masifaffiya" sai taja bakinta tayi shuru,tasan kadan daga aikinta.


     Tun kafin ta isa afifa tasa an cika shi da kayan motsa baki kala kala,tahowarta ya sanyashi miqewa,bai zauna ba har sai data zauna sannan ya zauna yana mata barka da fitowa,ta danne zuciyarta ta gaidashi,abinda ya masa dadi sosai. Duk yadda yasan zai sha kanta sai da yayi,tana zaune tana saurarensa har ya gama,sannan ta motsa labbanta


"Inda zakayi haquri da hakan yafi,saboda tuni na rufe babin soyayya daga rayuwata" kai ya girgiza


"Banajin zan iya,banajin zan iya daina sonki,kiyimin alfarma ki amincemin ki aureni,zan iya zama dake a hakan koda ke baki sona" tsam ta miqe,saboda ta fuskanci mahmud din yayi nisa,kuma bayajin kira sam. Ta bude bakinta da niyyar magana ya zaid ya iso wajen.


      Yanayin yadda taga suna gaisawa da shi cike da sanayya mutunci da girmama juna ya daga hankalinta,sanda suka gama gaisawan da tambaye tambayen juna sai zaid din ya kalleta


"Ki riqeshi da kyau,mutumin kirki ne sosai" maganar tayi mugun tabata,har kuma mahmud yayi mata sallama ya wuce bata sake fahimtar abinda yake fada ba. Haka taci gaba da kasancewa har zuwa dare,tabbas!,ba shakka komai zai iya faruwa,muddin mahmud yaci gaba da samun irin wannan soyayyar daga wajen 'yan gidansu,idan tace komai,tana nufin komai din,ciki harda tausata ta karba aurensa ba tare data shirya ba!.  


     Wannan sautin da ya tsarga daga cikin kwanyarta shi ya sakata miqewa zumbur ta zauna saman gadonsu,afifa dake gaban system tana wani aiki ta waiwayo tana dubanta,saita maida kai tana ci gaba da aikinta ganin ta dauko wayarta itama ta bude. Tun bayan tafiyar mahmud ta fahimci tana cikin damuwa,ta riga da tasan damuwarta na meye,so shi yasa ma bata tambayeta akan komai ba.


     Kai tsaye ta kirayi layin mrs sadeeqa,bugu daya tal ta daga,da alama tana kusa da wayar,cikin mamakin ganin kiranta da kuma zumudi hadi da girmama suka fara gaisawa,tana tambayarta tsaffin dalibanta su fadeel


"Basu dawo qasar ba har yanzu....." Ta furta cikin son yankewar tambayoyin ta kuma isar da nata saqon


"Ma sha Allah" mrs sadeeqa ta fada


"Inason tambaya ne naji,your student,ta samu nanny din nan kuwa?" Kai ta girgiza


"Kai,gaskiya i don't think so"


"So if you don't mind nace akwai me buqatar aikin" murmushi ta saki


"Ma sha Allah,so far dai banajin akwai wadda tayi musu,duk da hajiyan tata tace akwai wadanda aka yiwa screening,amma basu cancanta ba" duk da batun screening wa nanny's din ya bawa sãahar mamaki,amma ba wannan bane yanzun a gabanta


"Alright,hakan yayi"


"Naji dadi,nasan ko wace za'a samu daha bangarenki she wil be the best among others in sha Allah,wace a ina take?,sai na yiwa hajjajun magana"


"Nice" ta fada da qwarin gwiwa. Ba mrs sadeeqa ba,hatta afifa dake aiki batasan sanda ta tashi ta zauna sosai tana duban sãahar da wani irin madaukakin mamaki ba,tare da tantamar abinda kunnuwanta suke son jiye mata


"Na'am madam,me kika ce?" Mrs sadeeqa ta tambayeta cike da kokwanton abinda taji daga bakinta


"Yes,nice,ni zanyi aikin" dan murmushi mrs sadeeqa ta saki


"Madam,ko baki kula sosai da wanne irin aiki bane ake magana,ba aikin company ko na banki ko lecturing bane......raino ne,na yarinya me lalura,duk da ba qarama bace sosai,amma dai raino ne" ido sãahar ta lumshe sannan ta budesu lokaci guda


"Ya salam ya Allah" ta furta a qasan zuciyarta,batason ta fara da samun matsala tun yanzu,saboda ba zata iya jurewa ba,zuciyarta ta karkata matuqa,ta kuma kwadaitu da buqatar aikin


"I Know,na fahimta,just......ina sha'awar yin aikin ne" shuru mrs sadeeqa tayi cikin kokwanto matuqa, kafin daga baya tace


"Zaki iya kuwa madam,wouldn't it be a disgrace?"


"Surely mrs sadeeqa,ko ba komai aikin lada ne" ta fadi hakan har zuciyarta


"Gaskiya ne,i will talk to hajiyan,zan miki magana,kin gama samu ma in sha Allah,you are not the kind of people to be ignored"


"Thank you ma'am" sãahar ta fada tana gintse kiran


"Thanks for what sãahar?,wanne mummunan tsari ne wannan?,a nanny?" Afifa ta furta kamar zatayi kuka,kalmar na sukar ranta.


     A nutse abinta hankali kwance take kallon afifa din harta gama,saita sauka daga inda take zaune,ta dawo kusa da afifan ta zauna sosai tana fuskantar ta


"Wannan shine burina a yanzu, abinda kuma nakeso,bazan iya boye miki komai ba bestie,shi yasa nayi wayar ma a gabanki,jikina yana bani mahmud nason yin galaba akan su abba dasu ya Saifullahi,idan banyi wasa ba kuma komai yana iya faruwa,so I want to be far away from him for a while that's why na nemi wannan aikin,banason mahmud afifa,bazan iya aurenshi ba,zanyi nesa dashi,duk sanda na samu tabbaci da yaqinin iya zama da wani namijin.....koda shi mahmud dinne zan dawo a kurkusa,i won't be longer,support me please bestie"


"What a bad idea sãahar?,you mean....zaki koma 'yar aiki fa kenan?,wait.... idan na yarda ma su abba kina tunanin zasu yarda da ke?" Murmushi ta saki kadan


"A yanzun nafi sha'awar zama 'yar aikin bestie,ko banza babu ruwana da kowa da matsalarsa,zan zauna guri daya nayi rayuwata da yarinya qarama,zan cika burina na raino wanda adam ya dakushe min.......zan samu ladan yarinyar dake dauke da cutar epilepsy,ban sani ba,kota silar jinyar Allah ya yayemin tawa damuwar bestie,don Allah ki maaramin baya,kada ki watsamin qasa a ido" shuru afifa tayi tana jin yadda sãahar ta riqe hannunta da kyau,da alama tana buqatar yin hakan,kanta ya kulle sosai,ta yaya zata mara mata baya ta mayar da kanta nanny?,bayan da gantanta?,duk randa maganar ta bayyana me zatace da su abba da maama?. Sosai sãahar din ya tsareta da ido cikin laushi da salon rarrashi,sai ta rasa amsar da zata bata,daga bisani Allah ya kimsa mata,ta waiwayo ya dubeta tana sauke ajiyar zuciya


"Ni dake duka muje muyi istikhara,idan mun samu nutsuwa akan abun,zan maara miki baya"


"Kin tabbata da gaske kike?" Murmushi ta saki


"Da gaske nake,amma ki tanadi abinda zaki gayawa su abba,don ni bazan iya musu qarya ba" miqewa tayi daga tsugunon da tayi ta zauna sosai


"Kinfi kowa sanin ba dabi'ata bace,so nima ba qaryar zanyi masa ba". 


      Akan haka suka samu matsaya ita da afifa din,sannan kuma dukansu suka shiga istikhara din kamar yadda afifa ta shawarcesu. Cikin kwana ukun kuma baki dayansu ita da afifan,kowanne ya samu nutsuwa cikin ransa,rudanin dake ran afifa ya kau,haka dan kokwanton da ita sãahar din kanta takeyi game da aikin sai taji babu shi,taji har cikin ranta zata iya,fatanta daya kada abba yace ba zatayi ba.


*_TOFA??,me yake shirin faruwa kuma?,GUDUN K'ADDARA sãahar ke shirin yi ko kuwa?,ku biyoni dai muje zuwa_*

[02/09, 3:47 pm] +234 810 324 4136: Page 56


*H U G U M A*


*_TABARMAR ?ASHI_*??

Page 58


     Kwana biyu kacal Mrs sadeeqa tayi kiranta,ta gaya mata cewa hajiyan tayi accepting nata,saboda haka ta shirya kwana uku masu zuwa zasu zo da mota a dauketa ta kama aikinta.


     Taji dadin hakan,amma kuma fargaba ta lullubeta na yadda zata tunkari abban,wuni tayi cikin rashin sukunin,afifa na kallonta taqi bata shawarar komai


"Na gama aikina ai,tunda har nace bazan gayawa abba manufar komai aka aikinki ba"


"Haba bestie"


"Da gaske nake" ta sake jaddada mata,sai daga bisani ta samu qwarin gwiwa,bayan wata idea ta fado mata,ta dauki wayarta da sauri ta fara kiran anty farheen.


"anty,zan sameki yau a gida?"


"Eh ba inda zani yau,akwai wani abu ne?"


"Saina iso kawai" tace da ita,saita ajjiye wayar ta fada toilet kawai ta fara wanka,so take ta gama da kowacce matsala a yau,tayi shirin tafiyarta hankali kwance.


     Cikin lokaci qalilan ta shirya cikin wata doguwar rigar abaya qirar qasan oman mai sulbi da kuma tsarin zubin duwatsu masu daukan hankali,fuskarta ta sake wani fresh da wani irin haske me kyau,kalar abayan na charcoal color ya karbi farar fatarta sosai,sassanyan qamshinta na bin kowanne sashe na dakin har zuwa falon da batakai ga fitowa ba.


       'Dan abinda take da buqata ta dauka a wata qawatacciyar qaramar jaka me jikin mage,dai dai lokacin da afifa ke kitchen tana duba girkin abbansu da basu aikin gidan suka dora ta dawo dakin,ta murza qofar ta shigo,idanunta akan sãahar


"Madam nanny" ta fada tana murmushi hadi da tabe baki, zagayyun fararen idanunta ta juya tana goya jakar a bayanta


"Yes,daga yau sunana kenan" qaramar dariya afifa tayi tana zama saman stool


"Kinsan Allah zaiyi wuya ma su karbeki as nanny,shin wai ke baki kallon kanki ne?,wace zata daukeki 'yar aiki muddin tana da aure?,wace wawiyar ce?....."


"Don Allah afifa tsaya,kiyimin fatan alkhairi mana,wannan duka fatan tsiyan na meye ne ha'an"


"Baqinciki nakeyi, bestie na zata zama 'yar aiki"


"Okay,that's fine,kici gaba da fada" saita fara zura dogayen qafafunta cikin wani lallausan plate din takalmi


"Ina zakine ma babu ko gayyata?" Ta jefeta da tambayar bayan ta dakata daga danna wayarta


"Gidan yaa muhyi"


"Jirani don Allah na shirya" ta fada tana miqewa da gudu bayan ta cillar da wayar tata ta shige toilet ba tare data tsaya jiran jin abinda sãahar din zata ce ba. Iska me zafi ta fitar,afifa dole saita bata mata lokaci,tanason ta gama komai da wuri ta iske abbanta a gida,ta kalli agogon dake daure a hannunta dan india dan kamfanin Daniel Wellington,saita maida dubanta ga qofar bandakin


"Ki sameni a wajen ummee,don't stay longer please" saita tsugunna ta dauki laptop dinta me tambarin apple ta fice daga dakin.


•••••••••"daga ina kuke halan da yamman nan?" Farheen ta fadi tana zama saman kujera,bayan ta fito musu da plate din snacks,me aikinta dauke da daya try din data shirya musu smoothie,don ita din gwanar girki ce kala kala,fridge dinta kawai idan ka bude zaka samu fresh snacks sosai,a nan din sãahar ta koyi girki masu yawan gaske


"Nanny sãahar ce ta tasomu,ni fa amma gayyar sodi nazo,don bata gayyaceni ba nace ta tsayani mu taho tare" afifa tayi maganar tana duban sãahar daketa ji da rigimar khalipha shi da aleena data qara wayo sosai


"Nanny kuma?" Farheen ta fada tana dan dariya,a zatonta fadan da suka dan saba tabawa ne da shaqiyanci ma juna ya motsa tsakaninta da sãahar din


"Eh mana anty,koda yake dai ance waqa a bakin me ita yafi dadi" ta qarshe zancan tana jawo cup din da smoothie din yake,ta gyaran zaman straw din jiki ta fara zuqa a hankali tana lumshe ido,zaqi da dadinsa yana ratsata


"Uhmmmm,ta yaya don Allah ya muhyi zai iya qara aure ana masa wannan delicious din" qaramar dariya farheen tayi,tasan afifa qwarai badai iya tsokana ba,amma hakan na mata dadi,don babu komai tsakaninta da dangin mijinta face tsantsar girmama juna da zaman lafiya hadi da qaunar juna


"Basu da tabbas fa,iya girki ko qwarewa a wani abun baya hanasu qara aure idan sunso,koda kuwa ke din hurul'eeni ce,saidai kawai dai ki iya din don ki amsa sunanki na mace,sannan saboda lafiyarki yaranki dashi kansa me gidan,yaranki mata kuma ki zame musu makaranta,sannan koda wata zatazo din ya zamana ba'a fiki da komai ba,kin wuce kiyi kwaikwayo saidai keda ita ku goga,kowa ya baje hajarsa" kai sosai afifa take gyadawa cikin gamsuwa,zaiyi wahala ka zauna da farheen baka qaru da ita ba ta kowanne fanni na rayuwa.


"Ke kuma yaushe kika zama nanny?" Ta maida tambayarta ga sãahar,daga kanta tayi,sai kuma ta zaunar da aleena sosai tsakanin qafafunta


"Shi mutum idan gulma tayi masa yawa sai addu'a,da kin barta ta qarshe miki labarin..... bestie naga alama bazaki rufan asiri ba" dariya sosai afifa keyi harda kwanciya cikin kujera,abun yana bata mamaki yadda sãahar lokaci daya ta daukaki batun aikin da zahiri tafi qarfinsa,ita kanta a gidansu 'yan aiki nawa ne?,so amma a yanzun ita bata jin komai akan aikin,tunda suka tsaya sukayi addu'a a tare.


"To nayi miki qarya ne,ba nanny din bace?"


"Ban sani ba.....am anty don Allah alfarma nazo nema" ta qarashe maganar tana maida hankalinta ga farheen


"Ina jinki,Allah yasa bata fi qarfina ba". Komai ta zayyanewa farheen shi,saboda babu 'yar boye boye a tsakaninsu,sannan ta qarashe da cewa


"Matsalata daya abba zaice zaiyi bincike akan inda zani aikin,abu daya nakeson kiyimin,zance masa kin sansu,sannan wata uku kacal zanyi na dawo" shuru farheen tayi tana jinjina kai,tana qaunar sãahar har cikin ranta tamkar qanwarta uwa daya uba daya,zata iyayi mata kowacce alfarma,to amma kuma akwai matuqar girmamawa da ganin mutuncin juna tsakaninta da surukanta,batason tayi musu qarya


"Zan iyayi miki kowacce alfarma,amma bazan iya shaidar abinda bani da tabbaci ba,inason ki bani address dinsu na gani,zan aika ayimin binciken ingancin halayyar mutanen gidan"


"Alright" ba wani jinkiri ta kira Mrs sadeeqa kai tsaye,ta kuma tura mata komai da komai.


     Address din ta tura mata,ita kuma ta miqawa farheen wayar. A fili ta karanta address din


"Wannan layin ai kamar layin gidan qawata sauma,bari nayi confirming" khalifa ta tura ya dauko mata wayarta,saita tashi tabar gurin. Duk da hankalin sãahar nakan yaran,amma kuma fiye da rabin tunaninta yana kan farheen data fita a falon.


     Ta kusa mintuna ashirin sannan ta fito,ta koma ta zauna a inda ta tashi


"Yanzu kuma ina da qwarin gwiwar bada shaida,layin gidan qawata ne,tasan gidan,sanann me gidan ma tacemin sananne ne sosai,mutumin kirki ne qwarai da ya samu yabo da shaidar al'umma,ko jiya shine wanda ya qaddamar da committee na tsaro na unguwar,kusan ko yaushe suna tare da me gidanta tsakanin sallar magrib da isha'i,duk da ba mazauni bane,yakanyi watanni ma baya gari,yarinyar ce tace bata santa sosai ba,tunda ba inda take fita,amma tace eh tabbas yana da diya guda daya. Ajiyar zuciya sãahar ta sake,sai ta sake jin nutsuwa tana ratsata,yanzun kam ta samu qwarin gwiwar tunkarar abba,muddin farheen tace ta san gidan,tana da yaqinin babu lallai abba ya zurafafa ko yace zai hanata,yana ganin kimarta sosai cikin surukansa.


       Ana idar da magriba sãahar din ta miqe


"Zan wuce gida bestie ya za'a yi?"


"Kije kawai,drivern anty farheen sai ya saukeni"


"Ba wata damuwa?"


"Babu miss nanny" harara ta watsa mata,ta dauki qaramar hand bag dinta ta tsugunna tayi kissing aleena a cheeks dinta.


      A kan hanya ita kadai tana driving tana tsara zantukan da zata tunkari abba dasu,wani lokacin takanji abban me sauqi ne akan maama,amma tasan muddin abban ya amince,maama din ma komai zaya zo da sauqin in sha Allah.


    Mintuna talatin kacal suka kaita gida,saboda tana tuqin tana duba lokaci,tanason ta saita lokacinta dai dai da sanda zata riski abban yana hutawa.


     Baaba habu ne mutum na farko daya fara yi mata barka da zuwa bayan ya dage mata gate din gidan ta wuce zuwa ciki,ya iso gaban motar sanda take fitowa


"Barka da zuwa farar d'iya" qaramin murmushi dake qawata fuskarta qwarai ta saki tana fitowa a motar


"Baba habu,baaba rabi ta koya maka ko?" Murmushin dake dauke da dattijanka yayi


"Sunan ya dace da me shine ai,kedai Allah yayi miki albarka keda sauran 'yan uwanki"


"Ameen ya Allah baba habu,Allah ya qara girma" kamar sauran lokuta,bata fiya wucewa ba tare data yi masa alkhairi ba,tun tasowarta yake cikin gidansu yake kuma musu aiki bisa gaskiya da amana,ko sau daya bata taba jin wani yayi kuka a kansa ba,hakanan baaba rabi,ba kasafai gidansu suke sauya me aiki ba,saboda suma masu aikin idan suka fara,basa barin gidan haka siddan saidai mutuwa ko kuma aure.


     Hannu biyu yasa ya karba yana godiya,ba kasafai ta fiyason yawan godiyarsa ba,ko ya dinga sanya hannu bibbiyu idan zai karba abu daga wajenta ba,to amma koda zatayi maganar ma bazai canza ba,ya riga ya saba


"Ameen ameen,baba habu ayi min addu'a" ta fadi tana rufe jakarta


"Kullum cikin yi muku nake,amma a yanzun ma bazan fasa ba,Allah ya tabbatar miki da dukkan alkhairi a rayuwarki"


"Ameen ya hayyu ya qayyumu,na gode sosai" cikin wannan girmamawar da mutuntawar ta nufi entrance na gidan,bakinta dauke da


"La haula wala quwwata illa billahil aliyyul azeem" don taga motar abban nata,hakan kuma ya tabbatar mata yana gidan,koda ya fita to masallaci ne kawai.


      Falon nasu ba kowa,ta danja qaramin tsaki,ta tsani wannan loneliness din na gidan sam,shi yasa bata cike sati guda a gidan,kwanaki taji maama tana batun zuwa nijer cikin 'yan uwa ta dauko yara biyu mata,batasan inda zancan ya kwana ba har yanzu.


     Dakinta ta duba don sanar mata da isowarta amma bata risketa a can ba,saita zarce kitchen tana tafe tana yaba tsafta da kulawar da gidan nasu yake samu,wannan ya sanya ta taso da dabi'a ta masifar tsafta qwarai.


      Sallamarta ya sanyata waiwayowa sanda take juye tea a flask


"Daga ina da daren nan?"


"Gidan ya muhyi" ta fadi tana zagayowa ta rungumeta ta baya


"Yau kuma?,sakeni to kada na qone"


"Da kin barta ai hajiya,auta ce fa" cewar lariya me aikinsu


"Wannan gansamar?" Ta fadi dai dai sanda sãahar din ta zagayo ta karbe qaramar rariya da cup din da take tace shayin taci gaba da aikin


"Amma na hanaki tafiyar dare irin haka ko?,abbanku ma kuma bayaso"


"Za'a kiyaye in sha Allah maama"


"To Allah yayi albarka"


"Ameen maama na". Tsaf ta gama hada mata komai sannan suka fito tare bayan taji abban yana masallaci,ita tayi dakinta ita kuma ta wuce sassan abban.


     Kayan jikinta ta fidda,ta shiga wanka,ta wanke jikinta da kyau da ruwa me dumi sosai,sai data fara yin sallar isha'i sannan ta shirya cikin riga d wando masu laushi,rigar ta kawo mata har cinya me gajeran hannu,sai wandon shima daya saukar mata har qasa,ta kama gashinta ta hade da pink ribbom sannan ta shafe jikinta da lallausan turarenta. Wani kyau tayi sosai,kayan sun karbeta kamar bana barci ba,idan ka ganta a lokacin zata dauka duka duka shekarunta sha takwas ne zuwa sha tara. Remote din ac ta dauka ta rage qarfinta,ta ajjiye saman bedside table sannan ta dauki hijab dinta me hannu ta saka,ta zira slippers dinta ta fito daga dakin.


      Tana takawa qirjinta yana dukan uku uku,addu'o'i fal bakinta,daga jiya zuwa yau ta wani mugun damuwa da aikin,damuwar da ita kanta takanji mamaki,batasan dalili ba,tafi danganta hakan da abubuwa biyu,neman mafaka da kuma tausayin yarinyar da ya sauka tun daga saman zuciyarta har ciki tun jiya.


      Da sallama ta shiga parlor din abba,ya amsa mata yana dauke dubansa daga kan zain dake zaune a gabansa ya mayar kanta,ta qaraso cikin nutsuwa tana zama a gefansu. Abban ta fara gaidawa sannan ya zain,sai ta karbi maama dake qoqarin serving nasu abinci ta fara zuba musu,data kammala sai ta koma gefe ta lafe kawai,hankalinta yana rabuwa gida biyu, rabi a hirarsu,rabi kuma tana tauna yadda maganar zata fita a bakinta 


"Yadai ummin abba?,akwai labari?" Dr mamman ya fada sanda ya gama tauna lomar abincin dake bakinsa,murmushi ta saki,tayi qas da kanta tana murza yatsunta


"Babu abba"


"Ban yarda ba,bari mu gama cin abincin tukunna" ba abun mamaki bane sam don ya fahimci damuwarta lokaci daya,shi din wani irin mutum ne daya samar da shaquwa da sabo sosai tsakaninsa da iyalinsa,akwai fahimtar juna da kuma sakin fuskar da bai haifar da raini ko rashin girmamawa ba a tsakaninsu ba.


      Ba jimawa zain yayi musu sallama ya wuce,falon ya zama daga ita sai abban,don maama ma ta wuce bedroom dinsa tana sanya turaren wuta,wanda hakan din dabi'arta ce,duk da ko yaushe gidan ma gaba daya cikin turare yake,amma muddin abban yana gab da kwanciya sai ta kunna burner ta saka wani turaren,wanda yawanci yana riqe dakin har zuwa safiya,a gurinta sãahar ta koyi wannan,yana qarawa bacci dadi da armashi sosai.


"Ummi na,ma yake faruwa?,kada kiji nauyina,ki gayamin" sake takurewa tayi kadan tana jin fargaba,ta saci kallon abban,abinda ya alamta masa da gaske akwai magana me muhimmanci da takeson gaya masa


"Ehmmm,ina jinki ummi na"


"Abba....." Sai ta kasa ci gaba


"Ina jinki,fell free mana ummi"


"Abba don Allah wata alfarma nazo nema,wadda nake da tabbacin indai ka amince tafi dukkan wani aiki da zanyi kyau da samun lada me tarin yawa,abba.....inason ka saurareni,sannan kayimin alfarma"


"Ina jinki" ya fada yana tattara hankalinsa a kanta.

[02/09, 3:47 pm] +234 810 324 4136: Page 57


*H U G U M A*


*_TABARMAR ?ASHI_*??

No comments