Breaking News

Tabarmar Kashi Book 1 Page 55-56

 


Page 55



A nutse ya zauna a falon gidan yana duba report din qarya da Dr din bogin da adam yayi hiring ya hada,ga duk qwararren likita yana kallon abun zai fahimci an tsarashi ne kawai,saboda babu gaba babu baya,bayanan babu wani cikakken abun kamawa.


Nannauyar ajiyar zuiciya ya sauke,wannan mutumin bayan qwarewa da yayi wajen hada plan,harda sa'a ma daya taka cikin al'amarinsa,ko kuma qaddarar da bahaushe yakewa take da bata wuce rana da lokacinta,saboda ya duba ya dubo,family irin na dr mamman girema,ba abu bane me sauqi kayi musu irin wannan abu lokaci guda hankalinsu bai kai kai ba,duk da akwai tasirin boko sosai a tattare dasu,amma suna da ilimin addini a tattare dasu. Daga qarshe ya rufe file din yana sauke ajiyar zuciya,lallai banda ma wannan......sun bashi amana qwarai,ta yadda tunaninsu bai taba kawo musu wai adam din zai aikata wani abu makamancin wannan ba.


A nutse likitan ya maida dubansa ga momee dinsa data iso tanata kumfar baki akan case din filayen,tana ta fada akan duk wanda ya murqushe dukiyar,ya kuma bi d'anta da sharri bazasu qyale ba. Duba daya yayi mata ya karanci 'yar bariki ce tsantsa,amma dattako da karamci irin na iyalan dr mamman girema yasa basu taba nuna mata komai ba face zallar karamci da mutuntawa.


Afifa dake dakin sãahar tana tattaro dukka kwalaben alluran da aka dinga juyewa gangar jikin 'yar uwartata,tana jiyo dukka kumfar bakin momee,tun ranar tasan cewa komai da hadin bakinta ake aikatashi,tsanar da take wa matar ta sake ninkuwa cikin ranta. Qoqarin dauke hankalinta tayi akan maganganun amma kuma ta kasa,bala'i biyu ne ya hade mata,na farko qarfin alluran da aka dinga dibgawa sãahar din,wanda tasan banda ikon Allah,babu abinda zai hana kwanyarta juyewa,na biyu kuma yadda momee din ke magana kamar mutuniyar arziqi,wannan yasa ta miqe a fusace,ta daga inda ta yiwa jakar ajiya ta musamman ta cirota ta kuma fito daga dakin da wani irin hanzari,tana huci kamar ta hadiyi kunama.


Yadda ta buda qofar da qarfi har tana dukan bango ya dawo da hankalin dukka mutumin dake falon kanta,yaa zaid yana shirin tambayarta lafiya?,saita miqa kwalaben ga likitan


"Dr,dubamin wadan nan kwalaben,allurar meye?" Hannu biyu yasa ya karba ya fara dubasu daya bayan daya. Wani gumi ne ya yanko masa shima,ya daga kansa ya zubawa adam idanu.


Tun baice komai ba ilahirin jikin adam din ya dauki rawa,ko kadan baisan da zaman kwalaben ba a dakin,yasan duk sanda akayi allurar indai ya tuna zai kwashesu ya fita dasu,to waye ya tarasu?,ba shakka sãahar dince,hakan yana nufin duk lokacin da akayi mata allura tana fakar idonsa ta dauki kwalbar kenan ta adana?,lallai ta shiryama zuwan wannan ranar


"Wanne dan wutar ne cikin likitoci yake iya zuqar wannan ruwan allurar ya zubesu ga jikin dan adam?" Abinda likitan ya fara tambayarsa kenan cikin matsanancin bacin rai.


Duk yadda yaso ya shirya qaryar da zata sanyashi ya bulle amma bakinsa yaqi bashi hadin kai,saboda rawa kawai labbansa sukeyi,da qyar ya fusgo kalmar


"Bansan a inda aka samosu ba,don wannan kwalaben ni ban taba ganinsu bama"ya tabbatar qarya yake,tunda ya riga yasan da komai,sai kawai ya maida dubansa ga ya zaid ya fara karanto masa aikin da allurar takeyi a jikin dan adam,da kuma girman illarta.


Kuka kawai maama ta fashe dashi tana kiran sunan Allah,yayin da adam ya jiqe jagab kamar an masa wanka da ruwa,jikinsa yana bashi yau ba ranar sa'ar sa bace,yau ranar tonin sililinsa ce,momee ce mai qarfin halin miqewa,cikin borin kunya ta fara maganganu


"Dama dai kawai kun shirya ci mana mutunci da wulaqantamu,saboda talakawa ne mu bamu da komai,banda haka ta yaya yaron da bashi a zaune bashi a tsaye game da al'amarin diyarku amma ku rasa sharrin da zaku jefeshi dashi sai wannan,idan banda shi da yasan girman halacci ma waye zai zauna da mahaukaciya....."


"Ke tsohuwa,ki iya kalamanki" afifa ta dakawa momee tsawa da muryar da ita kanta batasan tana da irinta ba


"Tunda har kuna da bakin kare kanku,ai waqa a bakin me ita tafi dadi" saita fidda waya tana kiran anty farheen


"Muna hanya afifa,muna gab da shigowa layin"


"Saikun qaraso" sai ga juya gasu dr mamman


"Abba,don Allah ku jira minti uku,ga raba gardamar nan isowa" jin kalmar afifa ta qarshe ta kada hanjin cikin momee,zatonta ya bata jami'an tsaro kawai suka kira musu kai tsaye,sai ta kama hannun adam tana cewa


"Tashi mu tafi,Allah zai saka mana da wannan qazamin qazafin da sukayi maka saboda kana auren diyarsu"


"Ina zaku?,ku koma ku zauna,ai bakwa tafi muna zarginku ba,gwara a warware gaskiya ko hajiya?" Cewa dr mamman girema.


Jikinta ne ya dauki rawa ta fara kame kame,saidai kafin ta dire kame kamen nata sallamar sãahar ta dauki hankalin kowa.


Sanye cikin wani lallausan yadi da aka yiwa dinkin doguwar riga,da gyale mahadinsa,fuskarta har yau bata cika ba a yadda take a baya,saidai sassanyan kyan nan da baya gushewa kwance saman fuskar tata. Akwai alamu na samun nutsuwa a tattare da ita,sabanin satittikan baya da dukka wata natsuwa tayi qaura daga rayuwarta,ake shirin haukatata,a maidata mahaukaciya zalla,idan ta yiwu ma yazo da qarar kwana,bataga abinda zai hanata ta baqunci lahira ba.


Cikin azama tare da son nunawa duniya shi din wankakke ne,kuma masoyi ga matarsa ya miqe cikin zallar mamaki ya nufeta yana qwala kiran sunanta. Rungumeta yayi nufin yi,saidai kafin yakai ga aikata hakan ya samu tsarabar wani lafiyayyen mari saman fuskarta,sannan ta tattara dukka qarfin data shigo dashi ta ingizashi baya ya fada saman momee dake zaune cikin kaduwa da tsurewa.


Zumbur ya miqe yana shafa wajen,sannan ya maida dubansa a kanta,sanda take tsaye ta kafeshi da fararen manyan idanunta dake dauke yau din da wani irin matsanancin fushi da bai taba ganin irinsa tattare da ita ba


"Baki warke bane sãahar?,subhanallahi"


"Kaine zaka shiga taka haukar yanzun nan,mayaudari maciyin amana,ina neman tsarin Allah daga kai" sai ta fashe da kuka ta soma sulalewa a gurin zata zauna,anty farheen ta riqeta da kyau tana bata baki. Tuni maama ta qaraso bayan ta tabbatar ba mafarki takeyi ba,ta rungume 'yarta tsam tana jero addu'o'in godiya ga Allah


"Ya kamata kowa ya samu waje ya zauna" yaa Saifullahi ya magantu cikin nutsuwarsa,domin ya karanci akwai babban al'amari dake shirin faruwa,komai ya fara bayyanar masa saman fuskar adam da babarsa,sannan ya akayi sãahar take a gidan muhyiddeen duk da tsahon lokacin da aka dauka ana nemanta ba tare da kowa ya sani ba?,ga adam da momee suna matsawa daga bakin qofa?,tamkar yaa zaid ya lura,sai ya matsa yayiwa kansa mazauni daga can hanyar qofar,suka zamana a tsakiya.


A nutse afifa ta qaraso tsakiyarsu ta dire jakar. Lokacin da idanun adam suka sauka a kan jakar sai ga fitsari ya balle masa yana daga zaunen,zazzafar gudawa ta soma qoqarin kufce masa amma ya matseta da kyau,gurbatacciyar ziciyarsa tana gaya masa akwai sauran dama adam,kada ka karaya,muddin baka amsa ba ba wanda ya isa ya tilastaka,koda kuwa a kotu ne.


A gaban kowa sãahar ta matso,ta daga jakar ta zazzage komai ya tarwatse a qasa,wani zazzafan kuka ya taso mata,amma ta danneshi. Daya bayan daya ta soma basu labarin yadda suka fara hadaka a rayuwarsu,yarjajeniyar rashin daukan ciki,canjin halayensa,kamashi da tayi a waya da zuba mata tablet da yayi na zubda ciki,bayyanar ha'incin da yake mata ba tare amma data kama sunan raihanatu ba,azabar daya dinga gana mata har zuwa sanda Allah yayi fitarta daga gidan da taimakon afifa da kuma raihanatu. Kamar wani mahaukacin zaki ya miqe ya soma zage zage,yaa zaid baisan sanda yasa qafa ya kwasheshi ba cikin matsanancin fushi,sai gashi kif a qasa


"Idan ka sake mana magana sai na cire maka harshe" kota ina jikin momee rawa yake,duk sauran qwarin gwiwar da take dasu sun kwaranye sunbi ruwa,don itama wasu abubuwan batasan dasu ba.


Jakar ta fara musu bayani,tana zazzage abubuwan ciki tana nunawa kowa,sai maama ta kasa daurewa,ta rufe fuskarta da hannunta kuka mara sauti yana qwace mata. Duka duka nawa sãahar din take da har zata fuskanci irin wannan cin zarafin cin fuska da zallar cin amana daga gurin da namiji?,ko ita data kawota duniya bata taba fuskantar wani abu da yayi kamanceceniya da wannan ba


"Duk abinda ta fada gaskiya ne,ni shaida ce" muryar raihanatu ta ratsa falon,sai suka waiwaya suna kallonta, idanunta cike fal da qwallar tausayin sãahar din,don itama wasu abubuwan sai yanzu takeji.


Mamaki ya cika momee qwarai,wato raihanatu zata zame mata 'yar kuka?,ta raini makashiyarta?


"Ki daina mamaki momee,ko kina tunanin bansan ba don Allah kike riqe dani ba?,bayan bautar da nake muku kina lissafin sake maidani machine din tatsar kudinki?, bayan kin cinye dukka abinda mahaifiyata ta mallaka,tun tana raye bata da bakin musa miki?" Maganar ta sake zuwarma momee a bazata,lokaci guda ta nemi sukurkuta mata runani,ya akayi yarinyar tasan wannan


"ni zaki butulcewa raihanatu?"


"Dalla malama ki rufewa mutane baki" yaa Saifullahi ya fada cikin muguwar tsawa,ransa baqiqqirin,tamkar zai kifawa momee din mari,hannu Dr mamman ya daga masa,saboda shi wani abuma ya tsaye masa a wuya ya kasa magana,idanunsa qirrr saman fuskar adam,yana tuna girma da nauyin karamcin da ya yiwa rayuwarsa,tarin alkhairai wanda ko sãahar da take matarsa ya hana ya gaya mata,yakance masa


"Nayi maka ne fisabilillahi saboda Allah,ko ummin abba banaso ta sani,kasan su mata,wani qaramin tunani garesu,qanqani abu zai hadaka dasu sai su goranta maka".


Sam basu farga ba,ashe tuni yaa zain yayi kiran mopol,kafin kace wani abu sai isowarsu akaji da sanyo kansu cikin gidan


"Waye yayi hakan a cikinku?" Dr mamman ya tambaya


"Kayi haquri abba,nine" ya zaid ya fada yana miqewa,yanason a hukunta masa adam da mahaifiyarsa hukunci Mafi tsanani da radadi,irin hukuncin da har su koma ga Allah ba zasu mance dashi ba.


"Amma ina zaune ba zaka fara neman shawarata ba zain?"


"Kayimin afuwa abba" yana gama fada ga fita,cikin second biyar suka cika falon.


"Wait please" ya Saifullahi ya fada,ya miqa hannu ya ciro paper,ya zaro pen daga aljihunsa ya dorawa adam da ake qoqarin cukuikuyewa


"Maza rubuta mata takardarta" kai ya girgiza cikin taurin zuciya da taurin kai


"Matata ce,kuma ina sonta har yanzu,don haka bazan saketa ba,saidai......." Bai qarasa fada ba ya Saifullahin ya daukeshi da wani kyakkyawan mari


"Mu zaka gayawa maganar banza da wofi?,wato saboda baka daku ba har kana da qwarin gwiwar yi mana musu ko?" Duk da marin amma sai ya sake girgiza kai


"Saidai ta mutu da igiyar aure na"


"Ba zata mutu ba kuwa,saboda mudin ba jahilai bane,kawai kotu akwai shari'a kuma" ya muhyiddeen da mamakin adam ke sake kasheshi ya fada. Saidai yana rufe bakinsa mopol din ya saukewa adam din wani irin zazzafar mahangurba da lokaci guda ta sauke masa jini ta hanci da labbansa,ta kuma tara masa wani lafiyayyen jini a gefen idanunsa. Ihu momee ta saki tana neman taimakon wai za'a kasheta ita da danta


"Saketa,ka saketa nace karsu kasheka baka da gata" koda momee din bata fada ba zai rubuta,shi kadai yasan kalar azabar da yaji,idanunsa a rurrufe ya rubuta mata saki daya. A fusace ya Saifullahin ya duba


"Don ubanka qarashe mata sauran biyun" dr mamman ne da nasa mamakin ya qarasa daskarar dashi ya daga masa hannu


"Rabu dashi" ya basu umarni a taqaice,daa yaso ya hana a tafi dasu,amma yadda suka nuna rashin nadama kwata kwata bisa fuskarsu yasa ya kasa hana mopol din tafiya dasu.


"So nake a azabtarmin dasu yadda ya kamata,a sassaba masa kamanni shida uwarsa,banason kowa yasan inda suke,kada kuma a daga musu qafa ko na kwana daya,zamuyi waya" yacewa da shugabansun


"Karka damu,sakamakon mummuna ai mummuna ne" shima ya fada cike da jin takaicin adam da uwarsa.


Ko minti biyar basu qara a gidan ba suka tattara nasu ya nasu suka fice a gidan,sãahar ce tabi raihanatu da kallo wadda ta hada nata kayan ta fara yin titi


"Abba bata da kowa a qasar nan,kuma ko yanzun bata da wajen zama,dama suke riqe da ita,na tabbatar kuma ba zasu ci gaba da riqonta ba" wannan yasa suka dauki raihanatun,abban kuma ya tabbatarwa sa sãahar zai kula da nauyinta da rayuwarta,zuwa gaba kadan kuma zasuje ghana a binciko danginta na qwarai,don susan irin riqon da momee tayi mata. Ajiyar zuciya sãahar ta sauke


"Allah yasa su iya wani abu,saboda momee ta cikasu da kyaututtuka,a yanzu kuwa lalacewa ta tattaru a cikin dangi,duk lalacewarka izgilancinka da rashin ganin girman mutane,taka mutane da mugunyar halinka kaida iyalinka,muddin kana ungo ungo,sai idanun 'yan uwa su rufe daga aibunka,a rasa wani tsayayyen da idan kayi ba daidai ba za'a tsaya a tsawatar maka a kuma hukuntaka dai dai da laifinka" kai abban ya jinjina,maganar sãahar tana kan hanya


"Wannan shine yake kawo lalacewar zumunci da tabarbarewarsa,dole sai an hadu za'a gyara,dole sai an hadu an hukunta me qarfi ko mara qarfi,ya zamana kowa baifi qarfin doka ba,Allah ya kyauta,yasa mufi qarfin zukatanmu"


_NOTE:wadannan matsalolin da suke babbar masifa ce suna nan suna ruruwa cikin al'umma,a yanzu dan qanwarki ko dan yayarki yana iya cin zarafinki,uwarsa ta goya masa baya,saboda suna yiwa dangin nan dan ihsanin da bai taka kara ya karya ba,su kansu masu fada aji a dangin sai kaga sun zama hoto,basu da wani amfani saboda ba kowa suke iya juyawa ba,sun wulaqantar da kansu saboda suna tsoron wasu sashe,idan sunyi ba dai dai ba basu isa su hukuntasu ba,ke kuma uwa wallahi wallahi kanki kikewa baqar dabara,kin nunawa 'ya'yanki kowa baida mutunci,babu me gaya musu suji,saboda kema a haka kika taso,kina ganin kinfi qarfin a baki shawara ko a tsawatarmiki,kin ruguza iyalinki da hannunki,bayan babu ranki haka zasuci wahala,saboda masuyi don ganin idanunkin guduwa zasuyi su barsu,kina qabari ke kuma kina amsar query akan tarbiyyar da kika yiwa yaranki,kina qabari ana nan duniya ana alawadai da halin yaranki,abinda kina raye babu me iya fada,kin mutu kin barwa dangi masifa,qila akwai mata a cikinsu,sai kiga yarinya ta kasa zaman gidan miji,ta kasa biyayyar aure saboda a tarbiyyar da uwarta tayi mata batasan biyayya ba saidai ita a bita,sai tsananin rabo yake zaunar dasu,to duka mu sani,dake uwa da kika zama shashasha sauna,wadda ke iya bari diyan cikinta su wulaqanta 'yan uwanta saboda yunwar ilimin addini da qarancinsa,dasu dangi da suke ganin barna su kasa tsaiwa a gyara saboda kowa yana tsoron fadin gaskiya,ta silar haka zumunci ya gurgunce,wallahi wallahi kowa sai ya tsaya yayi bayani gaban Allah,da wanda aka cuta da wansa yayi cutar,Allah ka bamu dacewa,ka bamu ikon tsaiwa akan gaskiya akan mutum ko wayeshi,komai girma da matsayinsa,ka rabamu da kwadayin abun hannun kowa,ka wadatamu da wadatar zuci daga gurinka????_

[02/09, 3:47 pm] +234 810 324 4136: Page 58


*H U G U M A*


Page 56


    Cikin lokacin kowa qoqari yake ya faranta ran sãahar,tamkar rige rige akeyi,kowa yana bakin qoqarin ganin ya sanyata walwala,dukkansu sun fahimci depression ya fara kamata,ta soma wasu attitude da suke bayyana hakan. Anty farheen ita ta tashi tsayin daka a kanta,daga qarshe ta karbeta daga hannun maama,duk da maaman taso a barta da diyarta,to amma farheen din nada wani irin kirki da tausayi,dole ta haqura ta bar mata ita.


      Zamanta hannun farheen yasa ta qaru da abubuwa masu tarin yawa,sannan ta taimaka mata wajen mantawa da wasu abubuwan,tare da fara dawowa cikin saitinta. A lokacin ya muhyiddeen ya samu wani aiki a Scotland,sai duka suka tattara har sãahar din suka wuce can. Koda sukaje din asibiti me kyau farheen tasa yaa muhyi ya duba musu suka fara zuwa ita da sãahar din,akwai sashen guiding and counselling masu kula da matsaloli irin wadan nan da hanyoyin kubutar da tunani daga wannan damuwar,abinka da qasashen da sukaci gaba,watanni kadan saiga sãahar din ta koma dariyarta da walwalarta,ta sake murjewa,gayu ya sake zama a jikinta fiye da kima saboda tasirin zamanta da anty farheen,idan ka ganta saita bala'in burgeki ke da kika diya mace ma,nan da nan anty farheen tayi amfani da wannan damar ta nema mata makaranta da kanta,ta dora karatun mastering degree dinta.


      Cikin shekarun komai yazo ya wuce,saidai babu ta yadda za'a ji ciwo sannan a warke ba tare da ya barwa mutum tabo ba,koda a gangar jiki ne bare kuma a guri me matuqar muhimmanci da sammatsi irin ZUCIYA,zalincin adama gareta yasa ta hadu sa ciwon kai mai matuqar tsanani sanadin alluran da aka dingayi mata ba bisa qa'ida ba,wanda inda ace anci gaba da yinsu,tsaf kwanyarta zata juye cewar likita,wannan tabon shine abinda ya haifarwa da sãahar tsanar maza,tsana me tsanani,babu halitta da takewa bahagon kallo irinsu,ta tsani taji kalmar soyayya,kalmar AURE kuwa tana sanyata jin wani tashin hankali,kwatankwacin mutumin da yaqi ya tunkaro shi,duk wani abu da zai sanyata hulda da maza ta datseshi,wannan ne yasa tunda suka dawo Nigeria tayi zamanta wajen anty farheen dake ji da ita,take kuma sake maidata macen da idan aka kalla sai an sake juyawa an kalla cikin hikima. Batason kowa yayi mata zancan aiki,shi yasa taqi fidda results nata data samu,results me kyau da yayi bala'in burge yayyenta,duk da dama tunda can sunsan ita din bata da wasa ta fannin karatu,hakanan tana da kwanyar da dukka cikin gidan ita da yaa Saifullahi keda irinta,duk da sauran suma ba daga baya ba,wannan yasa kowanne yake riqe da wani babban matsayi,ya kuma tara dukiyar da a qananun shekarunsu idan aka gaya maka yawanta zakayi mamaki,dukka cikinsu babu rago,babu kuma koma baya.


      A wancan lokacin sati guda dr mamman yace su zain su saki adam,su barshi da halinsa,yayi imanin bazai gama rayuwa a daron duniya ya wanye qalau ba tare da Allah ya hukuntashi ba,duk kuma yadda sukaso hukuntashi hukuncin Allah shine gaba da nasu. Hatta da afifa bata bayar da goyon baya ba,ita inda son samu ne,akai adam din muhallin da hatta hasken rana baya shiga gurin ayi masa daurin rai da rai.   


      Sun bar dr mamman aka cewa an sakeshi,amma basu barsu ba saida sukayi watanni uku cur suna karban hukunci a hannun sajoji,kafin sannan kuwa gaba dayansu ba wanda baiji a jikinsa ba,duk wani abu da sukasan ya mallaka ta silarsu sun karbeshi,ciki harda gidan da momee ke zaune,da wanda suka rayu shi da sãahar,sai a sannan suka gane cewa gidan ashe shima ya saidashi,ta yadda idan yabar qasar saidai sãahar taji ana batun ta tashi ga masu gida. Tuni suka sayar da gida,su kuma ainihin wadanda suka siya a wajensa dama baikai ga basu takardun ba,ya karba kudinne kawai,nufinsa sai ranar da zasu bar qasar ya danqa musu ya qara gaba,sukace ba zasu yarda ba,yaa zain yace su nema kudinsu a hannun dan damfarar da suka bawa. Sunsan tako ina family din dr mamman girema ba abun wasa bane,sunfi kuma qarfin wannan gidan bare suce cuwa cuwa sukayi,don haka suka karkata akalar tuhumarsu ga adam wanda a sannan ko gidan da zai kwanta a ciki ya huce tarin gajiyar da sojojin suka hada musu ya kuma yi jinyar raunukan jikinsa bashi dashi.


      A sannan tuni abba ya samawa raihanatu karatu a maryam abacha American university dake garin maradi a jahar nijer,tana can ta dora karatunta daga inda ta tsaya,babban burinta kenan a rayuwa,wanda momee tasha gaya mata bazai taba cika ba,ba zata dinga adashin da batasan ranar kwasarsa ba.


*Dama hausawa sukance ALHAKI KWAIKWIYO NE,ME SHI YAKE BI*


_DUK INDA ZA'A JE AZO KA TABBATAR KAI AKA CUTA,KARKA ZAMA KAINE WANDA KAYI WANANN CUTAR,A RABUWAR AURE 'YAN UWANA MATA,KARKI YADDA IDAN TA KAMA A RABUN YA ZAMANA KECE ME MATSALA KO KECE AZZALUMAR, WALLAHI KIKA BARI HAKA TA FARU KUMA KIKA FITO SAIKIN RAINA KANKI,MUDDIN KE AKA ZALUNTA,KARKIYI KAICO,KADA KUMA KIYI BAQINCIKI,DOMIN ALLAH BAYA KI GYANGADI BARE BACCI_


*_wannan kenan_*


*_Dawowa labari_*


     Juyawa ta sakeyi a karo na babu adadi bayan gama dukka wannan bitar da qwaqwalwarta tayi,gefan da afifa ke kwance ta kalla,kusan wasu matsalolin tare suka fuskancesu ita da afifan,amma sau tari sai taji inama itace afifan?,inama bata taba sanin wani adam ba bare ya shiga rayuwarta ya cutar da ita haka ba?. Tsaki taja qasa qasa bayan fargar da ita da zuicyarta tayi,saita miqe ta sauko daga gadon a hankali ta nufi toilet,cikin ranta tana sake jin yaqini da qwarin gwiwar cewa,ya zame mata tabbas tayi wani abu,har yanzu batajin cewa tayi warkewar da zata doshi wani aikin ko kuma aure,dole tayi hobbasar da zata sake nesantata daga dukkan wata mu'alama da zata sake hadata da azzalumar halittar maza,marasa tausayi da jin qai,marasa amana kuma,dole ta yiwa kanta wannan aikin.


      Daren gaba daya ta raya,da tarin addu'o'in ta da buqatunta jingim wajen Allah,ko kafin ta kammala ma wata irin nutsuwa ta maye gurbin bacin rai da fargabar dake motsa zuciyarta,albarkacin wannan kuma a nan saman abun sallar daddadan bacci ya saceta.


     Afifa ta rigata tashi sallar asuba,batayi mamakin ganinta a kwance a nan ba,saboda ba kowanne dare ne take iya kwanciya ta shareshi dukka tana bacci ba,saita qarasa cikin tausayawa da qauna ta tabata tana kiran sunanta. Idanunta ta bude tana kallon afifa


"Ya shehiya sãahar,a tashi ayi sallar asuba,Allah ya amsa addu'ar nan,ina fatan kin sakani a ciki,Allah ya kawo masoyi na gari" qaramin murmushi tayi duk da cewa daga bacci ta tashi,hakan kuma ya sake qarawa fuskarta kyau,sai da tayi brush ta daura alwala ta fito sannan ta amsa mata


"Allah ya kakkawo,saidai ita afifa akwai wanda take jira" bata tsaya jin amsarta ta tayar da sallah ta barta da baki a bude tana cewa dariya nason kamata 


"Kajimin yarinya zatamin sharri?".


     Dukka wani azkar data saba yi sai data yishi,haka kawai taji idanunta babu wani sauran bacci,duk da cewa ba wani baccin kirki ta samu ba adaren jiyan,don haka ta shafa addu'o'inta ta nade abun sallar,ta dauki wayarta ta koma saman gadon su,tana kallon afifa da idanunta ke rufe,da alama bacci ne sosai a kanta, saita ja duvet itama tana shirin rufa,dai dai lokacin da tex din ahmad ke shigowa wayarta.


     Ko bata buda ba tasan saqon barka da safiya ne,taja qaramin tsaki,tana tunanin sai yaushe zai gaji da naci yace ya haqura da ita?,ba amsa,don haka ta share saqon bayan ta buda wayar.


     Watsapp tahau zata buda wani qaramin document na addu'o'i da anty farheen ta turo mata,yana da dan nauyi,don haka da tayi clicking akai,sai ta fita da zummar rage jira kafin ya kammala buduwa.


      Haka kawai ta samu kanta da buda jerin list na mutanen da sukayi status a safiyar ranar,duk da cewa kuwa ba dabi'arta bane hakan. Sunan mr sadeeqa yana sama sama,auntie din su nurain 'ya'yan yaa Saifullahi. Sam ta mance da matar a rayuwarta,duk da cewa tana da kirki qwarai,tun kafin tayi aure lokacin da takanje gidan yaa Saifullahi din,wani lokaci ita ke kaisu school da safe,a nan suka dan saba da ita saboda matuqar kirkinta,sai kuma dabi'arsu tason yara tazo daya,wannan ya sanya suka dan saba suke gaisawa,har sukayi exchanging numbers.


      Batasan ya akayi ba hannunta ya taba status din mrs sadeeqa,take ya bude,hotone na wata baby girl,duk da cewa hoton ya danyi blurry kadan,amma hakan bazai hanaka iya gane kyan yarinyar ba,tayi rubutu a qasan hoton kamar haka


_she has being suffering and battling epilepsy,she is looking for a good nanny,praying for an easy recovery my class cute angel_????. 


      Epilepsy qwaqwalwarta tayi mata tariyar maganarsu ta jiya da sukeyi da afifa kenan kafin ta fita,take tausayin yarinyar taji ya taba zuciyarta duk da bata iya ganin fuskarta sosai,fingers dinta guda biyu ta saka tayi zooming hoton,still dai it was blurry,hakanan kawai tayi replying status din da cewa


_"is that serious?,she's looking for a Nanny"_ sai data tura saqon kuma sai tayi shuru,ita kadai tana tunanin meye amfanin tambayar data tura. Da sauri ta koma ta jerin charts dinta da zummar gogewa,amma sai ta tarar mrs sadeeqa din tuni ta gani,har ma tana typing wani abu,hakan yasa ta haqura ta koma duba document dinta da take budewa,amma kuma hankalinta nakan inbox din mrs sadeeqa.


     Har zata buda taga shigowar saqo daga mrs sadeeqa din. Sake fita tayi ta duba 


"Yeah,she's my student,ina tausayinta sosai,akwai wata ne daga bangarenki?" Tausayin data darsu a zuciyarta taji ya sake motsawa,a taqaice ta tafa mata


"No,but zan bincika,i will back to you idan na samu Allah ya bata lafiya"


"Ameen,thanks for your concern". Kashe data din tayi,ya dudduba addu'o'in sosai,zuwa lokacin garin ya fara haske,sai ta kashe wayar gaba daya ta sake gyara kwanciyarta ta kwanta tana rufe idanunta da fatan samuwar baccin.


       Bacci tayi sosai,har na kusan awanni hudu,wanda qarshen baccin yazo mata da mafarkin da ya sanyata farkawa. Miqewa tayi ta zauna sosai tana duban gefan afifa,bata a gurin,tabi dakin da kallo,da alama ma harta gyara dakin,gadon da take kwance a kai ne kawai bata gyara ba. Hannunta ta sanya ta tattare gashinta daya zame daga band din data matseshi dashi saboda santsinsa,ta daureshi gudi daya tana sauke qaramar ajiyar zuciya,tunaninta na komawa baya kan mafarkin da shine silar farkawarta a yanzu,zuciyarta cike fal da mamaki,to meye hadinta da yarinyar da bata taba ganinta ba sai dazu a status din mrs sadeeqa da har zata yi mafarkinta?,ko a dazun ma bata gama tantance fuskarta ba,kamar yadda a mafarkin ma bata gama ganin fuskarta sosai ba. 


"La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" ta fada a hankali,sannan ta zamo ta sauka daga gadon,har yanzu zuciyarta bata daina mamakin yanayin data ga yarinyar a mafarki ba. Kuka takeyi sosai tana riqo hannunta,yayin da ita kuma take qoqarin zame hannun nata ta tafi ta barta,daga bayan yarinyar kuma wata matace take biye da ita da sharbebiyar wuqa tana son caka mata. Da wannan tunanin ta isa toilet din,ta ciri brush ta matsa toothpaste ta fara wanke bakinta,har yanzu tana nacin son gano abinda mafarkin ke nufi amma ko daya tunaninta bai iya hasaso komai ba,to shin me ma zata hasaso din?,bayan batasan wace yarinyar ba,daga qarshe sai ta tattara tunanin ta watsar,ta barwa ranta cewa tsabar son yara da take dashi a jininta ne,da kuma yadda zuciyarta ke da rauni akan dukka abinda ya shafi yaro.


       Wanka tayi gaba daya sannan ta dawo dakin tana shiryawa,afifa ta shigo da dan tray data shiryo breakfast dinta a kai,hannunta daya riqe da waya tana amsawa. Idanunta akan fuskar sãahar din harta qaraso,sai ta miqa mata wayar muryarta can qasa tace


"Please" hadi da karyar da kai gefe daya alamun roqo. Kafeta tayi da idanu tana son nuna mata bata kyauta mata ba da zata sanyata yin abinda batayi niyya ba,sai kuma daga bisani ta miqa hannu ta karba wayar,don afifa ce tafi qarfin komai a wajenta,ta kara wayar a kunnenta tana qoqarin tsane jikinta da qaramin towel.

[02/09, 3:47 pm] +234 810 324 4136: Page 59


*H U G U M A*


*_TABARMAR ?ASHI_*??


No comments