Breaking News

Tabarmar Kashi Book 1 Page 53-54

 


Page 53



Sai kuma ta daga kai ta kalli adam din dake tsaye qyam a kansu yana duban alluran


"Bani tissue mana" amsawa yayi da to cikin hanzarin da baiso ta aiwatar da wani abun da zai kawo kuskure wajen yin allurar,ya ciro tissu din ya bata,ta karba ta dora a bakin tsinin allurar,ta fara zirarawa ruwan zuwa cikin tissue din data linkata,sai data qarar da ita a ciki tas sannan ta zare allurar,tayi hanzari danne tissue din a qasan cinyarta gudun kada ya fahimci jiqewar da tayi.


Sanda yaga ta kammala wani dadi ne ya kamashi,ko yanzun hankalinsa ya samu ya kwanta,yaukam zaiyi bacci abinsa sosai,yasan har gobe zuwa wajejen azahar tana cikin bacci da tambele idan ma ta farka din kafin sannan,wala'alla ma ya gayyato wata cikin 'yammatansa idan kowa yayi bacci ta tayashi debe kewa,da wannan tabbacin gaibun daya samu ya fita a dakin abinsa hankali kwance.


Kwanciyar hankalin da afifan ta gani a fuskarsa sanda yake fita din ta sake dasa qaqqarfan zargi a ranta,sai ta bude alqur'anin cikin nutsuwa ta fara karantawa da madaidaicin sauti me cike da nutsuwa.


Kusan awa guda cur ta shafe a hakan,a hankali taji wani sassanyan hannu ya dafa hannunta dake saman qur'anin,kafin ta daga kai taji ta kira sunanta da wata iriyar siriryar galabaitacciyar murya


"Bestie,kema wai kin yarda ni din mahaukaciya ce?,na haukace?" Wasu irin birkitattun hawaye ne suka shiga silalowa afifa,banda ta sanya hannunta ta toshe bakinta da kuka mai qarfi zata barke dashi,hannunta na saman bakinta tana girgiza kai,sai kawai ta rungume sãahar din a jikinta tana sakin kukan data boye sautinsa


"Bazan taba yarda ba bestie,koda ma da gaske ne ina qaunarki a hakan" kuka dukkansu suka saki rurus,suka dinga rerashi babu wani me rarrashin wani,har tsahon wani lokaci kafin afifa da idanunta sukayi jazur ta magantu


"Bestie,wanne irin mummunan abune kika yiwa adam ya yanke hukuncin mai dake haka?" Ido ta lumshe ragowar hawayen dake maqale a idanunta masu zafi suka gangaro,tabba inda ace ruwan hawaye yana qarewa da tuni nata ya jima da qarewa


"Wannan damuwar da kika tafi kika barni a cikinta,wadda nayi alqawarin gaya miki ita,ashe itace zata zaftaro bisa kaina,tayi shirin kaini lahira koda ban shirya ba" a nutse ta rattabawa afifan komai. Wani mugun birkicewa afifan tayi,ta miqe zata sauka a gadon da zafi zafinta, fuskarta gaba daya ta sauya kamanni.


Da sauri sãahar ta cafko hannunta,don tasan halinta sarai komai ma zata iyayi


"Ina zaki?"


"Adam din zanje na samu ayita ta qare,tsinanne matsiyaci dan wuta" girgiza kai ta hauyi da sauri


"Tunkarar adam a irin wannan yanayin abune me hatsarin gaske,idan baka iya kama barawo ba sai shi barawon ya kamaka,sai kinbi ta takatsantsan da hikima sosai kafin ya zamana mai laifi red handed,baki tsoron kema yace dalilin kwanan da kikayi kin shafi aljanuna ko ciwon haukata?" Sanyaya jikinta yayi,lallai a yadda idanun adam suka rufe babu abinda bazai iya aikatawa ba,yadda ya matsu da jakar koma meye akace zaiyi zaiyi din,saita koma ta zauna tana ci gaba da kukanta,zuciyarta kuma ta zurafafa da tunanin daukan fansa.


Da qyar suka lallashi juna,ta kama sãahar da jikinta sam ba qwari ta rakata toilet,ta daura alwala tazo ta rama sallolin da ake binta,afifa na gefe tana kallonta tana kuka, sãahar din da bata wasa da sallah?,duk tsanani duk rintsi bata yarda lokacin sallah ya wuceta ba ba tare da ta yita akan lokacinta ba.


Abincin da raihanatu ta bayar adam ya shigo dashi tun dazu ta buda,ta saka sãahar din a gaba akan sai taci,da qyar tayi cokali biyar,saboda cikinta ya sake wani mugun tsukewa,baya iya daukan abincin sam me yawa,dama kuma tun asali na gwanar abincin bace.


Daga ita har sãahar ba wanda ya rintsa a daren,sãahar din nata bat labarin irin azabobin da adam ya gana mata,tayi kuka tayi kuka har ta bawa uku lada,a daren ta gama shirya yadda komai zai tafi,tsarin kuma ya yiwa sãahar din itama.


Washegari da adam din daya kwana da wata macen suna holewa kan gadon aurensa ya shigo ko a fuska bata nuna masa komai ba,saima zallar tsoron kwana da sãahar din data nuna masa ta dinga ji. Murmushin jin dadi da samun cikakkiyar nasara ya saki yana sauke dubansa ga sãahar daje kwance shame shame kamar dai yadda take a jiya,a yanzun sauran tsoronsa ya kau,abinda ya rage masa ya sake matsa qaimi kawai ta bashi jakarsa kafin yayyenta su iso su wuce da ita wani banzan asibiti. Afifa ce dama tsoronsa,yasan halinta tsafff, za'a iya fuskantar matsala ta sanadinta,amma a yadda yaga tayi firgai firgai ta kuma ce a jiyan batayi bacci ba,alamu sun nuna ba zata iya sake kwana ba(baizan qarfin aminci da soyayyar dake tsakaninsu ta ginu sosai bisa tubalin Allah da ma'aiki ba,ba abota irin ta wannan zamanin ba,iya fatar baki). Ilai kuwa yadda ya zata hakance ta afku,afifa ta hada kayanta tayi musu sallama bayan ta gama tsara komai ta fice a motarta.


Ba gida ta wuce ba,can cikin kasuwar qofar ruwa ta zarce,ta kuma sauka kai tsaye gurin mutumin da yafi kowa qwarewa wajen yanka muqullin da zai dace da kowacce qofa, cikin lokaci qanqani aka gama yanka mata saboda kudin data zuba ta biya,ta karba ta dawo gida,ta hada wasu kaya ta baiwa maama dake shirin tafiya gidan,tace ta ajiiye mata dakin sãahar din gobe zata koma ta sake kwana da ita


"Kada ta barnatar miki fa" hawaye ne suka ciko idanun afifan,mutum da hankalinsa amma ya sanya kowa yana mata kallon tabbabiya


"Ba zata taba ba in sha Allah" shuru maaman tayi tana juya kayan


"Na rasa abinda yasa har yanzu naqi ji a jikina sãahar ta samu tabin qwaqwalwa,jiya muna hanya da abbanku dana fada yace shaidan keson yimin wasa da imani na,na yarda da qaddara ne kyau ko akasinta"


"In sha Allah nan kusa bestie zata dawo cikinmu muci gaba da rayuwa kamar kowa" abinda afifa ta fada kawai kenan tana sharce hawayen fuskarta.


Fitar maama daga gidan ya baiwa afifa damar shiga dakinta ta dauke jakar ta canza mata muhalli,saboda gudun abinda zaije yazo,ta gama sarawa girman sharrin adam,tasan bazai taba rasa kawowa a ransa jakar na gidan ba,zai kuma ya tsara komai da zai sanya a aminta dashi a damqa masa ita.


Kuka sosai ta zauna tana yi sanda ta gama qarewa kayan dake cikin jakar kallo,burinta kawai taga ta watsawa passport din wuta da sauran takardun,to amma suna buqatar evidence,don haka tayi haquri ta tattarasu ta kaisu cikin motarta.


Kamar ko yaushe bayan kowa ya tafi yaja qofar ya kulleta,don ba kwana dakin yakeyi ba sai idan yana da buqata. Cikin sanda ta bude kayan da maama ta ajjiye cikin drower dinta,wanda tunda ta shigo dasu take ankare dasu tare da fatan kada hankalin adam yakai kai. Ta warware kayan a nutse ta ciro muqullin ta maidasu gurinsu,ta duba daya bangaren kayan nata ta ciro hijabi ta sakawa jikinta, sannan ta fara takawa cikin sanda da takatsantsan,qirjinta yana wani irin bugawa,bakinta dauke da tarin addu'ar samun nasarar ficewa daga gidan ba tare da kowa ya ganta ba,tana takawa iska na yawo da ita saboda jimawa da tayi rabon da tayi doguwar tafiya,ga ciwo da uban allurai rashin cin abinci da uban tashin hankalin da yasa ta zabge ta rame.


Cikin nasara ta bude qofar dakin da muqullin,ta budeta a hankali ta fara takowa ta falon,motsi taji me qarfi daga bayanta,abinda ya kada hantar cikinta kenan ta waiwaya da sauri har tana shirin kaiwa qasa saboda tsananin razana.

[02/09, 3:47 pm] +234 810 324 4136: Page 54


*H U G U M A*


*_TABARMAR ?ASHI_*??


54


    Raihanatu ta gani a tsaye,itama jikinta rawa yakeyi,plate din data debo suna shirin watsewa a hannunta. Bud baki sãahar tayi zatayi magana raihanatu tayi saurin dora yatsanta saman labbanta alamun sãahar din tayi shuru,sai ta maida plates din saman dining,ta sauko da mugun hanzari cikin wani taku na sand'a,ta qaraso inda sãahar ke tsaye ta finciki hannunta da mugun sauri ta bude mata qofar parlor din suka fice.


     Tsakanin baranda da farfajiyar gidan suka ja cak suka tsaya,dukkansu kowa yana maida numfashi,qirjinsu yana wani irin dagawa


"Mai gadi.....yana nan anty,bari na dauk....ke masa hankali" bata tsaya jin ta bakin sãahar din ba ta lallaba tabi ta cikin flowers din ta zagaya bayan dakin me gadin. Dutse ta samu me dan girma ta jefa ta saman roofing din ya bada sauti qwaalll,sautin da ya dan ja hankalinsa,sai yayi tsaki yaci gaba da abinda yakeyi. Sake daukan wasu dutsunan har biyu tayi ta sake jefawa,ya sauka kuwa a tare,sai ya fusata ya miqe don ya zagaya ya duba daga ina jifan yake,kafin ya qaraso tuni ta fita ta koma wajen sãahar,ta sake jan hannunta gudu gudu sauri sauri,ta bude mata qofar gate din tana magana cikin ruwan hawaye


"Jeki anty,Allah zai dafa miki,ubangiji yayi miki sakayya,duk da ban gama sanin kan komai ba amma zuciyata da gangar jikina sun gama gayamin me yake faruwa,ko yanzun yana dakinki da wata,ko iya wannan sakayyar Allah ne kadai zaiyita" tana gama fada ta maida qofar cikin matuqar takatsantsan ta rufeta ta koma cikin da sauri ba tare data bari me gadin ya ganta ba.


    Bibbiyu ta dinga gani cikin qwayar idanunta,jiri sosai ya dinga dibanta ta fara hada hanya. Da hanzari afifa dake zaune tana jiranta tsahon sa'a guda ta buda murfin motar ta fito da mugun sauri,ta tarbeta a hanya ta riqeta qam ta sanyata cikin motar,dai dai lokacin da numfashinta ya fara sauyawa,alamu suka fara nuna tana neman suma ne,wanann ya saka afifa tayar da motar da mugun gudu suka bar layin.


     A lokacin babu wanda ta gayawa abinda ke faruwa,saboda bataso a sani din,don taci alwashin saita wujijjiga rayuwar adam din. A yanzun da sãahar ta sume mata dole ta nemi taimakon wani. Kai tsaye anty farheen ta kira,ta gaya mata asibitin da take tace tazo yanzu don Allah


"Wa kikai wannan asibitin me nisa?,duk hospitals din da muke zuwa na kusa damu"


"Ba lokaci anty don Allah ki qaraso yanzu,its urgent"


"Ba laifi,gani nan" ta fadi maganar tana ajjiye wayar. Muhyiddeen baya nan already,don haka ta barwa masi aikinta duka yaran,ta tayar da driver suka fito daga gidan cikin motarta.


     Ba qaramin razana tayi ba lokacin da afifa ta gama zayyane mata komai,kuka sosai ta saki ita kanta anty farheen tana tsinewa adam din


"Dole mu dauki mummunan matakin shari'a a kansa,tabbas baici bulus ba" kai afifa ta girgiza


"A'ah anty,mubi komai a sannu kamar yadda sãahar ta shawarta,ni kaina yanzun tsoro yake bani,kaidinsa ya wuce tunaninmu,duk yadda nakai ga tsanarsa da qin jininsa......ban taba kawowa zai iya aikata haka ba,so sai mun iya takunmu,tsaf zai iya wanke kansa a wajen iyayenmu maza da 'yan uwanmu,bari kiji plans dina" a nutse ta warwarewa farheen shirinta,shirin ya yiwa farheen din sosai,kuma itace hanya guda daya da zata iya sanyawa adam ya tona asirin kansa da kansa.


     Anty farheen bata bar asibitin ba sai kusan qarfe daya saura na dare,tace gobe zata dawo asibitin secretly ta kawo musu breakfast,don so samu a gobe ta maida sãahar gidanta aci gaba da yi mata treatment a can,don batason rashin ganin gilmawar afifa ya sanya adam ko wani cikin 'yan gida ya fahimci akwai wani abu,basason hakan ya kasance,har sai zuwa sanda suka tsara faruwar hakan.


^^^^^^Sam adam bai waiwayi dakin sãahar ba tun bayan tafiyar afifa,duk da yasan afifan a yau ta tafi gida,sai ya tattare shi da karuwarsa suka qule dakinsa sukaci karensu babu babbaka. Kwata kwata bai doshi dakin ba sai bayan sallar asuba,ya miqe yana jiri saboda buguwar da yayi a daren jiya,da kuma masha'ar daya aikata son ransa.


     Zama yayi a bakin gadon yana jiran fitowarta,amma sai yaji shuru,don haka ya miqe ya nufi bandakin yana zage zage


"Na kusa kawo qarshen matsalata,tsaf zan iya hallakaki muddin kikace zakici gaba da boyemin jakata,ke kiyi asarry rayuwarki ni nayi asarar dukiyata" wata muguwar razana yayi lokacin da yaga bandakin wayam,ya fidda idanunsa waje kamar yana shirin zurarosu qas,ya waiwaya da sauri yana tuna cewa lokacin da yazo shiga dakin baifa budeshi da maqulli ba,yana turashi yaga ya bude,a zabure ya fito yana kwarara ihu kamar hauka sabon kamu,yayo falo yana qwalawa rahinatu kira.


     Tunda ta idar da sallar asuba take zaune tana zaman tsammanin jiran jin makamancin wannan kiran,sai da tayi addu'ar neman samun tallafin nutsuwa daga ubangiji ta shafa sannan ta fito,a sannan har ya gagara zaman jiranta ya bankado qofar dakin,kadan ya rage ta daki fuskarta 


"Ina sãahar take?" Ya tambayeta cikin tsawa


"Tana dakinta yaya" ta amsa masa a nutse,kamar da gaske batasan komai ba,ido ya zaro waje


"Tana dakinta zanzo ina tambayarki inda take don ubanki?" Cikin nuna zallar mamaki tace


"Bata dakinta kuma yaaya?,to ina ta tafi?, innalillahi wa inna ilaihi raji'un" duk sai ta nuna rudewarta a fili


"Ni tunda ka shigo kacemin na wuce dakina,kada ka sake ganin gilmawata ai ban sake fitowa ba yaaya sai yanzu daka kirani" yadda yaga ta rude shine ya sake gigitashi ya kuma rudashi,ya saki qofar da sauri yana barin wajen hadi da kama gashin kanshi da hannunsa bibbiyu kamar wanda yasha cocaine ya bugu da kyau,haka ya dinga zirga zirga kafin ya afka dakinsa.


     Tana nan tsaye taji hayaniyarsu shi da kilakin tasa,kafin zuwa wani lokaci taji yana jibgarta,ba jimawa sai gata ya jawota kiiiii zuwa falon gidan da wasu gantalallun kayan bacci da basu da maraba da tsirara


"Tsinanniya mitsiyaciya,ke kika jawomin,saida na gaya miki kada ki bani abun bugarwa,a situation din da nake ciki bani da buqatar sa amma saida kika bani,yanzu kina shirin jazamin masifar da tafi kowacce girma,fita ki barmin gida" haka ya korata ko kayan jikinta bai bari ta canza ba. 


     Dawowa yayi yaci gaba da yin safa da marwar cikin tashin hankali


"Ya akayi ta fita daga dakin dana kulleta?,ina ta tafi?" Tambayoyin daya dinga yiwa kansa daya gama cakewa kenan,sai ya juya a gurguje ya durfafi me gadi yana tuhumarsa,saidai ya tabbatar masa yau din banda afifa data fita a gaban idanunsu dukka ba wanda ya sake fita daga gidan.


     Qaramin hauka ya dinga yi tuburan, raihanatu na maqale tana hawaye,gami da janjantawa kanta game da muhallin da rayuwa ta jefota,dangin uwa marasa saiti,marasa imani jahilai masu shegen son kansu da kwadayin abun duniya fiye da komai.


      Sanda ya kirata yace itama ta fito tabar gidan yana auna mata zagi,hakan dadi yayi mata,don duka tsoro ya kamta,ganin gidan ba kowa sai ita dashi yanata kuma wani abu kamar me tabin hankali,don haka a gurguje ta zira slippers dinta bata ma tsaya daukan komai nata ba ta qara gaba.


*_BAYAN AWA UKU_*


      Mutum takwas ne cikin falon,ciki harda afifa maama da dr mamman sai yaa muhyi da yaa Saifullahi,wanda ba wanda yasan da zuwansu a yau din,sai kuma gashi sunzo sun tarar da tashin hankalin rasa sãahar.


      A falon saika rasa tantance waye yafi wani shiga tashin hankali?,maama Kuka kawai takeyi wiwiwi wanda yake taba ran afifa,yakeson kuma ya karyar mata da gwiwarta. Duk bayan mintuna saita saci kallon adam da yake shirin zaucewa,ya kasa zama ya kasa tsaiwa,sai kai kawo kawai da yakeyi yana kiran sunan Allah,ta sake sarewa,ta kuma sake jin tsoron kaidin mutum,lallai dan adam me buhun sharri ne,ba wanda bai tausayawa adam din ba a falon yanayin da suka ga ya shiga,ba tare da sanij cewa shine ummul aba'isin faruwar komai ba 


     Zaman da sukeyi a yanzu na zaman jiran tsammani ne,bayan sun bada report na batanta a kafafen yada labarai da kuma police station guri guri.


"kayi haquri adam,in sha Allah za'a ganta cikin aminci" abba ya fada cikin son qarfafawa adam din gwiwa,duk sa cewa shi dinma bawai yana da qwarin gwiwar bane


"Abba bansan ya akayi ta fita ba,ina ta tafi?, innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya fada da madaukakiyar murya,kai afifa ta kawar ta tabe baki,tabbas bawai yana cikin tashin hankali bane saboda batan sãahar,yana cikin tashin hankali ne kawai saboda jakarsa.


      Wuni sukayi ranar a haka,har zuwa dare,ba wani labari ko alamun samun sãahar.


     Ta fannin afifa duk da tanason komawa gidan yaa muhyi su kwana da sãahar din wadda tuni anty farheen ta samo likita ya fara bata kulawa ta musamman,to amma zamanta tare da maama dake cikin tashin hankali yana da matuqar amfani,tunda tasan ko ba komai zata debe mata kewa ta kuma kwantar mata da hankali,don haka ta bita gida,amma tana tuntubar anty farheen akan duk yanayin da ake ciki,ta shaida mata tana samun sauqi da kuma kyakkyawar kulawa. Lokaci lokaci take satar jiki taje taga sãahar din. Sosai sãahar din ke murmurewa tana sake samun lafiya,saboda kulawa ta musamman da anty farheen din take bata,duk da cewa sãahar din bata da aiki sai koke koke,saboda matuqar dimuwa da kaduwa ta shigeshi akan abinda adam yayi mata,gaba daya so take ta zama depressed,amma dagewar anty farheen da jajircewarta yanata aiki a kanta,baji ba gani haka take bata kulawa da shawarwari


"Um um ummin abba,baki godewa Allah ba kenan?,baki godewa ni'imarsa ba?,ya kubuto dake daga sharrin da bakisan iya zurfinsa ba?,da yawan koke koke zaki sakawa ubangijinki?"


"Dole nayi kuka anty,ashe dama haka maza suke?,dama masoyi yana iya komawa maqiyi mafi ban tsoro me muni?,ashe su din basusan halacci ba?,basusan soyayya ta ainihi ba?,basusan tausayi imani da jin qai ba?,ashe adam zai iya yimin haka anty?,me yayi saura kuma a duniya?,tunda har adam zaiyi haka,wanne masoyi ne bazai iya cin amanar masoyi ba?" A lokacin dukka bayanin da zata yi mata bazaiyi amfani ko tasiri ba,don haka sai kawai taci gaba da lallashinta cikin hikima da kwantar da kai.


KOMAI NISAN JIFA


      Bayan zamun tabbacin warwarewar sãahar,suka tabbatar ta dawo cikin hayyaci da nutsuwarta,da taimakin likitansu dake duba mafi akasadin matsalar data shafi familyn gaba daya. Ba abinda afifa ta boyewa Dr usman,ta kuma nemi taimakonsa ya zama jagora wajen zama MABUDIN tonuwar asirin adam,ba tare da jinkiri ba ya amince,don shi kansa al'amarin yayi masifar tsimashi tare da tayar masa da hankali matuqa da gaske.


       Tun cikin satin ta tayar da maganar zuwa duba filaye da kadarorin sãahar,tace


"Ya zaid,ya kamata a duba,kasan mutane babu amana, qilan wasu suji labarin batanta suje suyi rub da ciki a kai" zaid din ya gamsu da zancanta,yace zai samu lokaci yaje ya dudduba din.


      Lokuta lokuta sukanje gidan,basu barshi hakanan ba,kamar ko wanne lokaci,yau ma sun je gidan kusan su dukansu,banda zaid da yace zai fara wucewa duba filayen sãahar din,abinda yayi matuqar yiwa afifa dadi,ta dinga kallon adam da yaketa mazari irin na rashin gaskiya a tsakaninsu,tana jiran jin dawowar zaid.


       Maama na tsaka da jajensa kan ya dade ya iso gidan,cikin wani irin yanayi daya tabbatarwa afifa boom din data dana ya soma tashi


"Lafiya?" Maama ta tambayeshi


"Akwai matsala maama,lokacin dana isa na fara da duba filayenta daka bakin titi,amma ga mamakina kusan fiye da rabinsu an tada gini a cikinsu harma anyi nisa,ko dana zauna na fara bibiyar lamarin,na nemi haduwa da ainihin masu filin,na samu ganin mutum uku a ciki,don suna gurin suna duba aikin da akeyi musu,kuma dukkansu sun shaida min siyan fili sukayi,kowanne kuma ya nunamin takardar shaidar mallakar filin original copy" wani irin sauti cikin adam din ya bayar,wanne irin sabuwar masifa ce kuma take shirin afko masa bayan yana tsakiyar wannan dumu dumu bai gama fita daga cikinta ba?,dakiya da qarfin hali ya aro,cikin nuna bacin rai gami da mamaki yace


"Kai,wanne irin rainin wayau ne wannan?,me yasa mutane masu da kirki basu da imani?,daga batan baiwar Allahn sai kawai su hau gine mata filaye?"


"Basu x laifi,kuma suna da gaskiya,don kowanne ya shaidamin a hannun mijinta ya samu damar mallakar filin,ya tabbatar musu kuma babu wata matsala" ai baisan sanda ya miqe ba,ya soma fada yana yarfa hannu,sam ya manta a gaban su waye yake 


"A gidan ubanwa suka sanni?,ni zasu yiwa sharri saboda sunga Allah ya rufamin asiri?,muna zaman lafiya da soyayya da matata?,ko su waye wlh bazan qyalesu ba,tabbas saina kaisu qara kotu" relaxing ya zaid yayi yana qare masa kallo


"Ka kwantar ds hankalinka,ko nima bazan qyalesu ba sai nayi shari'a dasu,so shi yasa a gobe na yanke hadaku ku duka acire me gaskiya da mara gaskiya,tun kafin ta ritsa da wanda baida laifin komai" mummunar faduwa gabansa yayi,amma ya maze


'"hakan yayi,ko baka hadamu ba ni zan nemesu,na kuma nemi fansar batamin suna da sukeso suyi" sai yaci gaba da fada,ya kasa shuru hakanan ya kasa nutsuwa ya zauna guri guda.


      Daren ranar bacci barawo duk qwarewarsa bai iya satarsa ba,ya dauki wayarsa ya kira momee ya zayyane mata komai


"Kada ka wani damu,kuje din,iyaka ka murje idonka kace baka sansu ba,zanma shigo gidan goben saboda ka samu supporting " akan hakan suka samu matsaya,saidai abinda basu sani ba,tuni afifa ta gama nata shirin na goben,don ko da suka tashi zuwa,tare da Dr suka taho,bisa shawarar adam din ya bada report na duka lalurar sãahar din ya duba da kyau. Tace hakan yana da kyau,idan da yiwuwar suyi attaching nasa cikin cigiyar neman sãahar da akeyi,qila wannan ya sauqaqe samunta da wuri.

[02/09, 3:47 pm] +234 810 324 4136: Page 55


*H U G U M A*


No comments