Breaking News

Tabarmar Kashi Book 1 Page 51-42

 Page 51


     "Mahalan,mahalan(ku kwantar da hankali)" ya fadi da sigar lallashi



"Aiki mukeyi,kuma kukanku zai iya bada matsala,ayi haquri da qaddarar Allah,mijinta yana bakin qoqarinsa qwarai da gaske,kuma ko yanzu ma an fara ganin nasara,son ba ko yaushe suka sakata surutan da bige bige ba".


       A nan suka zauna cikin matsanancin halin kuka da jimami,shi kansa gidan gaba daya ya sauya yayi wani iri,dama raihanatu tana bakin qoqarin tsaftaceshi da kula dashi,ita kanta tana zaune rakube daga gefe,tausayin iyalin duka ya kamata ganin tashin hankalin da suka shiga da cutar bogin da aka laqabawa matar da bataji ba bata gani ba.


"Ko zan iya ganinta?" Maama ta fada cikin zallar alhini da tashin hankali. Kallon juna adam da malam usama sukayi,sai ya maida dubansa ga maaman


"Bako yaushe ake shiga gurinta ba,saboda hakan yana sakata yunqurin guduwa,da kuma surutai marasa kan gado,amma yanzu barin na fara shiga nayi mata wasu addu'o'i,yadda ba zata cutar da ku ba koda kun shiga din" ya fadi hakanne saboda allurar da aka danqara mata sunason ta fara aiki,jikinta ya saki gaba daya,yadda ko magana ba zata iya dasu ba barw ta fadi wani abun da zata shanshano ainihin batun.


      Lokacin da ya shiga dakin ya isketa allurar ta fara mata aiki,ya hadiyi wani yawu muqut yana qare mata kallo,kullum yaga yarinyar sai ransa ya biya,tana da wani mugun kyau da kyakkyawar suffa,Allah Allah yake wataran ya samu dama kamar hakan nan sanda bata da sauran qarfi shima yadan dandanata,ya rage qishirwar dake ransa,baisan ma wanne irin rashin rabo bane ya sanya adam din yake mata wannan izayar,shikam inda shine ya mallaki zuqeqiyar mace irin wannan,baisan wanne asarar bace zata sakashi yayi sakacin da zai rasata ba,ai shi kam zai iya cewa ma Allah ya sallameshi a duniya dai.


      Kamar masu cutar rashin kuzari haka suka shigo dakin,su hudu ciki harda afifa da maama,gaba daya dakin a hautsine yake da fasassun abubuwa,wanda duka setup ne. Wani irin kuka afifa ta saki,ta kuma durfafi sãahar a gigice ganin yadda gaba daya ta koma zararriya sak,dakatar da ita malam usama ke shirin yi yana fadin


"Subhanallahi,karki qarasa gareta,na samu nayi musu addu'o'in kashe jiki,karki zaburar dasu" saidai kafin ma ya qarasa bayaninsa tuni ta isa. Rungume sãahar din tayi cikin jikinta,dumin afifan yana ratsata ta sauke wata iriyar qaqqarfar ajiyar zuciya,ta lumshe idanunta da suka kasa sauka daga fuskar maama dinta,tanason koda motsa labbanta ne ta fadi kalmar da maama zata fahimci diyarta lafiya lau take amma ta kasa furta komai.


       Irin kukan da suka wuni sunayi zai baiwa dukkan me imani tausayi,don ko raihanatu haka ta dinga boyewa a kitchen tana tayasu kukan, tare da jin qaqqarfar tsanar momee da shi kansa adam din,duk da kasancewarsu jininta. Abinci kuwa ba wanda ya iya sakawa cikinsa dukkansu,har zuwa dare suna zaune a gidan,daren da ya riski sãahar batasan ma me akeyi ba,tana can wata duniya ta daban da adam da likitocinsa suka kaita.


      Da qyar Dr mamman ya lallabasu maama da afifa suka wuce gida,da nufin gobe sa dawo. Hankalin adam ya tashi sosai jin su yaa Saifullahi suna can neman asibiti me kyau da zasu dauketa su kaita,hakan ya tabbatar masa asirinsa yana gab da tonuwa,sannan kuma yana gab da tafka asarar da gwara mutuwar sãahar a wajensa akan yayi wannan asarar ta dukiyar daya narka zuwa dollar,ga passport dinsa na yaransa dana matarsa duka a hade. Kwana maama tayi tana kuka,tana ganin abun kamar almara, innocent sãahar dinta,wadda duka duka shekarunta tsakanin ashirin ne zuwa ashirin da daya,idan tayi wuta sa biyu amma wannan mummunar qaddarar ta afka mata.


      A daren gaba daya afifa bata samu bacci ba itama,duk inda ta juya fuskar sãahar take gani,kamar yadda adam baiyi bacci ba shima,yanata juya yadda zai matsa sãahar din ta sallameshi salin alin,tun bata ritsa dashi ba.


      Wannan tunanin ya sanya washegari ya yayyaba mata maganganun da suka qona mata rai yasa kuma akayi mata allurar maaye da kyau waiko zata magantu,wannan yasa ta zabure,ta dinga fashe fashe tare da surutai a dakin saboda qarfin allurar,hakan kuma sai yayi dai dai da zuwansu afifa. Abun ya yiwa adam dadi ganin tashin hankulan dake kan fuskarsu tare da sake yarda da cewa eh lallai sãahar din ta haukace,wani irin mawuyacin yini sukayi a gidan, qwayar shinkafa babu wanda ya kaiwa cikinsa sai zallar ruwa. Sãahar na kwance daga bakin qofar dakin inda allurar ta bugar da ita daga qarshe tana jin muryoyinsu jifa jifa,wannan yasa ta yita motsa bakinta tana magana dasu,amma babu me jinta kasancewar sautin baya fita,taji muyar maama dinta na addu'ar Allah ya yaye mata ya bata lafiya yafi sau shurin masaki, furucin dake qonawa gami da soya mata zuciya,ya tabbata dai da gaske adam yaci galaba a kanta,ya kumma manna mata haukan dai,sannan ya sauya mata suna zuwa MAHAUKACIYA, sunzo sun taddata tana attitude na mahaukata tuburan.


*_W A S H E G A R I_*


       *_waiwaye_*


"Ina sonki.....kuma banajin zan daina sonki,saidai kin shiga hurumin daba naki ba,kin shigar gonar daba taki ba,kin tsallake iyakarki,kuma a yanzu nafi buqatar wadan nan abubuwan fiye dake,ki daukominsu ki damqamin,ke kuma na barki kici gaba da rayuwarki cikin salama" kai take girgizawa tana hawaye,wani irin mamakinsa tana jin kamar zai kasheta, kowacce rana da zata bullo zuwa faduwarta cikin shakka da kokwanto take,anya wannan din ADAM NE?,anya adam dinta ne?,anya musanyensa akayi mata ba?,ko kuma wata rundunar mugayen shaidanun aljanu ta shige jikinsa ne ta samu mafaka?,don abinda yakeyi a yanzun da ainihin wannan suffar tasa ta yanzu.......bata taba ganinta a tattare da adam dinta ba,koda kuwa cikin mafarkan bacci bare a kai ga rayuwa ta zahiri,adam din da ko quda baya qaunar ya sauka a kanta?,adam din dake kuka da idanunsa idan bata da lafiya?,adam din da yake kasa bacci saboda ta shiga damuwa?,adam din da yake kasa sukuni idan tana da buqata har sai ya adar mata?,dole ta shiga shakka.....amma kuma kullum yana qara tabbatar mata da cewa shi dinne fa,bawai kama ko musaye bane,to me yake faruwa?.


"Bazan taba baka ba.....burinka bazai taba cika ba,saidai na rasa rayuwata,kayi duk abinda kaga dama" ta fada tana jin bacin rai yana taso mata,tare da wani irin qwarin gwiwar tunkarar duk nau'in kalar azaba tuggu da makircin daya shirya mata.


      Wani murmushi ya kuma saki yana dubanta,da wani irin kallo na qasa qasa mai cike da tarin mugunta


"Ke kike jawa kanki koma meye,tunda ke muguwa ce ba zaki iya sallamamin abinda kikafi qarfinsa ba tako ina,to nima bazan sassauta miki ba har sai sanda kika gasu,kikaji cewa zaki iya sallamawa" daga haka ya miqe,ya fara fidda kayan jikinsa yana zubarwa a wajen.


      Idanu ta bude da kyau cikin tsananin tashin hankali tana dubansa,kada dai ace haqqinsa na aure yake shirin karba kamar yadda ya saba?,zallar rashin imanin da yake gwada mata bai sanya ya daga mata qafa ba,yakance 


"Har yanzu fa a sunan matata kike,ban saki igiyar ba,wannan abun dake faruwa wani issue ne na daban daya shafi interest dina da kuma naki". A duk lokaci irin wannan idan ya rabeta tana jin inama zata bude idanu taganta kwance cikin ramin qabarinta?,banda addininmu ya haramta kisan kai,naka ko na Wani,tabbas da tuni ta tsufa da kai kanta kiyama.


      Da gaske so yake ya kusanceta alhalin yasan cewa cikin jinin al'ada take,rashin imanin nasa qara gaba yake,dole tace rundunar shaidanun aljanu ne suka shigeshi,don lamarinsa yafi qarfin shaidani guda daya. 


    Kansa tsaye ya nufota gadan gadan,kamar ba adam din nan da abaya a lokutta irin wanann yake sanyata taji babu ya ita cikin 'ya'ya mata ba,ya sanyata taji duk duniya babu macen da tayi sa'ar abokin rayuwa irinta ba,a yanzu ya koma mata wani tsohon annamimin ifritu mashayin jinin bil'adama da ko motsinsa bataso ji bare ya rabeta,bashi da maraba da qaton shaidani a idanuwanta.


     Ringing din wayarsa ya dakatar dashi daga sake tunkarota,sai ya koma cikin aljihun wandonsa da ya yasar yana lalubar wayar. Cikin hanzari ya karata a kunnensa,sai kuma yace


"Ok,yanzu yanzu?,tom" ya latse wayar da sauri ya maidata,sannan ya soma mayar da kayan jikin nasa tana daga zaune tana kallonsa.


     Ga mamakinta sai taga yana bi yana balle button na rigarsa yana watsarwa,ya kama gaban rigar da qarfin tsiya ya ciccisge,sannan ya tsugunna ya jawo plate din tangaran din dake ajjiye gefe wanda ya kawo mata abincin da bata budawa bare ta taba,ya dagashi har abincin ya tamfatsa shi da qasa ya tarwatse,ya dauki wani yanki daga ciki ya yanki jikinsa ya kuma shashshafe maiqon a jikinsa.


      Sake miqewa yayi ya fara fatali da kayan dake saman madubi da duk wani abu na glass dake dakin yana cewa da matuqar daukaka murya


"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,ki tsaya......ki tsaya don Allah,ya salam,karki jiwa kanki ciwo, Hasbunallahu wa ni'imal wakeel,ya hayyu ya qayyumu ya baki lafiya" yana fada hawaye na sauka a idanunsa,yana kuma ci gaba da tarwatsa dakin tare da sake hargitsashi,bayan tsaiwa da tayi tayi masa gyara na nutsuwa,waiko hakan zai sanya wani daga cikin ahalin nata su ankara da cewa akwai hankali tattare da ita.


      Sanqamewa tayi a zaune,tunaninta ya dinke cifff kan meye manufar adam na aikata haka?,saidai koma meye tasan halinsa,ungulu ne baya jewar banza,ba shakka akwai abinda yake shirin sake qullawa. Kafin takai ga lalubo abinda ke shirin faruwa sai ta tsinci muryoyin mutanen da a kullum take addu'ar isowarsu gareta,qila akwai wani haske da zai risketa,ya kuma zama silar fitarta daga duhu zuwa haske.


     Da mugun qarfi ta yunqura zata dira daga gadon,yayi caraf ya tsallako ya damqeta ya cukuikuyeta da kyau yana sake yamutsa rigata da yamutsatsen gashinta. 


      Ya mata mugun riqon da bazata iya qwacewa ba,saboda banbancin qarfi da kuma qarancin garkuwa jiki dake tare da ita,don haka ta bude baki da zummar kiran daya daga ciki


"Koda kin kirasun ma sun shigo sunanki bazai canza ba a idanunsu,sunanki mahaukaciya har yau har gobe,sai ranar da kika fanshi kanki,ni kuma zan wankeki a idon duniya" daga haka yaci gaba da qaraji da ambaton sunan Allah yana mata kyakkyawan riqo,ita kuma taci gaba da yunqurin qwacewa hawaye na gudu bisa fuskarta, kokawa ta barke a tsakaninsu duk da cewa ba wata nasara a hakan sai azabar riqon da yayi mata da takesha,dai dai sanda aka turo qofar da sauri aka shigo,ya saki wani lafiyayyen murmushi daga can qasan zuciyarsa,burinsa ya cika,plan dinsa ya tafi a dai dai,dama abinda yakeso kenan,shigen abinda ya faru jiya,yau ma sun sake samunta a mahaukaciyarta.

[02/09, 3:47 pm] +234 810 324 4136: Page 50

_TABARMAR ?ASHI_*??


Page 52


    Afifa ce wadda ta kasa jurewa ci gaba da jin muryar sãahar din cikin wannan birkitaccen yanayin,da sassarfa ta nufo sãahar dake riqe a hannun adam da yayi wata irin wajiga,yayi hajaran majaran


"Karki ce zaki tabata, qoqari nake a yanzun ma kada ta yiwa kanta illa,don ko kanta bata ganewa bare wani"


"Komai girman haukan da bestie takeyi jikina ya bani ba zata taba illatani ba,saketa" afifa ta fada da wani irin zafin zuciya. Tashi zuciyar shima tazo wuya,amma dole ya sakar mata sãahar din saboda su maama dake a tsaye daga bakin qofa,can qasan ransa kuwa yana sake cika maqil da afifa din,baya qaunar mu'amalarta sam sam da sãahar,saboda ita din sãahar ba mai damuwa ko maida hankali akan abubuwa bace,tana da mugun kawaici da kuma sanyi akan abubuwa,duk da zazzafa ce ta fannin miskulanci da kima qin daukan raini wulaqanci ko qanqanci daga gurin kowa.


     Talau haka tayi a jikin afifa,maama ta taimaka mata suka kwantar da ita saman gadon,tanata buda baki da zummar yi musu magana,saidai kalma ko daya ta kasa fita daga bakinta,don allurar da aka shimfida mata ta fara aiki a jikinta.


     Shurun dakin ya dauka saboda bacci daya kwashe sãahar,afifa ta dauke dubanta daga fuskar sãahar tana jan majina saboda kukan da tasha,ta maida dubanta ga adam dake tsaye jikin qofa,gaba daya fuskarsa babu komai kwance a samanta face zallar tashin hankali


"Zan samu qur'ani?" Ta tambayi adam din,sai ya daga kai da sauri


"Eh,akwai,amma karki ce zakiyi karatu ne,an samu ta samu bacci ba kuma wani matsalan ya biyo baya" kai ta girgiza tana kafeshi da ido


"Ba inda karanta qur'ani yake zama matsala,saidai waraka,ka daukomin" ta fada tana miqewa zuwa toilet din sãahar din don ta daura alwala.


    Tayi alwalar tana fitowa ta taka wani abu,sai ta tsaya taja baya da sauri tana furta


"Subhanallah" ganin kwalba ce,ta sunkuya ta dauketa ta cillata a dust bin din,ta shimfida abun salla kusa da maama wadda ke zaune tun dazun,riqe da hannun sãahar,ta zuba mata ido tana mata wani irin kallon qurilla,cike da zallar tausayinta,time to time tana tofa mata addu'o'in da taketa karantawa.


       Sanda ta idar da sallar saita dauki qur'anin da adam ya kawo ya ajjiye ya fita,ta zauna dai dai saman kan sãahar din ta bude ta fara karantawa. Sai data shafe awanni uku cur sannan ta miqe ta sauka daga gadon,ta ajjiye qur'anin,ta sake juyawa da nufin komawa bandakin don tayi fitsari.


      Kamar gilmawar walqiya hasken kwalbar data yar dazu ya gifta mata,saita tsaya ta koma da baya,ta tsaya gaban sharar tana duban kwalbar wadda takewa kallon sani.


      Duqawa tayi ta sanya hannu ta cirota kusa da syringe din dake nuna dashi aka zuqe ruwan aka zubawa duk wanda aka sakawan ma,ta soma bin rubutun jiki tana son tantance allurar data sani din ce?. Wani irin dimuwa firgici da kuma tashin hankali ne suka shigeta farat daya,ta waro idanunta kamar zasu fado qasa,saita juya da sauri fa koma saman gadon. Gaba daya jikinta rawa yakeyi,zuciyarta na ayyana mata abubuwa kala daban daban,babban burinta a yanzu sãahar din ta farka,akwai abubuwa da alama masu tarin yawa,akwai wasu abubuwa a lullube a kima binne babu ko shakkaMaimakon karatun da taso yi,saita kasa aiwatar da komai,ta koma ta zauna saman gadon tana riqe da hannun sãahar gam kamar wadda zata bacewa ganinta,kwanyarta nason hakaito mata abinda yake faruwa da sãahar amma gaba daya tunaninta yaqi aminta da hakan. Ta jima a cikin wannan yanayin kafin taji an budo qofa. Maama ce tare da Dr mamman,dukkansu suka tsuguna a gaban gadon sãahar din,kowanne fuskarsa a narke zuciyarsu cike da rauni.


      Addu'a yayi mata kamar ko yaushe,sannan yace su shirya su wuce gida,duk da ya gama karantarta sam batason tafiya gidan


"A nan yau zan kwana" afifa ta fada kanta tsaye,saboda zuciya da gangar jikinta suna bata abubuwa da dama da takeson tabbatar dasu,akwai qaqqarfan zargin daya shiga zuciyarta


"Anya?,zaki iya?" Dr mamman girema ya fada yana kallon afifan,kafin ta bada amsa adam da yake shigowa yayi caraf da zancan cikin tashin hankalin daya bugi qirjinsa na jin cewa zata kwana da sãahar


"Gaskiya abba banajin zata iya,zan iya ci gaba da kwana da ita kafin randa zamu wuce asibitin,babu abinda ta rasa,zan kuma ci gaba da kulawa,ba zata rasa komai din ba in sha Allah har zuwa lokacin da Allah zai bata lafiya"


"Kana qoqari kam,mun shaida mun kuma yaba sosai,a qalla yau kaima ka kwanta kayi bacci sosai yadda ya kamata, saboda haka yau ni zan kwana da bestie in sha Allah,don na tabbatar koda nice irin hakan ta sameni,ba zata gujeni ba koda na kwana daya ne" ta fada tana sakin qwalla,don tanason karya zuciyar dr mamman ya qyaleta ta kwanan. Ta samu nasara kuwa,don dukkansu qas sukayi da kansu,yayin da maama ke share hawaye


"Gaskiya ne,kaima ya kamata ka huta koda iya yaune, ubangiji yayi maka albarka bisa qoqarinka"


"Ameem ya Allah abba" ga fada kansa a qasa yana murza yatsunsa,zuciyarsa na wani irin bugawa da zallar tashin hankali tare da tunanin mafita,don ba shakka zuwa nan da awa daya zuwa biyu sãahar din zata iya farkawa,farkawarta kuma dai dai yake da tonuwar asirinsa da tashin ballin dukkan wani rufaffen asirinsa.


     Har motarsu dr mamman ta tashi yana tsaye kamar wanda aka kafa a wajen,daga qarshe dabara ta fado masa,ya fada motarsa kai tsaye yabi bayansu ya wuce gurin likitansa. Allurar da ake mata me sanya nannauyan bacci har fiye da wadda aka saba yi mata,da kuma wadda ke sanya birkicewar kwanya ya karbo,dukkansu yasa aka sauya musu gida,tunda yasan me afifan ta karanta,harkar kafiya ne,a yanzun tana cikin matasan likitoci masu qarancin shekaru da jahar kano ke dasu,yanason yayi wasa ds hankalinta,ta kuma yiwa 'yar uwar tata da take mutuwar so take aibatashi sabods ita allurar da zata sake mata illa tako ina.


      Tana zaune tana karanta qur'anin ya tura qofar,ta daga kai a hankali ta qare masa nutsatsen kallo amma a fakaice,sai a yanzun ta lura da wasu abubuwa a tattare dashi,cikin son nuna kulawa ya qaraso ya ajjiye ledar hannunsa,sannan ya matsa gaban gadon ya shafi wuyan sãahar din dake baccin mutuwa,ganin bata motsa ba ya tabbatar akwai ssuran lokuta kafin allurar ta saketa


"Alhamdulillah,Allah ya qara lafiya" ya fadi da sigar dake nuna damuwa da kuma kulawa. Waiwayawa yayi ya kalli afifa


"Ina ganin kije kici abinci sai ki buda daya dakin ki kwanta ko?" Qaramin murmushi ta sake


"Banda abinka mr Adam,ai ba hutawa nazo yi ba,jinya nazo yi,yau kaine da baccin nan,kada ka damu" tsaki yaja cikin ransa yana tsinewa afifan,yassn tunda har ra dawo dole ne aikinsa a yanzu ya hadu da qalubale masu yawa,amma idan tasan wata ai batasan wata ba,zaiji da ita


"To yayi,yanzu ga alluranta nan,za'a yi mata su kafin ta farka,hakan yana taimakawa wajen farkawarta ba tare da buge buge ko surutai ba"


"Okay" ta furta tana ajjiye qur'anin,ta buda ledar tana fiddo ruwan alluran hade da syringe din.


      Duban farko ta yiwa alluran tasan cewa ba ainihin mazubinsu suke ba,abu na biyu kenan daya qara qarfafa zarginta,ta fitar dasu kaf ta zuqe ruwan allurar a syringe,ta matso ta dora tsinin allurar saman hannun sãahar da batasan abinda akeyi ba.

[02/09, 3:47 pm] +234 810 324 4136: Page 53

No comments