Breaking News

Tabarmar Kashi Book 1 Page 23-24

 


Page 23



           Ya motsa bakinsa a hankali yana maimaita sunan,me yasa yake yawaita maimaita mafarkinsu?,ameesha tuntuntuni ya gama rufe babinta a rayuwarsa.....maji fa?,yasan babu ta yadda zai iya cire jininta daga jikinsa,amma yawaita mafarkin nata a yanayin da yasan a zahiri ba haka rayuwarta take ba shine abu mafi daure kai a wajensa.


             Har sai da yaji idanunsa suna dan masa yaji yaji sannan ya kulle famfon,ya jawo towel ya goge fuskarsa data qara wani haske,ya fito a hankali daga toilet din zuwa bedroom dinsa,baccin da bai samu ya koma ba kenan,daga qarshe ya matsa ya koma saman sallayarsa ya sake kabbara sallah.....boyayyar rayuwarsa kenan da ba kowa bane yasan hakan.


           Washegari da wani irin weakness ya tashi,babu karsashin nan da kuzarin da ya saba wayar gari dashi duk safiya,saidai makara da yayi bai fito lokacin daya saba fitowar ba,don a sanda ya fito din tuni fadeela ta wuce makaranta.


            Cook dinsa yana tsaye yana serving dinsa,yayin da shi kuma yake danne danne a wayarsa,sallamar hajiya qarama ta karade falon,sanye take da wani lace na alfarma,wanda ke nuni da zallar tsadar da yake dashi,a kallon farko zaka karanci mutum ce me izza tare da son komai na alfarma da kerewa sa'a,don a iya takun tafiyarta ma kawai ya nuna haka.


             Kujera daya taja ta zauna cikin kujeru shiddan dake zagaye da mulmulallen dining table din me wani irin siffa da tsari,a gurguje Noah cook din nasa ya kammala zuba komai bayan ya zube a qasa ya gaidata,ya sauka da sassarfa yana barin parlor din zuwa kitchen don ya tsaftaceshi hadi da kammale komai kamar yadda ya saba a duk sanda ya kammala girkawa uban gidan nasa abinci,daya daga cikin dokokinsa daya kafa masa akan tsafta ne,baya qaunarta sam sam,sai kuma akayi sa'a shima Noah din gwanin tsafta ne dama.


"Kunyi waya da maji kuwa a kwanan nan?" Ta tambayeshi da kulawa,kamar ya dago kansa ya kalleta saboda ambatar sunan da tayi,wanda hakan ya tuna masa da mafarkinta da yayi a daren jiya,sai kuma yaci gaba da diban chips da yakeyi a fork


"Bamuyi ba,bata kirani ba"  boyayyar ajiyar zuciya ta sauke,duk da hakan batajin nutsuwa a tattare da ita,shurun maji ta tabbatar bawai yana nufin tabar mata toufeeq bane,hakanan a duk sanda shurunta ya tashi maido da amsa......yana magana ne cikin amo da amsa kuwwa me qarfi,irin qarfin da ita kanta takejin sautin saman jiki da zuciyarta. Ta sani,ba sanin jiya ko yau ba......itadin jarumar macace,wadda bata yarda da faduwa saarewa ko gajiyawa ba,wannan dalilin ne ya sanya har yanzu burinkan mommy qarama ya gaza kaiwa ga gaci,duk da ta cimma nasara da galaba masu yawa a kanta


"Ka qoqarta kayi kiranta" kai kawai ya gyada mata,shuru ya sake ratsa tsakani,tana mamakin yadda har yau bai iya doguwar hira da ita ba,duk da tana data cewa da yawa cikin al'amuran rayuwarsa


"Nace ba" ta sake fada tana fifita masa tea din don ta saisaita zafinsa,qwayoyin idanunsa kawai ya daga ya kalleta ba tare da yace komai ba har zuwa sanda ya janyesu. Janyesun da yayi ne ya qara mata qwarin gwiwa,idanunsa na dabanne,haka kallon dake cikinsu,suna da kwarjini wanda har yau idan ya dubeta tana jin hakan sosai yana tabata


"Yaruwarka HASEENA,nace kuna gaisawa kuwa?" Sosai tambayar tata ta bashi mamaki,ita kanta daya kalleta sai taga tambayar kamar bata hau dai dai ba,tunda tasan kome yake akwai tsakaninsu


"Bani da lokacin biyewa shirmenta" ya amsa a taqaice. Yanason ya bawa hajiya qaraman haske amma kuma shi din bame sanin yadda zaiyi magana me tsaho bane,a ko yaushe yakanyi magana ne a dunqule,indai bamai matuqar muhimmanci ba,shine zai zauna bayani.


          Murmushi hajiya qarama ta saki tana tura masa cup din tea din


"Me kakeso na gayawa daddynka?" Ta sake jefa masa tambayar tana dubansa. Bai amsa ba har sai daya kusa cinye abinda ke bakinsa sannan ya miqe alamun ya gama kenan


"Ya kamata ya fahimceni don Allah" shine amsar daya bata,saiya ciri tissue guda daya ya soma sauka,da kallo ta bishi,sannan daga bisani tace


"A dawo lafiya,Allah ya tsare" taci gaba da kallonsa har ya fita daga dining room din. Dubanta ta dawo dashi inda ya tashin,ta jijjiga kai,sai kuma murmushi ya kubce mata,tadan daki table din kadan sannan itama ta miqe ta fice a nutse cikin qasaitaccen takunta.



***********Kamar kowanne lokaci,yau yadan saba lokacin dawowarsa,don bai shigo gidan ba sai bayan sallar magariba,bayan sun tsaya sunyi sallah a masallacin dake gine daga farkon layinsu.


            A kullum itace mutum ta farko da yake fara nema idan ya shigo gidan,yau dinma hakanne,sassansu ya wuce kai tsaye,ya samu baaba ramatu tana gyara kayan ruwa lemo da ice cream kala kala da yake zubewa fadeela a fridge din.


"Barka da dawowa yallabai" tafada cikin mutuntawa,cikin girmamawa shima ya amsa mata,tun kafin ya tambaya kuma ta amsa masa


"Tana ciki ita da hajiya qarama" ta nuna hanyar da zata sadashi da bedrooms dinsu,baice komai ba yaci gaba da takawa da 'yar sasaarfa zuwa dakin,yanajin yadda gajiya takebin gabbansa.


           A nutse tare kuma da sallama ya tura qofar dakin,hajiya qarama na tsaye goye da hannayenta,fadeela da sabuwar nannynta na daga bakin toilet,nannyn tana tsane mata jiki da towel. 


         Sallamarsa kadai ta zaburar da ita,ta watsar da towel din ta tako da gudu,sai ya durqusa mata kamar yadda ya saba,ya bude mata hannayensa ta shige tana fadin


"Oyoyo" murmushi hajiya qarama ta saki


"Shikenan,mun huta da complain din daddy yayi late" siririn murmushin da ba kasafai ake ganinsa akan fuskarsa ba ya saki,wani irin sirrintaccen kyansa ya bayyana


"An dawo lafiya?,ina nan ina sake nunawa nannynta yadda zata dinga kula da abubuwa,bana fatan a sake samun matsala daga kanta" hajiya qarama ta fada,sai ya jinjina kai,yana maida hankalinsa ga fadeela data dauko wani kwali ta miqo masa


"Mommy qarama ce ta bani,kai nake jira ka dawo ka hadamin" karban kwalin yayi hannu bibbiyu


"I hope kince mata kin gode?" Kai ta gyada cike da zumudi


"Good,me zai hana ki bawa mommy ta qarasa ladanta?" Kafada ta noqe,kafin tace komai ma mommyn ta daga hannunta sama


"Inaaa,wannan kuma aikinku ne,nidai na gama nawa tunda na cika alqawari" ta fadi tana dariya gami da nufan qofa


"Allah ya bamu alkhairi tunda tsohonki ya dawo ai kuma shikenan" ta fadi tana ficewa daga dakin.


             Duk yadda yaso fa barshi yaje yayi wanka yaci abinci sannan a hada qin yarda tayi,abu daya ta bari akayi,ta kira nanny din nata,tazo ta saka mata kaya,tana riqe da kwalin suka fito zuwa sassansa.


           Ta harabar gidan suka sake fitowa maimakon yayi Linkin ya bulla ta sassan nasu,tana gaba yana biye da ita,dai dai sanda qaramar motar da aka gama parking dinta yanzu ke budewa.


            Labiba ce ke fitowa,sanye da wani skinny jeans da shirt mai gajeran hannu, high heels ne a qafarta me azabar tsini kamar idan ka takashi da kyau zai iya karyewa,yalolon mayafi ne saman wanda baida maraba da mayafin yaran da shekarunsu ba zasu zarta tsakanin uku hudu zuwa biyar ba


"Hi fadeela" abinda ta fada kenan,idanunta a kansa tana jin wani qunci a ranta,duba daya yayi mata,kallon da bata tunanin ya b'ata second uku yana yi mata shi,ya dauke kansa kamar yaga wani abun qyama


"Hi" yarinyar ta maida mata,sannan ta taka da hanzari tabi bayan babanta da yayi gaba tuni tana kiran ya jirata. Tsaye tayi a wajen har suka bace mata,sai a sanann ta samu qwatar kallonta daga kansu,taja wani dogon tsaki


"Yarinyar sai shegen rashin saurin yarda da sabo fal cikinta,ta kwashe halin tsohonta tsaf" tayi maganar cikin salon mita tana maida murfin motar ta rufe,sannan ta saka mata key tana takawa cikin gidan,zuwa yanzu ta fara tuqewa,zuciyarta ta fara gazawa daga yadda ganinsa yake neman fara yi mata wuya,ta jigata sosai da yadda a yanzun ya sake daure mata fiye da baya. A baya koda zai watsar da ita,koda bazai kulata ba,koda bazai kalleta ba amma bazai kyaret ba,bai kuma taba shata mata layin zama inda yake ba,saidai yayi kamar baisan da ita a wajen ba,ita kuma ko babu komai iya hakan ma tasan wata alfarma ce ta samu,wadda dubban matan dake yawo,suke kamar zasu mutu a kanshi basu samu hakan ba,ko babu komai tana samun daman zama ta kalleshi iya son ranta.


          Sai daya tsaya ya hada mata komai,ta sake tubure masa sai daya zauna suka fara yi tare sannan ta barshi ya shiga ciki,wanka ya fara yi,ya dawo ya shirya cikin gajerun pajamas.


           Yana tsaka da taje kansa wayarsa ta dauki tsuwwa. A nutse ya jawo wayar yana duba me kiran,MAJI shine ya bayyana saman screen din,sai ya ajjiye comb din hannun nasa,ya jawo stool ya zauna akai yana daga kiran.


          Sassanyar muryar dattijuwar,dake cike da wani irin amo dake nuna zallar sanyinta koda a yanayi na halitta ma,tayi cikakkiyar sallamar data saka zuciyarsa dokawa,ya lumshe idanunsa yana amsa sallamar tata,tare da qoqarin tuno watannin da ya shafe ba tare daya kirata din ba


"Ka manta dani ko moha?" Ta kirayeshi da sunan da ita kadai ke kiransa dashi,kuma koda a wani guri yaji wannan sautin ya tabbatar ita dince,ko kuma wani dake da alaqa da ita.


          Cikin tsananin jin kunya da nauyinta ya motsa labbansa


"Kiyi haquri" ya fada a sanyaye,qaramin murmushi ta saki,ta saba da jin wannan kalmar ta ban haquri daga bakinsa,har batasan iya adadi ba,bada haqurin da kuma ba wai yana nufin ya daina bane,wani abu ne da yake faruwa tsahon shekaru masu yawa,wanda batasan ranar yankewarsa ba,duk da cewa idan har ta bugi qirji ta kuma daga hannuwanta da sunan samun nasara ba shakka batayi laifi ba.


        Cikin wani irin rashin sakewa da kuma rashin sabon da baisan daga ina yake taso masa ba a duk inda suke waya ya fara gaisheta,saidai kuma cike da girmamawa ne


"Ina fatan komai yana lafiya?"


"Alhamdulillah"


"Ma sha Allah,kada kayi wasa da addu'a a dukka wani gaba ta rayuwarka,komai yana da lokaci,kuma nan kusa nake fatan samun wani haske da fatahi daga rayuwarmu gaba daya,ina jikata?" Ta tambayi fadeela cike da shauqin son jin muryarta,wata irin qauna me gauraye da tausayi takewa yarinyar. 'Yar halak din kamar tasan ita ake nema kuwa,sai gata ta buda qofar dakin riqe da games dinta tazo kawo qorafi. Kai tsaye ya miqa mata wayar


"Maji ce" ya fada qasa qasa,saita ajjiye kayan hannun nata duka a qasa,ta tako da sassarfa ta karbi wayar.


        Gefe ya koma ya harde hannayensa yana kallon yadda suke waya da maji,kamar sun san juna sosai da sosai,duk da batasan maji ba,amma akwai wanda wani irin sabo tsakaninsu qwarai da gaske,tasan maji a baki kamar me. Lokaci kadan tama manta da daddyn nata dake tsaye,hira suke abinsu,kamar ba daga wata qasa maji din ke kira ba,bata jin katinta sam da take yawan qonawa akan fadeela.


FURAR DANKO

Billyn Abdul


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay at??


1487616276 

Access Bank

Bilkisa Ibrahim

Sai katura shedar biyanka anan??


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan??

09033181070


VIP????

Zafin kai 3k

Furar danko 3k

Tabarmar kashi 3k

Bakon munafuki 3k


*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*


+22799643131


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*??


Zafafa????

[17/08, 5:30 pm] +234 907 013 9442: *H U G U M A*


*_TABARMAR ?ASHI_*??

https://arewabooks.com/u/huguma


Page 24



           Lokaci kadan tama manta da daddyn nata dake tsaye,hira suke abinsu,kamar ba daga wata qasa maji din ke kira ba,bata jin katinta sam da take yawan qonawa akan fadeela.


           Sun jima kafin daga bisani suyi sallama,ta kawo masa wayar,fuskarta qunshe da murmushi


"Daddy,wai a ina maji take?" Ta jefa masa tambayar da baiyi zaton jinta daga bakinta ba


"Bata a nan qasar angel"


"Tana ina?" Ta sake tambayarsa,da alamar da gaske tanason jin a inda take din


"Algeria"


"Yaushe zamuje daddy?,tanason ta ganni nima inason na ganta" ta tambayeshi a shagwabe. Ido ya zuba mata sosai,shi kansa a yanzu bazai iya kai kasa kai tsaye inda maji take ba,tun haihuwarsa har girmansa bai taba zuwa,a baya yana da kwadayin zuwan,amma a yanzun kwata kwata babu wannan cikin ransa,baisan kuma yaushe hakan ta faru ba,kawai dai ya tashi ne dare daya yaji yayi loosing interest akan dukkan abinda ya shafeta,kafin daga bisani kuma ya yakan yawaita samun mantuwa akan komai daga danganceta.


"Zamuje angel"


"Daddy yaushe?" Ta sake tambayarsa tana kafeshi da idanu,idanunsa ya janye daga kanta,murmushi kadan yana subuce masa,ya fuskanci rigima takeji


"Wata rana" ya bata amsa yana sanya hannuwansa ya dauketa cak hadi da cewa


"Muje muci dinner" zata sake magana ya dora yatsansa akan lips dinsa gami da cewa


"Shshshsh,ya isa" duk da qanqantarta amma tana gudun abinda zai bata masa rai,tana matuqar jin maganarsa fiye da tunani,saita kwantar da kanta a kafadarsa,a haka suka qarasa dining room din.


         Sallamar cook din nasa dake jiran ya iso yayi serving nashi yayi,da kansa ya zuba musu iya abinda zasu iya ci shi da fadeelan yabar sauran.


*********Karfe daya na rana ne,lokacin da kowanne ma'aikaci dake qarqashin company din yake morewa lokuttansa na break. Dai dai lokacin da sãahar a cikin nata office din ta duqufa wajen ganin ta gama hada dukka bayanan data samu daga financial team na company,tana duba yiwuwar yin magana akan document dinta dake office na CEO,batason tayi aikin banza,tanaso ta aiwatar da dukka tsare tsaren da tayi,don ta tabbatar zai kawo gagarumin ci gaba da kuma sauyi cikin company din.


          Buda qofar da akayi ya sakata daga fararen idanunta tana kallon bakin qofar,mr sameera ce,ta bata izinin qarasowa bayan ta janye hannuwanta daga kan system din


"Ranki ya dade,sir hamza ne ya sake dawowa" idanunta da suka dan daure saboda kallon allon system din tadan juya kadan,qaramin tsaki taja,hamzan yanason shiga rayuwarta,kaf fadin company din a yanzu bata da wata matsala saishi,yaqi fahimtar inda tasa gaba,gaba daya sake shige mata yakeyi a kowanne lokaci,don kawai office dinta yana da alaqa da department dinsa,don ko yanzu report din da take dubawa daga office dinsa ya fito,banda haka da tuni ta yanke dukkan wata alaqa da zaya bashi damar ganinta


"Ki gaya masa ba yanzu ba,aiki nakeyi,ya tura kowanne saqo ta email din office,zan duba sanda na zama available" jinjina kai sameera tayi,ta juya ta fice.


          Cak ta tsaya da aikin da takeyi tana sake jan wani dogon tsakin da yafi na farko,saita tura kujerarta baya tana dan fidda iska daga bakinta,da alama wani tunani ne ya darsu a ranta lokaci daya. Yatsunta tasa tana murza goshinta dasu,tana tuna shigowarta company a safiyar dazu,yadda ta tadda employee a dan hautsine,sakamakon korar wasu ma'aikatan guda uku da ceo yayi a safiyar


"wanne irin mutum ne shi?,me izza da dagawa?,he doesn't give excuse to anyone?,abu kadan kora?,kowa ma yana iya kora ko yayi masa fada?" Tayi maganar can qasan zuciyarta,haushinsa da kuma tsanarsa suna huda zuciyar tata,abinda ta lura dashi ma,gaba daya yafi zafafa al'amuransa akan mata. Sake jan wani dogon tsakin tayi karo na uku,gaba daya tuna abin da ya farun yasa tayo loosing interest akan aikin,ta duba baqin agogon dake daure a tsintsaye hannunta qirar kamfanin Casio,akwai ragowar mintuna talatin kafin lokacin komawa bakin aiki yayi,coffe take da buqata,amma batason takura mr sameera,don haka ta tsugunna a hankali ta daura igiyoyin baqon takalaminta daya mugun haska farar qafarta me dauke da dogayen yatsu,ta miqe a nutse ta dauki iya wayarta ta fita a office din.


         A nutse take takawa a farfajiyar gurin,cikin girmamawa ma'aikatan ke gaidata,saboda Suna respecting nata sosai,duk wanda yayi mu'alama da ita kuma kusan sai ya fadi halinta ya kuma yi mata shaida me kyau.


         Ko kusa ko alama bata ga koda inuwarsa ba,saijin maganarsa tayi a bayanta


"Ranki ya dade,barka sa fitowa" mr hamza kenan,wanda ke biye da takunta yana son ya cimmata cikin zumudin da katarin ganin fitowarta da yayi. Kadan ta waiwaya ta aje masa kallo daya


"Ya kake?" Ta fada a daqile,hamza na daya daga cikin mutanen dakeson zame mata barazana cikin company din,tare da yi mata kutse cikin walwalarta da al'amuranta,duk wani hanya da zatayi avoiding nasa tayi,amma ta karanci kamar baya fahimta,da alama yana sahun mazan dake da shegen naci da kafiya ne


"Lafiya amma ba qalau ba,please ki taimaka ki gayawa secretary dinki,ta daina min shamaki da ganinki,wallahi it really hurts me" sunzo bakin qofar kitchen din,kuma bata da buqatar yaci gaba da binta,don haka ta dakata,ta juyo gaba daya tana dubansa


"Excuse me mr hamza.....ko zaka taimaka ka juya,saboda banason ka shigarmin lokacin nawa hutun,na gaya maka idan maganar office ce ka tura ta email zan duba,idan kuma bata office bane, please i beg you,banason wani abu da bashi ya taramu a nan ba ya hadani da kai,bama kai ba,koma waye bana buqatar wata hulda ko alaqa" da hanzari ya buda baki zai maida mata da martani,amma sai taji yayi dif,batasan dalilin daukewar wutarsa haka lokaci guda ba,amma koma meye sanadi ita ba damuwarta bane,don dama tafi buqatar shirunsa akan amsarsa,don haka ta juya ta shige kitchen din kanta tsaye.


          Wayam din data gani a kitchen din babu kowa da kuma qarancin haskensa bai sanya ta zaci akwai wani abu ba,saboda wannan shine karon farko data taba shigowa kitchen din. Coffe dama kadai tazo nema,don haka ta nufi mini coffee maker din data gani a jone,data duba sai taga akwai saura a ciki,don haka ta ciri mug guda daya,ta cikashi dashi,yawunta yana tsinkewa,saboda wani qamshi da taji yanayi na musamman,uwa uba kuma kana kallonsa zakasan ya hadu iya kwadayinka da shan coffee.


        Dan qaramin murmushi ta sauke,saita gyata tsaiwarta tana kai mug din bakinta,dai dai sanda ta juyo. Babu zato ta saki mug din,cikin razana taja baya,fararen idanunta suna sake girma hadi da fitowa waje. Tsoratar da tayi yasa bata iya tsaiwa ta tantance waye ba tayi qofar waje da sassarfa,saidai kuma tana dab da isa ya rigata isa gurin,ya saka hannu ya tura qofar ya rufeta bam,taja birki a mugun hautsine tana sauke dubanta a kansa,sai a lokacinne ta gane waye.


             MT jarma ne da kansa,cikin shigar suit dinsa ta ko yaushe,saidai kuma a yau din babu suit jacket din a jikinsa,alamu suna nuna ya barota a office,hannun rigar ciki da ya kasance dogo ya tattareshi ya barshi iya gwiwar hannunsa,wannan ya bawa murdadden hannunsa dake cike da gargasa da wasu irin jijiyoyin da yawan shiga gym ya haifar dasu. Kwantacciyar sumarsa me santsi a dan hargitse take kadan,lips dinsa sundan sake yin jaa saboda zazzafan coffee din da yake sipping a hankali.


         Ko a yanzun ma da yake tsaye ci gaba yayi da sipping abinsa cikin nutsuwarsa da kamewarsa,kamar bashi ya tsorata ta ba,sanann yasa hannu ya garqame musu qofa haka kawai ana zaune qalau. Ranta ne taji yayi mummunan baci,tadan motsa fuskarta kadan saboda yadda zafin coffee din data saki ya dan taba qafarta yake mata zafi kadan kadan,wannan wacce irin dabi'a ce zai samu guri ya zauna a kitchen,a corner din da ba lallai kai ka iya ganinsa ba?,saita janye idanunta ta taka zuwa qofar don ta bude ta fice,don bata qaunar hada rufi daya dashi bare taci gaba da zuqar qamshin turarenta da yake neman sanyaya dukkan wani zafi data dauka akan abinda yayin. 


           Table din dake daura dashi ya matsa kadan ya dora cup din,cikin zuzzurfar muryarsa dake cakude da wani irin amo me ya soma magana


"You must learn saying salam a duk wajen da zaki shiga,saboda nan din mudai musulmai sunfi yawa......sannan bari na taimakeki na tuna miki wani abu daya,nan masana'anta ce,kayi aiki a biyaka da gwargwadon wahalarka na wata daya,ba waje bane da aka bude saboda soyayya ba,saboda haka ki kiyayi bawa wani damar ganinki a office da kebantacciyar buqatarku wadda bata da alaqa da company,idan ba haka ba,you will loose your job" ya qarasa maganar yana dora hannunsa a mariqin qofar,ya budeta sannan yace


"Dont try to do this again......inda kin fita a yadda kikaso fita,wani ya ganki me kike tunani zai zata" bai jira amsarta ba ya taka zai fita, zuciyarta tazo mata iya wuya sosai. Yama gama raina mata hankali,yaso qona mata qafafuwa,sannan kuma ya bita da wasu sharuddansa marasa amfani a gurinta,tunda dai ai ita ba yarinya bace,tasan meye ya dace da ita. Ji tayi idan ya fita ba tare datace masa komai ba tabbas yaci bulus,duk da zuicyarta na qoqarin tuna mata maganganun yaa Saifullahi da yaa zaid na ta girmamashi,gaba yake da ita


"Shi kuma wannan kullemu da kayi fa?,idan wanin ya gani yace me?" Ta fada tana jin takaicin yadda tayi dogon zama a guri daya dashi,harta shaqi turarensa da kyau,ya shiga kowacce kafa ta hanci da kwanyarta. 


          Waiwayowa yayi ya zube mata manyan kewayayyun idanun nasa dake da wani irin magnet da kwarjini,har sai dataji kamar zata zube,yayo taku biyu ya dawo baya kadan


"Kina iya gayawa duk wanda ya tambayeki..... nayi raping naki ne,don wanann din kadanne daga aikinku". 


"Ya salam" ta fada can qasan zuciyarta hade da wani mugun bugawa da zuciyar tata tayi,ba kuma tare data shirya ba ta koma da baya ta zauna saman kujerar dake kusa da ita,wanda tayi yaqinin banda taimakon Allah kujerar tana kusa da ita lallai zata iya faduwa qasa. Kamar baice komai ba ya juya a nutsensa ya fita a kitchen din.


FURAR DANKO

Billyn Abdul


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay at??


1487616276 

Access Bank

Bilkisa Ibrahim

Sai katura shedar biyanka anan??


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan??

09033181070


VIP????

Zafin kai 3k

Furar danko 3k

Tabarmar kashi 3k

Bakon munafuki 3k


*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*


+22799643131


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*??


Zafafa????

[17/08, 5:30 pm] +234 907 013 9442: *H U G U M A*


*_TABARMAR ?ASHI_*??

https://arewabooks.com/u/huguma


No comments