Breaking News

Kyalkyalin Kauna 43

 43

https://www.instagram.com/p/CtvvsTiI0Px/?igshid=YjgzMjc4YjcwZQ==





Yamata rumfa wani kalan kankame idanunta tayi tana numfashi da sauri da sauri gabanta na faduwa dum dum dum kaman zai fashe ganin Pablo gabanta, ahankali ya lumshe idanunshi yanajin yanda numfashinta ke sauka akan kirjinshi yana karajin mugun shaukin dayakeji aranshi gently yabude idanunshi yadaurasu akan fuskanta yanabin dogayen eye lash nata da kallo, zuwa kan pink lips dinta da har yanzu janbaki kadan ke kansu dayasa takara wani kyau kaman ba itaba lokacin nan da akai kidnapping nata,  murya chan kasa dakeda dan kauri yace “open your eyes and look up” dudda yanda kirjinta ke bugawa kasa musu tayi kaman yamata magani tabude idanun ahankali tareda dago su tazubamai su sai kyalli suke sunyi tartar kaman an wankesu da ruwan alam. Tsarki ya tabbata ga Allah ubangijin daya hallici yarinyar nan sannan ya hallici wayan nan idanuwan nata saura kadan Maheer ya shide yadai daure ya tsaya yana kallonta kaman yanda take kallonshi gabanta na faduwa sosai batare daya nuna mata yanda yakeji ba, da hannunshi yadaki gefen bangon datake jingine saida ta firgita cikin tsananin fushi danshi kanshi he’s angry with yanda yakeji akanta azafaffe yace “what have you done to me”? Kaman ta kurma ihu takeji but sabida tasan akwai dalibai awaje yasa ta rike bakinta tareda lumshe idanu da sauri, adan zafafe Maheer yace “nace ki kalleni” bude idanuwan tayi dasauri ta maidasu kanshi sun cika da kwalla sosai dake gab da zubowa, babu wasa akan fuskanshi yace “wani spell kikai casting akaina? Tell me!” Yadanyi ihu kadan still ba irin wanda za’ajisu a school ba, rawa bakinta yafara tama kasa magana kawai gabanta is hopelessly beating, fizge hannunta Maheer yayi yarike gam yakai kan kirjinshi dashima ke bugawa binbimbin yace “listen to my heart beat from the day dana fara ganinki beating dinshi ya chanza to this, koda yaushe tunanin ki nake, when am awake, when am asleep, nabude ido na ganki, na rufe ido na ganki, you are in my head, my body, my eyes, my thoughts, my eyes, my everything, look at me, look at what I’ve subjected myself into ni koyarwa in this I donno cottage school din naku all because of you tell me wani black magic kikamin hooon!” yasake dukan bango dayasa tafashe da kuka tana girgizamai kai tama rasa mezatayi tadaura hannunta akan baki sabida kar karan kukanta yafito tsayawa she’s just so scared, wannan mutumin yabiyota school yana cewa metamai, to metamai? Kuri Maheer yayi yana kallonta da tsoronta da kukanta da yanda yake goge hawayen da bayan hannu everything about her na burgeshi ji yake kaman he should hug her and tell her sorry, ahankali yasauke ijiyan zuciya yana kallonta still batare daya dauke idanunshi daga kanta ba yace “i want you to become my wife!!!” Dum dum dum haka gaban Yasmeen yafadi shi karan kanshi Maheer din mamakin abinda yafito daga bakinshi yayi dan wlh wlh baisan ya akayi abin yafito ba, sakin hannunta yayi da sauri yawuce yazauna kan table yay crossing kafanshi daya kan daya yana kallonta yanda take kallonshi tana kuka tana goge hawayen da bayan hannu kaman tana kokarin kara gasgasata abinda yafadi, yakai kusan 5min yana kallonta yana tunanin abinda yace sannan ahankali yace “remember you are indebted to me dan haka…” yamike tsaye yawuce chan gaban tv office din ya tsaya tareda kulle hannunshi tabayanshi yana kallon tv yajuya mata baya awani irin hankali yace “Fateema Ibrahim Ibrahim!” Faduwan da gaban Yasmeen yayi this time around saida ta daura duka hannayenta kan kirjinta tana kallon bayanshi dan yabata baya, anatse Maheer yace “i hate marriages but for the first time I think shine solution dina and how to end all this problems” yasake shiru kafin chan yace “listen and listen very well, there’s an envelope akan table dina jeki dauka ki bude” share fuskanta Yasmeen tayi ahankali kaman bazataba tawuce table nashi tadauko wani envelope data gani takoma inda take tsaye da, budewa tayi yawanci hotunan Baba ne dashi da wani dan saurayi daya kamo yana kalle kalle yasa a mota, sai wani gida, sai Baba da kayan yan sanda, Baba yafito daga masallaci, Baba dasu Baffan ta suna magana gaban mosque” juyowa Maheer yayi yakalleta yace “I know kinsan waye a hotunan nan dan mahaifinki ne d other mutumin dakika gani is one of my drivers” dan murmushi kadan Maheer yayi yace “Baban ki is secretly trying yakamani at all cost, all the four drivers ranan da aka sakesu suka bar garin wannan ma mamanshi ke rashin lafiya abinda yahanashi tafiya kenan but Babanki yakamoshi secretly yakaishi wanchan secret gidan yana ganamai azaba just sabida yasami information akaina wanda trust me driver chan gwara yamutu daya fadi anything” yadanyi shiru yace “what he don’t know is babu abin Babanki da bansani ba I have men dake binshi 2,4,7 sabida I know mutum kaman mahaifinki bazai taba barina mutumin dayakama yaranshi ba that easily he will do duk abinda zai iya dan kamani, yanzu haka naso sniper na ya harbe mahaifinki 1mins is too much” sosai Yasmeen ke kallonshi dan bata taba ganin cruel, ruthless dan ta’adda irin mutumin nan ba, dan murmushi kadan Maheer yasakin mata yakarasa zuwa gaban table dinshi yadauki kwalin taba yazaro daya yakai bakinshi yadau lighter zai kunna yaga tadan yatsine fuska hakan yasa gently yacire daga bakinshi ya ijiye danji yayi bazai iya sha agabanta ba, yakalleta yace “akwai wani al’ada damu yan mafia kedashi” yadanyi murmushi kadan yace “idan kanada enemy daya addabeka the best way kuyi ending na kiyayyan shine ta hanyar kulla auratayya, idan akai aure kasan bazaka taba iya taba gidan wane ba dan diyarka na ciki, haka kaima baraka taba gidan wane ba dan yarsu kake aure, zan aureki for only 2 reasons Fateema!” Yanuna mata yatsunshi guda biyu yace “one sabida yanda nakasa cireki daga zuciyana kinyi bewitching Pablo Escobar and secondly sabida mahaifinki daya addabeni” sosai take kallonshi kirjinta na faduwa, maida hannunshi kasa yayi yace “idan ban aureki na tabbata zanma mahaifinki abinda bazanso namai ba” tasowa yayi yazo gabanta dab da ita yana kallonta kasa jurewa tayi tasauke idanunta kasa awani kalan hankali yace “I will be sending my father his friends and my brother to gidanku azo atambayi aurenki” dan dukawa yayi yakai bakinshi saitin kunnenta ta saman hijab kaman mai whispering yace “if you dare koda wasa kika fadi cewa nine nake neman aurenki I will first kill that little girl ta gidanku mai shegen kukan nan like you” dasauri Yasmeen tajuyo da fuskanta takalleshi numfashinta dake fita fast fast na sauka kan fuskanshi hakan yasa shima yakalleta in the eyes irin tantirin nan yace “followed by yayarta, then your Mom…” yay dan murmushi irin na mugunta dinnan yace “then ur sweet caring father sannan kuma I will still marry you duk inda kika shiga kuma saikin zauna dani” hawaye ne masu zafi suka zubo mata daga idanu dasauri yadauke kai yace “you can go zamuzo” ya nuna mata kofa da hannu.

44

https://www.instagram.com/p/CtwFCtXITwD/?igshid=YjgzMjc4YjcwZQ==


No comments