Breaking News

Gidan Aunty book 1 page 19-20

 



بسم الله الرحمن الرحيم 💖💖………


 Free Page 19 🦋



A hankali yake bude kyawawan idanuwansa da suka kada sukai ja, dafe goshinsa da ke tsananin sara masa yayi tare da mikewa zaune , bin dakin yake da kallo ta ko ina kafun ya dawo dashi kan hannunsa me ciwo, abubuwan da suka faru dazu ne suke dawo masa, sosai jijiyoyin kansa suka kara mikewa , ganin yana kokarin sawa kan sa wani ciwan kai ya mike tare da shiga toilet,ko kayan jikinsa be cire ba haka ya sakar wa kansu ruwan sanyi, sai faman sakin ajiyar zuciya yake, ya dade tsaye cikin ruwan kafun ya fito daga cikin toilet din , gashin kansa da ke faman d’igar da ruwa ya taba kafin yashiga wata door dake degensa , kusan awa daya da yan mintuna ya fito cikin sabuwar shigarsa, ash din Riga ce a jikinsa sai farin wandon da yasa, cikin sa sai faman tashin daddadan kamshin turaren sa yake, duk da yana yin da yake ciki ba karamin kyau yayi ba musamman gashin kansa da se faman kyalli yake , hatta ciwon hannunsa ya sake masa dressing kafin ya dauki wayoyinsa ya bar dakin , a kofar part din sa ya tarar da zaki sai faman kai kawo yake , Wanda ya ganine yasashi sakin ajiyar zuciya tun dazu yake tunanin ya koma ya duba sa amma yana shakkar shiga, ganin ya fito da kansa yasashi ajiyar zuciya , sau daya king ya kallesa tare da dauke kansa yana lumshe ido, wata hadaddiyar Ferrari la ferrari ya dakko sai faman kyalli take, ganin hakan yasa bodyguards dinsa matsowa, hannu daya kawai ya daga musu tare da nufar motar da zaki yayi Parking, cikin sauri daya daga cikin bodyguard dinnan ya bude masa kofar, bai ce komai ba sai shigewa dayayi, bayan ya kulle kofar sara masa sukai gabaki Dayan su kafun zaki ya tayar da motar tare da barin gidan gabaki daya , lokaci zuwa lokaci yakan dago idanuwansa ya kalli king da tun shigowarsa motar kansa yake a sunkuye kwata kwata ransa ba dadi , ya dago da niyar kara kallan sa yaci saukar muryarsa a bazata “ what happened “, ya gane me king ya ke nufi, be bata lokaci ba ya zayyane masa tun shigowarsa dakin har fitarsa saidai ya boye masa shakesan da yayi duk da yasan zai iya gane hakan.kara lumshe idanuwansa yayi sosai yake jin zuciyarsa wani irin amma a zahiri ko gezau bayayi har suka karasa katafaran asibitin Al_nahyan .


➰➰➰➰➰


Bata dau dogon lokaci ba , sai gata sun dawo ita da bintalo da sai faman ja mata Allah ya isa take a haka har suka kusa zuwa inda bukkar bokannan yake kafun tayi shiru, sai faman zare ido dake , dan ba karamun azaba Tasha ba a hannunsa, yana ganinsu ya fara babbaka dariya take da sudar baki kamar wani maye, jikinsa sai faman tashin wari yake .kara babbakewa da dariya yayi “kinsa mu duniya kamar yadda kuke so, burikanku zasu cika kamar yadda nayi muku alkawari, ayukanki da akai miki na baya bazasu taba fito wa fili ba hhhhhh” ya karasa tare da sakin sautin dariya Mara dadin ji,nannauyar ajiyar zuciya Dije ta sauke tana jin wani farincin na ratsata ta ko ina, bintalo na gefe jin ta take kowama zata iya takawa , sai faman washe baki take, kallansu bokan nan yayi tare da jefowa Dije wani magani, “ga wannan maganin kije ki zuba musu a duk inda kika san zasu taka, kada ki kuskura ki dawo nan wajen batare da kin cika aikin nan va,maza ki tafi”saurin daukar maganin Dije tayi sai faman Godiya take masa, tashi sukai da niyar tafiya ita da bintalo ya dakatar dasu”ke kadai zaki tafi, ita anan zaki barta sai kin dawo sai ku tafi a tare , Inba haka ba aikin da kuka fara zai karasa rugujewa da zarar kun isa wajan”, ko karin rike Mata hannu bintalo take bokannan ya daka masu tsawa” ku bace mun da gani “,hakuri Dije ta shiga bashi, bata tsaya sauraran bintalo ba tabar wajan ko tsoron halin da zata shiga batayi,tana fita bokan nan ya daka tsawa” zonan “ , jiki na rawa bintalo ta nufeshi, har kwalla ta fara tsoran ta karyace ze kuma tabata , bata karasa zancan nata ba taji razananniyar muryarsa” zauna anan “, inda ya nuna matane yasata sakin kuka , tsawar da ya daka matane yasa ba shiri ta zauna akan cinyarsa da ya bude,matseta yayi sosai a jikinsa yana shin shinarta, daga nan komai ya canza salo, sosai bintalo Tasha wuya a wajansa, ihu kawai take dan ji tayi azabar da taji yanxu yafi na wancan lokacin , kuka kawai take amma ko kezau bokannan beba sai da ya tabbatar ya biya bukatarsa sannan yayi jifa da ita har lokacin Dije bata dawo ba , ganin hakan yasa bintalo daukar hijabinta tare da rugawa a wuje sai a hanya tasaka hijabin sai faman tsine wa Dije take .


🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧


Zazzaune mutanan gida suke duka a falon dada , king ne kawai babu, zoya na gefan tahee yau sai faman hira take mata ita da ihsan , yan matan ma kowannansu na zazzaune a falon , amrah da sumayya sai faman harara juna suke batare da kowa ya hankalta dasu ba, musamman amrah da lokaci zuwa lokacin takan Kure tahee da kallo, ita kadai tasan abunda take rayawa akanta. Mikewa zoya tayi , aunty tahee please cakes dina zaki dakko mun kinji,jinjina mata kai tahee tayi tare da mikewa , kama hannunta zoya tayi suka soma tafiya, kallansu abeey yayi” yarana ina zuwa kuma “ sun kuyar da Kai tahee tayi “dama zoya tace zan dakko mata abune “, hararar zoya ummey tayi, kin kallanta zoya tayi tana buya bayan tahee, batace musu komai ba shima abeey da ammi murmushi kawai suke , su mamy kuwa kowannansu murmushin ya’ke yake saki, can dining su tahee suka nufa inda cakes din suke dayawa a ajje, kallanta tahee tayi “ wanne kikeso a ciki” wani me kalar chocolate ta nuna mata, daya daga cikin kankanin plate din tahee ta dauka tare da zuba mata chocolate cake din”, har tun juya da niyar komawa kuma sai tahee ta tsaya tare da komawa, cakes din ta zuba cikin kananun plates din tare da jerasu kan babban tray a haka harta karaso falon da suke zaune kowa sai binta yake da kallo, inda su dada suke zaune ta nufa tare da ajje musu tray din, babu Wanda be yi murmushi ba ganin abinda tayi, sosai ta burgesu musamman abeey da dada dake faman sakin murmushi, murmushin jin dadi uncel salim ya saki”mun gode sosai kuwa daughter , Allah yayi albarka “sosai kowa ya nuna jin dadin musamman dada da sai faman shi mata albarka take, abeey ne ya kalleta cikin zolaya yace “an kawo mana abun turawa daughter saura abunda sha”, murmushi ta saki tana sun kuyar da kanta , “tom bari na dakko muku” ta fada tana mikewa har lokacin zoya natare da ita kowa na mamakin sakewar da tayi da ita, murmushi amrah dake zaune tayi ganin ta kara komawa wajan dimming din, bata motsawa saida taga taheee ta futo da wani tray din cikin sa cups din glass ne sai juice din data dakko a kai tazo Daidai wjan da steps dinnan cikin Sauri amrah ta tashi da niyar wucewa sai ta bugar mata kafa batare da kowa ya lurasa sai aunty dake faman sakin murmushi ganin abinda amrah tayi,tray din hannun tahee ne ya fadi kafarsa sosai ta bugu jikin stairs din da kwalba ta fashe, mikewa kowa yayi ganin abinda ke faruwa, gadan Ganda kanta ya taho da niyar Dakar glass din, cikin sauri mutanan gidan suka nufeta , kara kawai tahee ta saki, Jin zata fada ga azaba da kafarta ke mata, ta sadakar faduwa kawai zatayi taji an riketa, sosai ta rike Wanda ya riketan, sai faman sakin kuka take, kafarta harta fara kumbura ga Jinin da yake fita a jikinta..



Ba yawa please .


Comment and share.


Mss Lee 💖✍️.

PAID BOOK 


BOOK 1


Free page 20🦋


Ganin wanda ya riketan yasa ko wannansu sakin ajiyar zuciya sabanin amrah da aunty ta da suka fara farin ciki, hatta sumayya sai da ta tausaya mata duk da ba kaunarta take ba, dada sai faman sallallami take ganin Jinin da yake fita a kafar tata, ganin ta kasa taka kafar ne yasa ta daukar ta gaba dayanta tare da nufar 3 sitter din kujerun, har yanxu fuskarsa a hade ba ko digon dariya ga kuncin da zuciyar sa take tun dazu, hannu yasa da niyar zare kwalbar ta saki karan azaba tare da sakin wani saban kukan, inda kwalbar tashige ya kurawa ido, tabbas yasan in yace zai cire da karfi zai kara raunana mata ne , inda ya kunbura ya kalla da lumshash shun idanuwansa, a hankali ya kai hannunsa wajan tare da Mara matsawa a hankali, kara goce kafarta tayi jin wani saban azaba da take ji,kowa na cikin falon hankalinsa a tashe yake musamman ganin yadda kafar ta kunbura,”son kodai asibiti zamu wuce”cewar uncle musaddiq , lumshe idanuwansa yayi ,bai san takura da zata kaishi da yin magana , shurun da yayi ne yasa abeey kallansa” baka ce komai ba , in baza aje hospital ba sai a tafi clinic room ai ko ”, a fiske ya furta  “no need abeey” kafun ya ciro wayarsa, wasu numbers ya danna tare da kaiwa kunnansa , bai jira anyi magana ba ya furta “ large first aid box” yana gama fadar hakan ya kashe wayar, dan gajeran murmushi ya saki , yasan tabbas akwia abunda yake damun gudan jininsa tun ba yau ba amma da muwar da ya gani yanxu ta nunka wacce ya saba gani, fatansa ya samu wacce zata gyara masa wannan murd’ad’d’en halin nasa. Kukan tahee ne ya fargar dashi tunanin da ya fada , kanta na cinyar ummey sai faman sannu suke mata,dada ma ganin ciwon kafarta na kokarin tashi yasata yin shiru, kara rintse idanuwansa yayi ganin tana kokarin sa masa ciwon kai, dabadan su abeey ba da ba abunda zai Hana be faffalla mata mari ba, ko cikakken munti biyar ba ai ba sai ga zaki da wani dogon first aid Box a hannunsa, king ya ajiyewa kafun ya gaishe da mutanan gidan, a hankali yake motsa hannunsa kafun ya bude first aid box din, abunda zaiyi anfani dasu kawai ya dauka tare da nufar kafarta, sosai take hawaye duk da ba a jin sautin kukan nata,kwalbar data shige mata kafa yake kokarin cirewa sabida zafi batasan lokacin da ta kama hannunsa ba tana rintse idanuwanta,fuskarta duk ta baci da hawaye , cikin sauri ya dago da idanuwansa jin  shock din da yaji  lokacin da hannunta ya taba fatarta,

Sau daya ya kalleta tare da dauke kansa, be wani sha wani dogon wahala ba ya cire mata doguwar kwalbar ,bin kafarta data kunbura yayi da kallo kafun yayi mata dressing dinta,har yanxu akwai ragowar hawayen a fuskarta, kowa na falan sai faman sannu yake mata,sabanin aunty dake mata dan dole, amrah kuwa sai faman danasanin turatan dayi take ganin king ya tabata,a fakaice take goge kwallar ba’kin ciki, yana gama dressing din be jira cewar kowa ba ya far part din fuskarsa a had’e har yanxu.


🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧


Tunda Dije ta koma gida neman hanyar da zata kuma sawa su oumma maganin nan tayi, ganin kowa hankalinsa ba ya kanta tashige nan garansu sai faman ya tsine take kuwa, taci sa’a kuwa tunda ta shiga bataji motsin kowa ba harta sa kafa zata shiga ciki jin motsin ana taba ban daki yasata barbada maganin nan cikin sauri tare da barin wajan , Daidai taheer na fitowa daga ban daki, bin kofar da aka ‘bane yayi da kallo a tunaninsa oumma ce ,ganin babu Wanda yake shigo musu ban gare sai neman Futuna, kofar dakin nasu ya nufa,kamar Wanda aka rufewa baki ko sallama beyi ba yashiga dakin, jiyai kansa ya sara masa, duk dakin ya canza masa, waje ya samu ya zauna kamar Wanda aka tsira kuma ya mike, sosai yaji dakin ya fita aransa bazai iya zama ba, har ya taka kafarsa da niyar shiga inda oumma take sai kuma yayi saurin ja da baya jin kamar ya taka kaya, sosai yaji jikinsa ya daukan zafi , da yayi baya baya kuma sai yaji zafin na raguwa, da sauri ya fita daga dakin jin zafin na raguwa ne yasasa rugawa da gudu da barin gidan baki daya duk akan idan Dije da ta la’be a kan soro ganin yadda taheer ya fitone yasata sakin dariya, a zuciyar ta sai gode wa boka take .


A daki kuwa kusan awan oumma d’aya sai faman zagaye take ganin har yanxu taheer be shigo ba, kofar toilet din ta nufa tare da kwankwasawa”taheer !! Taheer!! Taheer!!’ Ganin ta kirasa har sau uku be amsa ba yasata bude ban dakin, babu kowa a ciki sai ruwan dake nuna anyi anfani dashi, batayi tunanin komai ba ta koma ta zauna kusan yan mintuna ganin be dawo ba har lokacin yasa hankalin oumma ya fara tashi, hijabinta ta dauka da niyar lekasa, a tsakar gidan ta samu wasu daga yan gidan zazzaune kamar yadda yazama al’adarsu, Dije dake zaune har lokacin ne Tasaka shewa” za a tafi yawan tazubar Din da aka saba cikin dare” oumma bata kulataba tayi ficewarta dan tasan kota musu bayani ba saurara zasuyi ba, ganin hakan yasa yan tsakar gidan fara kuskus. Duk inda tasan zai iya zuwa taje har wajan da yake koyan faci taje amma bata tarar dashi ba , sosai hankalinta ya kara Tashi sanin da tai masa ba ya dare haka ko zeyi ma zai fada mata kafin yayi, bata koma gida ba taci gaba da duba shi duk inda taje sai tayi musu kwatancan sa ko sun gansa amma babu Wanda yace ya gansa, hankalinta ba karamun tashi ya karayi ba ganin har karfe Tara da yan mintuna ba taheer ba alamunsa, sosai ta bazama nemansa har tayi nisa sosai da gida, kuka oumma kawai take fatanta Allah ya tsare mata d’anta, tunanin ko ya koma gida yana nemanta shima yasata juyowa daniyar komawa gida, Daidai zata tsallaka titi wata had’ad’d’iyar  bakar prado tai bal da ita, birki me Motar yaja cikin sauri tare da fitowa, shima na bayan motar be jira an bude masa ba ya bude da kansa cikin takun dattako ya karaso wajan, ganin yadda take zubar da Jini ga bakowa a wajan yasa ya kalli babban dansa dake gefensa, “khaleed kamata a sata a mota”,ba bata lokaci kuwa khaleed din da aka kira ya sata a mota ganin Jinin har yanxu be tsayaba yasa ba bata lokaci suka tada motar tare da barin Wajan batare da sun damu da sanin daga ina take ba, a Tunaninsa in ta samu lapiya sai tayi musu kwatance su dawo da ita.


**ganin har karfe goma ta wuce ba taheer ba oumma yasa dije kara sakin wata dariyar mugun ta , bintalo ma dake zaginta ganin har lokacin nan basu dawoba yasa ta dena zagin nata sai faman washe hakwara suke burin su ya cika , a yan gidan kuwa babu Wanda ya damu da dawowarsu balantana suyi tunanin ko wani abune ya samesu , hajiya kaka tabawa kuwa tun safe tana daki sabida cikon kafarta da ya sata a gaba , duk abun nan da yake faruwa batasani ba , babu Wanda yayi tunanin sanar da ita, a ganinsu in oumma ta dawo daga barikinta sai tayi musu bayani..


🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧


Tun da ta tashi daga bacci taji zuciyarta na faman tsinkewa ,burinta  yau taji muryar su oumma dan sosai tayi kewarsu, kafarta da ta kara kumbura ta kalla kafun ta mike a hankali dakyar take taku har ta karasa ban daki, ta dau dogon lokaci a cikin bayin sabida ciwonta kafun ta fito daure da towel , komai cikin karfin hali take yinsa , pant din ta kawai ta saka tare da doguwar Riga batare da tasa bra a ciki ba,kadan ta shafa turarenta tare da komawa kan gadon, sosai kafarta ta kara kunbura dan basosai take takataba, kwankwasa kofar da akai ne yasata dago da fuskarta, ammi ce ta shigo dakin bayanta kuma  asabe ce dauke da babban tray a hannunta, ya jiki tayi mata tare da ajje mata tray din abincin, cikin tausayawa ammi ta kalleta, “sannu daughter, ko asibiti zamu tafi ne” saurin girgiza mata kai tahee tayi, “ah ah ammi ba sai munje asibiti ba zai warke ai”, sosai ammi ta kalleta “Anya kuwa daughter kalli yadda kafarki ya kunbura, gaskiya asibiti zamu tafi “ta karasa tare mikewa , saurin kamo hannunta tahee tayi kwalla harta soma taran mata” Allah aunty da gaske nake miki ya dena , saura kadan kuma shima ba sai munje asibiti ba”, ta karasa kwallar na sakko mata, girgiza kai ammi tayi daman Tasan halinta da mugun tsoran asibiti, shiyasa bata kuma cewa komai ba ta gyada mata kanta”shikenan ga abincin kinan Kici kafin na kawo miki magani”, katuwar ajiyar zuciya tahee ta sauke tare da sakin mata guntun murmushi “insha Allahu aunty”, bata kuma ce mata komai ba ta kama hanya tare da barin dakin, ganin ta fita ne yasata mikewa a hankali tare da dakko abincin da aka kawo mata , sosai taci abinda sabida yunwar da takeji, ta dade zaune a Wajan har ta fidda ran shigowar ammi sai taji an bude kofar dakin, ammin ce kuwa ta shigo,har ta bude baki da niyar yin magana ya shigo dakin fuskarsa a hade taka ina kamshin turarasan yacika wajan,saurin sunkuyar da kanta kasa tayi tana hadiye abunda ya tarar mata a makoshi, lokaci d’aya taji wasu hawaye na tarar mata, kallansa ammi tayi “son duba mata kafar naga har yanxu kunburun be sace ba”, be motsa daga jinginar dayayi ba har yanxu , har ammi ta bude baki da niyar sake magana ya bude lumsassun idanuwansa tare da zubasu a kanta a hankali ya soma tafiya kafun ya karaso gaban gadon, bin kunburarriyar kafar yayi da kallo ganin tafi kunbura fiye da jiya kafun ya dauke idanuwansa ya maida kan ammi,a fiske ya furta “man zafi” cikin sauri ammi ta karasa gaban mirror din tare da miko masa man da ya tanbaya, TAHEE sai faman zare ido take, akan kujerar dake gefen gadon ya zauna, hannun doguwar rigarsa ya fara nannad’ewa tare da tsuke fuskarsa, ganin hakan yasa ta fara sakin kuka kasa kasa,a hankali ya daura hannunsa kan kafar tasa, Baisan lokacin da yayi saurin daukewa ba sabida shock din da yaji , kusan sakanni ya dauka kafun ya mayar da hannun nasa kan farar kafarta da yayi jajur Sabida kunbura,kuka tahee ta saka jin azabar da taji be kulataba sai ma rike kafar da yayi gam yana kara hade fuskar tasa, ganin yadda tahee take kukane yasa ammi saurin barin dakin dan tasan in tazauna zata iya hanashi matsa kafar bayan ita ta kirashi da kanta. Tsurawa kafar ido yayi kafun yasaki iska kadan ta bakinsa, a hankali ya soma matsa wajan da ya kunbura cikin kwarewa, kara tahee ta saki tare da kankame hannunsa, kafarta take san kwacewa amma ta kasa sabida yadda ya rike kafartata, wani kukan ta kara saki gabaki daya tafita daga hayyacinsa, be kulata ba sai ma kara matsa kafar da yayi yana shafa mata maganin, Daidai inda yafi kumbura ya dora hannunsa , wata karar tahee ta saki da iya Karfiinta na karshe ta ture hannunsa da ya kara fama ciwon, a maimakon ya saki hannun sai kujerar da yake zaune tayi baya yayinda tahee ta fado ta gaba, gaba d’ayansu suka fadi kasan, shi yana kasa ita kuma ta fado kansa, saurin rintse idanuwansa yayi tare da fusgar nunfashin dake kokarin kwace masa, kara lumshe idanuwansa yayi lokaci d’aya kuma ya ware idanuwansa jin saukar lips dinta akan nasa tare da saukar tsayayyun breast dinta a jikin sa adaidai lokacin da ake turo kofar dakin ………

      (Tofaa 😂)…..


Comment and share…..

No comments