Breaking News

Gidan Aunty book 1 page 15-16

 


BOOK 1📕 

بسم الله الرحمن الرحيم……..



Free page 15 🦋


Karfe 8:30 na dare, amrah ce sanye da d’an karamin towel da ko gwiwa bai karasa mata ba,sai uban gashin attachment din dake yawo a bayanta ,waka ta saka tana tikar rawarfa sai da ta gaji dan kanta sannan ta kashe tana sauke ajiyar zuciya. Toilet ta nufa da nufin watsa ruwa ko d’an kwali babu akanta, ta karasa kenan zata kunna fanfo, abinda ta ganine ya firgita ta tare da sakin gigitacciyar kara, a guje ta juya da niyar komawa , amma kafin ta karasa wajan komar wata irin mage ce ta fito ta wajan fara tass da ita, wata karan amrah ta saki, tuni ta fita a hayyacin ta sai faman ihun neman agaji take, dan karamun towel dinta ma tuni ya fadi a jikinta, saukar bulalar dataji a fatar jikintane yasata sakin razanannan kuka, sosai bulalar ta shigewa, bata gama shafa wajan ba ta karajin saukar wata bulalar, kuka kawai ta fashe da shi, ba tsaya ba aka dunga zulamata wannan bulalar, gadan gadan farar Magen nan tayo kanta, ganin haka yasa amrah sakin wani gigitaccen kara tana zube a kasa sumammiya.


*******

Tana shiga daki ta fada kan gadanta sai faman murmushi take saki ita kadai, sosai take sakin murmushi idan ta tuno fuskarsa da irin yadda yake hade fuska, take fargaba da tsoransa ya kara shiga jikinta, musamman da taji ammi na kiransa da son.Lumshe idanuwanta tayi amma still shitake gani ,duk da tsananin tsoransa da ya dirar ma , amma sosai ya burgeta a iya ganin da tayi masa. Wanka ta tashi tayi kafun ta kwanta tana adduar bacci, mintuna kadan bacci ya dauketa.


Sosai wasu irin halitta ke binta, yayinda tarike hannun wani da ba’a iya ganin fuskarsa, amma sai faman kareshi take daga cutar dashi dasuke kokarin yi, tun tu’ben da tayi ne yasa ta faduwa, shima Wanda tarikewa hannun ya tsaya har yanxu ba’a iya ganin fuskarsa, kafun suyi wani kwakkwaran motsi , wadannan halittun sun zagayesu sai tsalle suke saki , daya daga cikin sune yayi kanta yana zaro harshe , daidai yana kokarin cabkota wani irin girgiza ya karade ko ina, take a wajan wata katuwar farar macijiya ta bayyana a wajan, daga gefenta kuma wata farar kuliyace me shegen haske , sosai ta fito da farar farcinan, yayinda bakinta yake abune sai faman “meow meow “take cewa. Zabura wadannan halittun sukai kafun su fara Kai musu sara da faratansu, sosai macijin nan da Farar kuliya sukai musu jina jina lokaci daya suka bace batt ba aganinsu. A firgice tahee ta farka da ga mummunan mafarkin data fara duk jikinta yayi gumi sai faman zufa take hadawa, adduar neman tsari ta fara karantawa har taji nutsuwarta ta Daidai ta kafun ta mike tashiga bandaki, mintuna kadan tafito dauke da alwala, nafila tayi tare da adduoin da oumma ta koyasu hartaji ta kara samun nutsuwa kafun ta mike ta koma bacci.


➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰

🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧 


BUNKURE


Duk da tsananin yadda bintalo ke ihun ta hakan be sa yaji tausayintaba sai ma kulle mata baki da yayi da kazamin bakinsa me shegen wari, sosai yake zuba muguntarsa akanta, tsabar wahala kusan sumanta uku , azaba na sawa ta farfado, iya rashin imani saida yayi mata yayi mata kaca kaca ko dan yatsanta bata iya motsawa, se hawayen azaba dake digo mata ta ido, azuciya kuwa ta tsinewa Dije yafi a irga duk da kasancewar ta mahaifiyarta. Saida ya gama lalatarsa sannan ya bawa Dije da ke rabe damar Shigowa ya tafi da ita cikin hade rai, duk jikinta yayi sanyi ganin irin aika aikan da yayi wa bintalo, amma ko saudaya batayi nadamar hakan ba tunda burinta zai ciki, cikin razananniyar muryarsa me tsoratarwa ya daka musu tsawa akan su bace da ganinsa, ganin yadda bintalo ta kasa ko motsine yasasa babbaka dariya” ku sawa ranku aikinku kamar ya tabbatune” sai ga wata kwarya nan ta fado kasa da dan karamun ruwa a ciki jaa da shi, ruwan yasa dije ta dauka ta kwarawa bintalo a gabanta, cikin Karkarwa ta dauka tare da kwara mata, wani irin gigitacciyar azabar kara bintalo ta saki da ya firgita Dije , kara babbakewa da dariya yayi tare da hade ransa , kusan mintuna uku bintalo na kukan azabar nan kafun ta sauke nannauyar nunfashi tare da mikewa da kanta, ganin hakan yasa dijen sakin ajiyar zuciya a haka suka ajiyewa boka kudin da suka zo masa dashi tare da fita da baya baya har suka bar wajan, sai lokacin bintalo ke taku da dingishi dukda azabar da take ji ta ragu babu ita,amma gudun kar a asirinsu ya tonu basu koma gida ba sai wajan shadayan dare lokacin babu wuta, sannan babu me gane halin da suke ciki, zuciyar dije sai faman zillo take akai ta aiwatar da kudurinta kan oumma da suka shige mata hanci , ga wani tsanar su da ke kara ruruwa a

Zuciyar ta.


************

Tunda ya tashi yau be fita ko ina ba sai bayan karfe goma na safe bayan motsajikinsa da yayi, Hakanan yau besan jin kowa a kusa dashi ga yunwa yana jin amma ya kasa motsa koda dan yatsar sane, coffee yake San sha dan haka ya mike cikin takun kasaitarsa kamar kullum, a hankali yake taku sanye Yake cikin black trouser da black singlet , sosai kakkarfar surar jikinta ta bayyana , farar fatar jikinsa sai sheki yake dauka, a hankali ya karasa inda coffee maker din yake, cikin yan mintuna ya gama hada coffee dinsa , a nutse ya zauna kan daya daga cikin sofa din wajen , sipping daya yayi wa coffee din tare da ajjesa, wani irin daci yaji coffee din nayi masa kamar zaisa amai, a hankali ya kara lumshe idanuwansa ko me ya tuna oho, sai gashi ya mike tare da nufar wani daki, ko cikakken minti ashirin beyi ba wani daddadan kamshi ya karade ko ina , a hankali kamshi ya kara kusan towa kafun mamallakin kamshin ya bayyana , sosai shigarsa tayi masa kyau , sanye yake cikin black suit sosai bakin suit din cikinsa ya fito da ainahin kalar farar Tatar’s a da sai sheki take , bakin nan kullum sai kara turuwa yake kamar mai shafa abu wajan, har yanxu fuskarsa a hade take amma sosai yayi kyau , ga diamond watche dinsa sai faman kyalli yake, wayace kare a kunnansa sai faman motsa baki yake ko abunda yake cewa ba aji, be tsaya a ko ina ba sai part din amminsa .


A zaune ya sameta cikin shigar manyan mutane da ta saba , sosai tayi kyau cikin shigarta, kujerar da take zaune ya nufa tare da langwabar da Kai kadan, kallansa tayi tare da dauke kanta, bai ce komai ba sai hannunta da ya kamo ya dora a fuskarsa , a fusge ya furta “sorry ammi”, ajiyar zuciya ta sauke daman ba fushin take dashi ba ganin yaki zuwa haryanxu kuma tayi kewarsa ne yasa ta yi masa haka, a hankali ya furta “ina kwana ammi na “, murmushinta da baya boyuwa ta saki “ ka tashi lapiya son” lumshe mata ido yayi kawai batare da yace komai ba , ganin hakan yasan ammi tasan yan miskilancin ne a kusa, kadan suka taba hira yana amsawa kadan kadan,shafa gefan fuskarsa tayi” da alama wannan son din nawa ne ci komai ba” kara lumshe mata ido yayi tare da bude wa alamun amsa . Mikewa tayi “bari na dafa maka abinci ko” riko hannunta yayi tare da kallanta “ coffee” shine kadai abunda yace mata , jinjina masa kai tayi tare da nufar kitchen din, a tsaye ta samu tahee da asabe na aiki a kitchen , sosai tahee take jin dadin hakan sabida tana Kaunar taga ta iya abinci hala hala , ba tare da ta kalla taheen ba ta soma magana, “tahee hadawa son coffee kafun na kammala dafa masa abinci”, suman tsaye tahee tayi , zuciyar ta sai bugawa take gashi bata da dalilin musawa, kamar wacce zata saki kuka haka ta hada coffee din tare da fita falo , ko ina na falon mayataccen kamshin turaran da ke mata dadi ne ya cika wajan, Zuciyarta sai faman zillo take sabida tsoro, a hankali ta karasa inda yake bayan tayi sallama , cikin in ina ta soma magana “ina.. kwana”, kamar wacce tai da gunki ko motsi beba sai ma sarrafa wayarsa da yake cikin nutsuwa , kamar wacce zata saka kuka ta kara cewa “ina.. kwana”, yanxu ma be motsaba balantana tasa ran amsawar, siraran hawayene suka dan zubo mata kadan tare da sun kuyar da kai, kamar daga sama tayi saukar muryarsa “ fine” , wani murmushi ne ya subuce mata, sosai taji dadin amsawar dayayi, a hankali ya sa fararan dogon yatsunsa tare da dauka cup din, a hankali ya fara sipping, zuyawa tahee tayi da niyar komawa tazo daf da kitchen din ta tsinkayi muryarsa “ who permit you to leave”, sun kuyar da kai tayi tare da dawo wa ciki “ bakowa “ ta bashi amsa , tsawan mintuna goma tana a tsayen , kofin hannunsa ya ajje tare da kyara zama, another cup,”Tom “kawai tace masa tare da nufar kitchen din, har lokacin ammi na tsaye tana masa abinci da kanta, kallanta ammi tayi sai yanxu, sauke ajiyar zuciya tayi “wani cup din yace na hada masa”kallanta ammi tayi sai dai bata ce mata komai ba sai jinjina mata kai da tayi, wani cup din ta kara hadawa tare da nufar inda yake har yanxu zuciyarta bata bar bugawa ba, sallama tayi a falan kamar bazai amsa ba , sai ya amsa a hankali, batare da wani dalili ba lokaci daya taji kanta ya sara mata Daidai lokacin da zata mika masa coffee din, a maimakon ya sauka a hannunsa sai ya subuce ya zube a jikin hadaddan suit dinsa …….


         (😳😳Tahee )……


Manage plx …. 


Masu comment ina Godiya sosai da sosai 


MASU BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAYI MUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581 .


MASU BUKATAR A TALLATA MUSU KASUWANCINSU SU TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581 AKAN NAIRA 500 KACAL.


💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖


DUK KARFIN IZZATA ( star lady )


GIDAN AUNTY (mss Lee )


JINI DAYA (mrs bbk)


YA FITA ZAKKA( maman sayyid)


BABY (mhiz innocent)




💖💖💖💖💖Mss Lee ✍️.

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/JyvVuOvzYyF19np8UmFKV4


💖💖GIDAN AUNTY 💖💖

    (a heart touching love story)


Story & written 

       By 

 Mss Lee 💖


PAID BOOK 


LITTAFIN GIDAN AUNTY NA KUDI NE AKAN NAIRA 300KACAL , MAI SAN CIGABA DA KARANTAWA HAR KARSHE ZAI BIYA KUDINSA TA WANNAN ASUSUN :

7041879581 OPAY 

AYSHATOU GALADIMA , sai a turo da shaidar biya ta wannan number 07041879581.


BOOK 1 📕 

بسم الله الرحمن الرحيم ❤️❤️…

Free page 16 🦋


Sosai tazaro idanuwanta waje tana faman girgiza kai,bata san lokacin da ta karasa kusa dashi  tana kokarin goge masa ba , gigitacciyar tsawar da ya daka mata a lokaci daya da lafiyayyen marin da ya sauke mata ne yasata kara firgita, ga kanta da yake tsananin sara mata, lokaci d’aya taji juwa na dibarta “Dan Allah kayi hakuri” shine abunda bakinta ya iya furtawa, be kuma cewa komai ba sai mikewa da yayi kwasan wayoyinsa,Daidai lokacin da tahee take kokarin fadawa kan wani designer dake gefenta , taku daya yayi ya riko damtsen hannunta tare da Jefata kan daya daga cikin kujerun tare da sakin siririn tsaki, cikin bacin rai ya bar part din azahiri Kuma fuskarsa tananan a yadda take, baka isa fassara yanayinsaba ” me ya Hana ban karyataba “ ya fada a cikin zuciyarsa ransa na kara baci , dogon tsaki yaja iya kasan makoshi, hatta zaki daya bude masa kofa yayi mamakin ganin sa haka amma bashi da hurumin magana a haka har suka koma part dinsa.


Tunda ya jefata kan kujerar da ya tashi har yanxu bata bar wajan ba , sosai taji kanta na sara mata, ta dau kusan minti biyar zaune a wajan tana addua, kafin lokaci daya ta nemi ciwan kan ta rasa gabaki daya, ajiyar zuciya ta sauke sai a lokacin kumatunta ke mata zafin marin dayayi mata , dafe wajan tayi tana sosawa “Mugu kawai” ta fada a zuciyarta tana turo dan karamin bakinta, amaimakon ta koma kitchen kai tsaye dakin ta ta nufa tare da fadawa kan gado tana sauke a  jiyar zuciya har yanxu hannunta na kan kuma tunta.


*******Ta dade kwance a ban dakin a sume, bugun ban dakin da ake da karfine ya farfado da ita, tayi mamakin ganinta kwance a kasa ga tsami da jikinta ke mata,kara bugun kofar da akaine yasata mikewa cikin din gishi, towel dinta dake Yashe a kasa ta dauka tare da daurawa, da Kyar take taka kafarta dake mata tsami, sai bin ko ina da kallo take, da kyar ta karasa jikin kofar, a tsaye ta sami aunty duk ta rude, tana ganinta ta saki ajiyar zuciya” me kikeyi acikin ban daki tun dazu, kinsan irin neman ki da nayi”, batasan lokacin da bakinta ya furta “bacci ne ya daukeni “,kallan ta aunty tayi tana sakin baki “bacci fa Kikace amrah “, gyada mata kai amrah tayi tana turo bakinta tare da rabata tawuce , binta kawai aunty tayi da kallo batare da tace komai ba tabar dakin. Samun waje amrah tayi kan gadonta tare da dakko wayarta dake ajje saman gadan, dogon tsaki ta saki sai a lokacin take tuno abunda tahee tayi mata,azabure ta mike tsaye “ ni amrah , nice yau nake bawa wata yar iska hakuri, ni amrah hmmm” girgiza kai tashigayi “ yau nice na kaskantar dakai na bawa wata shegiya hakuri, wallahi ko zanyi yawo tsirara sai na wulakanta ta sai na musgunawa rayuwarta sai tasan dani take magana “ ta kare zancen tana sakin kwallar bakin ciki…


******* Director part dinsa ya nufa sai faman taunar lips dinsa yake, be bi steps ba ta elevator ya hau , a second floor dinshi ya tsaya ko ina sai faman tashin kamshi yake da sanyin Ac musamman kamshin turaransa da ya kama ko ina na part din, rigar jikinsa ya cire kai tsaye faffadan zurar jikinsa ta fita fari tass dashi,sosai muscles dinsa da 6 spacks dinsa ya fito kallo daya zaka masa kasan ba karamin motsa jiki yake ba,kofar da take facing dinsa ya nufa, ya dau kusan mintuna 30 aciki kafun daddadan kamshi ya karade ko ina , sosai yayi kyau , a maimakon suit yanxu  kananan kayane a jikinsa ,tun daga kan bakar jigar jikinsa tare da bakin wanda jikinsa , sosai yayi kyau cikin kayan , sumammiyar gashin kansa ya fito sosai yau ma kadan daga cikin yalwataccen gashin kansa ya fito har wajan idanunsa, sabida tsananin bacin rai pink lips dinsa ba karamin turuwa yayi ba sai faman tsuke fuskar yake, cikin takunsa na kasaita ya hau elevator tare da nufar 3rd floor, a maimakon hanyar da ya saba bi yanxu wata daban yabi,babban waje ne nashakatawa gata iska me dadin gaske dake huro wajan,kayataccen wajan shakatawa ne a wajan sosai wajan ya hadu,ga gefe d’aya dayake abude ko ruwan sama akai yana dan shigowa kadan kadan , akan daya daga cikin kujerun shakatawan yazauna ne kama da sararin samaniya, sosai yanayin wajan yasakashi cikin nutsuwa sai faman lumshe ido yake, daga gefensa ma wani cup ne me shegen kyau cikin sa wani lemone kamana da sararin samaniya shima.sai faman lumshe idanuwansa yake yana budewa, wayarsa dake ringing a hankali ya dauka batare da bata lokaci ba, Ahankali yake magana ko nakusa dashi ba Lalle yaji me yake cewa ba,sai lumshe kyawawan idanuwansa da yake faman yi.


🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧

Futowar da ammi zatayi a kitchen ne taga babu king babu tahee, tsayawa bin falon tayi da kallo kamar anan ne zata gansu,a tunaninta tahee ta koma daki ne shiyasa bata bita ba ta dauki wayar ta da niyar kiran king, tana kara wayan a kunnenta ta haye stair case din din falon..


A dan kwanciyar da tayi batasan lokacin da bacci ya dauketaba, wasu matasan yara tagani da akalla befi su bata shekaru uku ba, kyawawa dasu sai faman kuka suke , daga gefensu wani farin macijine shima tass dashi, kallan tahee dake gefe sukai sai suka kara fashewa da kuka , suna kuka suna biyota , cikin tsorata tahee ta fara jan baya, girgiza mata kai suka shigayi, cikin daddadan muryarsu “sun kashe mana farin cikin mu , sun cutar damu, bamuyi musu komai ba, laifin me mukai musu, nace laifin me mukai musu” suka karasa cikin data tsawa , firgita tahee tayi da yanayinsu, ganin sun tsaye ne yasa itama tsayawa,cikin rawar murya tahee ta fara magana “su..suwane ku, me nayi muku”, dariya suka saki tare da kara sakin wani saban kukan, “SIF,LOLA,”sai kuma farar magan ciki ta shafa can macijin nan” SUSAN”, tana gama fadar haka suka kara sakin kuka tare da bace bat kamar basu taba wanzuwa ba. A firgice tahee ta farka daga baccin da ya dauketa bakin ta dauke da addua , shafa wuyanta da ya dan rike tayi” me yasa nake yawan mafarkin masu sunannan,su wanene su”ganin babu me bata amsa yasata mikewa , kayan jikinta ta cire tare da shiga wanka , mintuna kadan tafito daga nan dakin, daya daga cikin abayoyin da ammi ta bata ta saka , gaban mudubin dake shake da kaya ta nufa,kurawa fuskarta ido tayi ganin irin sahirtaccen kyan da tayi a cikin kwanaki uku da tayi a cikin gidan , sanye take cikin red Egyptian abaya sai faman walwali stone din jiki ke dauka,asalin farin fatarta ta buzaye ta fito tass a jikinta, yayinda cikakken yalwataccen gashin kanta ya sauko har wajan kugunta, sosai bakin kwantaccen gashin goshinta ya kara kwantawa tare da dogon siririn hancinta , ba make up ne a fuskarta ba amma fadin haduwarta bata lokaci ne musamman dan karamin lips dinta da ya fito tass dashi kamar wacce ta saka janbaki,bakin kwalli ta saka da ya fito da farin kyawawan idanuwanta, sosai kwallin ya fito da asalin kwayar idanunta,cikakkiyar gashin girarta da dogayen eye lashes din idanuwanta su suka kara fito da ainahin kyawun fuskarta , ba ma a bociyar lip gloss bace shiyasa tabar dan karamun lebenta a haka, ribbon dinta ta dauka shima red colour tana kichiniyar daurashi, sosai ta jigata kafun ta daureshi sabida cikowarsa,mayafin abayarta ta dauka tare da yafashi saman kanta, red din takalmin ta ta saka , gaban mudubin ta kara komawa tare da karewa kanta kallo , murmushi ta sakar wa kanta tare da rufe fuska , “ ke din me kyau ce “kalmar da kullum taheer ke fada mata, murmushi kawai ta kara saki , tayi kewarsu sosai, hanyar fita daga dakin ta nufa bayan ta gama feshe jikinta da turaruka, Daidai lokacin da yan matan ke shigowa part din,amrah sai faman dingishi take haryanxu jikinta be dena tsami ba, sakin baki tayi ganin irin kyawun da tahee tayi, bama ita kadai ba hatta su ihsan duk sakin baki sukai suna binta da kallo, gaishe da su tayi babu Wanda ya amsa mata sai ihsan dake faman sakin murmushi, “tubarkallah Masha Allah , gaskiya ke kyakkyawa ce tahee”,sun kuyar da kai kawai tahee tayi tana wasa da yan yatsun hannunta, binta da kallo su sumayya sukai kowa yana hadiye abunda ke ransa, dogon tsaki amrah taja tare da karasa kan daya daga cikin kujerun falon, sosai take bakinci, dama ace Itace take da wannan kyawun, wani dogon tsaki ta kuma ja tare da daukar wayarta suma duk yan matan waje suka samu tare da zama ,ihsan ce ke kokarin magana ,jin sallamar zoya ne ya katse mata zancenta, inda Ihsan take ta nufa “aunty ihsan” rungumeta ihsan tayi “na’am my baby”kallan yarinyar da aka kira da baby tahee tayi , Itace dai yarinyar da ta gani tana bacci,”aunty ihsan wai ina da wata aunty tana ina “murmushi ihsan ta saki, “toh daman bazuwan kowa kikai ba sai na auntyn taki ko”dariya zoya tayi tana rufe fuskarta , itama murmushi ihsan din ta saki “oya kinganta” juya wa zoya tayi tare da kallan Wanda aka nuna mata, zaro fararan idanuwanta irin na king tayi, “aunty ihsan tana kyau, harta fini ma, amma yaya king dina ya fita” dariya ihsan ta saki kawai , sai alokacin tahee taga tsananin kamanninta da Wanda yake zuwa part Dinsu,murmushi kawai tahee ta sakar mata, itama murmushi zoyan ta saki “Aunt ya sunanki” taheera shine kadai abinda tahee tace,kara zaro ido zoya tayi “sunanki me dadi , ni kuma zoya yanxu Kema kinzama aunt dina kinji”girgiza mata kai tahee tayi sosai yarinyar tashiga ranta, duk wannan abun su sumayya na zaune suna kallan ikon Allah musamman amrah dake jin kamar ta samu wuka ta caccakawa tahee..shigowar ammi ne ya katsemata tunanin da ta shiga,”yaude yan mata na sai yanxu nake ganinku” ko wannansu murmushi ya saki sabanin sumayya da amrah da suka saki na yake “Aah ammi kinsan akwai school shiyasa “gyada musu kai ammi alamun gamsuwa kafin ta mike ,”yanxu dai ku Tashi ku kaiwa son abinci sai a dawo a yi hirar”, cikin firgita kowannansu ya zaro idanuwansa tare da furta YAYA KING…..



Comment and share .


💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖

Duk karfin izzata

Gidan Aunty

Ya fita zakka

Jini daya 

Sarki sameer

Baby .



MSS LEE💖..

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/JyvVuOvzYyF19np8UmFKV4


💖💖GIDAN AUNTY 💖💖

    (a heart touching love story)


Story & written 

       By

    Mss Lee 💖


No comments