Breaking News

AQIDARMU Book 2 Page 8

 🅿️8️⃣





Bayan awa uku aka dawo saidai ba shari'a a ka sanar alqali ya 'daga shari'ar zuwa sati shida masu zuwa sannan kotu taci tarar Hayat 300k na taka dokar qasa wajen 'daukar mataki a hannunsa da haka a ka 'daga shari'ar 




Baba da General da Taimur na zaune inda su ke Mummy ta nufi Hayat ta riqoshi tana furta pls son ka koma gida inda yanzu ka huta kaga dr yace motsinka dayawa bai kamata ba ok ya furta tace zanje na duba lauya kafin na qaraso ta wuce su Najwa su kace yazo suje saidai hankalinsa na kanta ganin tana zaune itama har yanzu ga duk 'yen gidansu sun fita saidai yana qarasawa escorts na isa suma hannu su ka kai zasu ta'bata da nufin zasu 'dauketa ya kaiwa 'dayan naushi inda take su ka tarar masa Mimi ta fara kuka tana furta *pls mine ka bari* sosai su ka fara naushe2 shi da su inda su Abu'noor su kayi2 Hayat abu yaci tura inda 'dayan ya kaiwa Hayat wani wawan naushi a wuya ya fa'di ba ko motsi Mimi ta saka ihu tana tsugunawa kansa escorts 'din su ka fisgota su kayi gaba 



Cikin mugun zafin nama su Abu'noor su ka taru kansa abu'Nawwal ya ta'ba wuyansa yaji shiru ya kalli 'yen uwansa cikin tashin hankali saidai su ka nutsu su ka 'dauke shi da zuwa 44 




Najwa kuwa tana office tana magana da lauyansu domin tana son su 'daukaka qara zuwa kotun qasa tanada wasu shahararrun hujojji da zata ga bayan Baba Safwan da General Taimur sun gama shirya komai da lauyan ta fito ta samu sabon tashin hankali a gogice tabi 'yen uwanta suka nufi 44



A falon baba su ka ajiyeta Salman da Baba na tsaye 



Wani irin Mari Salman ya sakar mata a kumatu da sai da tayi ta da gaske kafin idanunta su ka kara bu'duwa baba ya fara magana 




A yau ba sai gobe ba zaki bar kaduna ko da yake duk inda kuka je binki ya keyi ko.? Toh wannan karon za ki ga inda zaki zauna har zuwa ranar da zamu koma kotu hawaye kawai ta keyi suka fita su ka barta tana kuka






Bayan kusan 1h Salman ya shigo da akwatinta a hannunsa ya furta "muje" a hankali ta miqe ta tanabin bayansa su goggo su mami duk suna waje suna kallon su har suka wuce ya bu'de mata baya ta shiga ya tayar suka fita gidan




Comma Hayat ya shiga mummy sai kuka ta keyi ta kasa zaune ta kasa tsaye Najwa kuwa ta gama kaiwa bango da duk al'amarin ya kaita bango tayi shiru 





Ji tayi yayi parking bata motsa ba taji an bu'de wasu gardawan mata biyu suka rikota su ka fito da ita sai lokacin ta 'daga kanta tana kallon sunan gurin da aka rubuta da manya haruffa *REMINDING HOME BARNAWA KADUNA*  taji matan sun jawo ta da arfi kukan ma kasa yinsa tayi sam ta nemi hawaye a idanunta ta rasa har wani 'daki kamar sales na prison suka jefata katifa ce kawai a ciki suka kulle ta zauna tayi shiru tana kallon faratunta 





**************





Yau kwanan Hayat biyar yana comma sai Mimi da ke cin qaniyarta a Reminding home saidai sam ba wannan bane damuwarta "kwana ta keyi sallah tana masa addu'a har gari ya waye tana kan dadduma tayi haske fayau ta rame..




Najwa ta gama komai na kararsu inda yanzu lauyan ta ke jira da zai nema a mayar shari'ar babban kotu shima baya asar ne suna jiransa su Abu'noor duk sun koma Iran sabida ayyukansu saidai ko yaushe suna kan video call da Najwa 





General da Taimur ne a 'dakin General su ke magana Taimur yace



Daddy wai to yanzu in still bai bada sakinba yaya za'ayi? General yayi ajiyar zuciya yace kai dai ka bar komai hannunsa banason ka qara yin wani abu tunda ka kai bakada kula yanzu da ban kashe maganar nan ba a ka gano kai kasa masa bom da yanzu kome zanyi sai ka fuskanci hukunci sabida shima kaga Danginsa masu shine kuma sunada zumunci zasu tabbatar sun hukuntaka 




Hawaye mama ta fara tana mamakin yadda Taimur ya zamani me son kansa dukda ta bashi labarin yadda suke kamar tagwaye ita da maman hayat auren baban Hayat ya ne yasa ta nisanceta a amma har gobe ko cikin 'yen uwanta da su ke ciki 'daya bata da wanda take kauna kamar zainab



Ita mamaki ne abin ke bata just 'dan kwanakin da Mimi tayi da su ne Taimur ya kamu da sonta haka har yaje yin kisa dominta





A hankali ta juya tana sharar qwalla ita gashi har yanzu ko Yasmin bata sakewa da ita sabida fushin abinda su ka yiwa 'yer uwarta amma zata neme ta ta mata magana da neman yafiyarta har a kan cikin da suka je fiddawa 





Hayat dai har yanzu yana comma wanda hakan ya zamewa su baba Zuma suna fatan ya qarasa ko sun huta suna kuma jin tsoron in bai mutu ba har ranar komawa kotu alqali yace ya 'daga shari'a har sai ya warke..





Mummy da Najwa kuwa sun bar komai sun tare asibiti su kansu kana ganinsu duk basu cikin hayyacinsu 





Wannan matsalin da rayuka dayawa ke ciki Wai duk kan babancin AQIDA ne Allah ya kyawta ya mana jagora.!






"Yau 3wks mimi ciwo yaki ci yaki cinyewa tun bayan da tayi sati a gurin ta fara rashin lafiya tun suna banza da ita har suka dawo suka fara kula da ita inda gwajin farko a ka gano shigar ciki a ka kuwa kira baba a ka sanar masa ya zabura yana furta Innalillahix3 




Ko Salman baba bai fa'dawa ba ya kira salisu su ka nufi gidan a office 'din dr baba na shiga Najwa na zaune itama 




Tsayuwa yayi cikin mugun tashin hankali yana kallonta Sanye da Bakar abaya da 'dankwalin ta yane kanta sai songlass a idanunta tsaf a balarabiyar 



Ta miqe ta miqawa baba takardar tace (ka duba ga original hannuna tana 'dauke da cikin sati uku kuma wlh tallahi cikin nan ya fita ko da kansa ne sai na 'daure ka har igiya ya saura ta yi tsaki ta fita 




Yawu baba ya ha'diya gumi ya taru masa a goshi kamar mai saran itace ya furta *wannan wane irin qaddara ne*?

💖AQIDARMU💖







PART2 




No comments