Breaking News

AQIDARMU Book 1 Page 9-10

 🅿️9/10




Kallonta yake kafin ya miqe ya 'dauke ta ya ha'da mata ruwa cikin baf ya shigar da ita ajiyar zuciya ta saki mai nauyi da 'dan qara sabida sai yanzun taji gidinta yana mata wani zugi ba cin wasa Hayat ya mata ba da kansa ya mata wanka sau biyu ya canza ruwa kafin ya tallafo fuskarta yana kallonta ya ce "baby zaki yi wankan tsarki"? Girgiza masa kai tayi duk idanunta sun nutse sosai jikinta yayi tsami hot kiss ya qara mata ya fito ya barta tayi wankan tsarki shima ya nufi bathroom 'din 'dayan 'dakin yayi wanka da na tsarki ya fito nan ya ga bata fito ba ya nufi bathroom 'din tana zaune but tagama wankan jiri ne ya hanata tashi riqo ta yayi suka fito ya saka mata jallabiya ya saka mata hijabi yace tayi sallah a zaune hakan kuwa tayi ya fita ya kirawo Banat ya yi sallah ya shiga kiching ya ha'da mata noodle da tea mai kauri ya zo har inda tayi sallah ya 'dauketa cak ya zaunar kan cinyarsa ya cire mata hijabin ya fara bata abincin taci sosai tasha tea bu'de tsakanin qafafunsa yayi ya kwantar da ita cikinsa nan da nan ta fara bacci shima gyangya'di yake ...



7:45am Banat ya iso ya sakawa mimie drip yace Hayat ya tabbatar drip 'din ya qare kada ya barta ta cire to yace su kayi sallama baccine mai nauyi ta keyi don haka ya shirya ya shiga Office yana office Mummy ta iso ta shiga ganin babu motarsa ta tabbatar ya qarasa office ne 'dakin tashiga taga mimie still da drip hankalinta ya kwanta et tabbas basu qara wani shirmen ba ta dawo falo ta jefa layinsa




Yana ma cikin meetings ya fito ya 'daga call tace masa zata shiga kasuwa yiwa mimie da yayanta tsaraba "ok" yace su kayi sallama shiru yayi a hankali ya jefa kira a ka 'daga naji yace mai 3steps tnx yace ya tsinke call 'din...



Baba babba ya kalli maman Safwan yace binta karki damu a kan alaqar Salmanu da Safwan da can ba ke kika qulla shaquwarsu ba tun suna yara haka bamu zamu shiryasu ba aure dai Farida da Safwan zan maidashi babu fashi ranar juma'a da yardar Allah babu mai hanawa to tace yaya amma don Allah yaya a yiwa Salmanu da Safwan sulhu su manta komai domin hakan ne zai qara zumunci tsakaninsu da kuma auratayyar Farida da Safwan to baban yace IA Allah ya shirya mana su baki 'daya amin tace yaya ni bari na wuce yamma ta gabato malam yace nace maka yana shigowa gobe da yamma IA yace to Allah ya kaimu kice masa kada ma ya damu nan zanyi komai kamar yadda nayi na farko dukansu yarana ne godiya taci gaba da yi kafin ta wuce 



Sai kusan 5:pm mummy ta dawo Hayat bai dawo ba still mimie na bacci kiching ta wuce taje ta 'danyi girki ta zubawa mimie ta kai mata gefen gado sai lokacin ta kalli mimie taga yadda tayi wata fayau kamar sai kyalli take amma ta zube ta kai 3mnts tana kallonta kafin tayi ajiyar zuciya ta fito 'dakin tana fitowa yana shigowa ta kalleshi shima har ya zube mugun tausayinsu mummy taji saidai batada yadda zatayi dole suyi hakuri murmushi ta saki tace babyna sai yanzu..? Ajiyar zuciya yayi ya zauna kusa da ita ya ajiye mata babbar paper bags yace tsarabarsu twins murmushi tayi tace da baka yiba domin suma sunce nan da 2wks zasuyi and shigo da sunyi hutu ok yace su yayi shiru shafa fuskarsa tayi tace kaje kayi wanka kaci abinci ka sakemu gida jirgin safe zamu bi qura mata idanu yayi na 1mnt kafin yayi ajiyar zuciya ya miqe 'dakin ya shiga a hankali ya zauna gefenta still tanata baccinta hannunsa ya kai yana abada fuskarta kafin a hankali ya tura hannunsa aljihu ya 'dauko wata 'yer akwati mai 'dan tsawo da 'dan fa'di ya bu'de wani kyakykyawan jigida ne na qugu amma wannan na gold sannan mai 3steps yayi masifar kyaw da haruffa a jiki kamar haka (stay for me forever) a hankali ya yaye mata mayafin jikinta ya 'daga jallabiyar jikinta ya tura hannunsa qugunta ya saka mata ya kalli yadda yayi mata kyaw wayarsa ya zaro yayi pic 'din qugun nata ya gyarata ya mata salon peck yana kallonta kusan 5mnts ya share qwallar da ta taru masa ya fito 'dakin ya nufi 'dayan 'dakin can yayi wanka yayi sallah ya canza jikin wando jeans da shirt mai qaramin hannu yayi kyaw sai agogo ya fito kallonsa tayi tayi murmushi tace my boy bari na tayar da farida taci abinci naga drip 'din ya qare sai mu wuce sabida mu samu mu gama shiri da wuri ok yace ta miqe ya fita mota ya shiga yana jiransu




a hankali mummy ke tashinta da kyar ta bu'de idanunta har ta ware su mummy tayi murmushi tace in taimaka miki ko zaki miqe da kanki.? Girgiza kai tayi alamar bazata iya ba sabida har lokacin tanajin jiri mummy ta taimaka mata ta miqe ta rakata bathroom tayi alwala tazo ta zauna tayi zuhr da asr mummy ta bata abinci da kyar ta 'dan ci ta ture ta nata 'dan satar kalle2 mummy ta gane ta sarai Hayat ta ke nema ta yi ajiyar zuciya tace bari mu wuce dare na yi ta miqe ta 'daukar hijabinta da h/bag tasa mata takalmi suka fito a qofar motar ne tunda suka fito ya ke kallonta har suka qaraso mummy ta bu'de mata baya ta shiga itama bayan ta shiga ya tayar yana driving titi kawai ya ke kallo sai kallonsa take amma yaqi yarda su ha'da idanu har su ka iso gidan mummy ta fito ta riqota suka fito ita mummy ta riqeta suka wuce benensu tanata juyawa shima tunda suka fita bai qara juyawa ba ya tayar da motar ya bar gurin kuka ta saki tana fisge hannunta cikin na mummy ta juya zata bi motar mummy ta riqota zama tayi qasa ta qara sakin kuka sosai wani irin tausayi mummy taji sun bata wani irin mugun son junansu suka kamu da shi kuka ta keyi sosai mummy ta tsuguna gabanta tana furta "Farida kiyi hakuri kinji"? Kizama jaruma komai mai wucewa ne pls kizo muje kada a taru a kanmu yanzu kuka take sosai a hankali mummy ta riqota ta 'dagota ta rungumeta tana shafa bayanta an da'de kafin suka shiga ciki 



Yana tuqi kansa na mugun sara masa ya fara ganin jiri2 ya parking ya jefa layin Banat yace ya sameshi gida yau yanason suje yawon dare ok banat yace ganinan zuwa bayan sunyi sallama ya tayar da motar saidai wani irin mur'dawa zuciyarsa ke yi kansa kamar a na buga masa guduma idanunsa kamar yayi yana ya fara mutsuke idanun sabida baya gani da kyaw a haka ya ke driving motar wani company furnitures na zuwa yana zuwa sam baya gani nan suka yi mugun buguwa inda qatuwar motar funitures 'din ta daki motar Hayat yayi can fege ta wullashi hankali a tashe motane suka firfito daga inda suke wasu daga motocinsu suka yi can gurin motar Hayat da ta kwankwatse babu alamar mai rai a ciki



Tana ninke kaya taji gabanta yayi mugun fa'duwa ta saki kuka mai qarfi tana kama irjinta baba talatu da Mummy suka shiga hankali a tashe suna tanbayar ta "kuka ta qara saki sosai tana furta "zuciyata" kallon juna su kayi kafin mummy tace mai ya sami zuciyarki.? Kallonsu tayi jikinta yayi sanyi ta kasa magana ganin kamar suna mata kallon ta samu ta'bin hankali sunkwi da kanta tayi hawaye na kwarara a idanunta kamar fanfo wani irin bugawa irjinta ke yi kamar zuciyarta zai fito magana tayi cikin zuciyarta "ya Allah ka sassautamin abinda na keji" a hankali duk suka fito mummy cike da masifar tausayin yaran" 



Mutane suka yi qoqarin fiddo shi daga motar saidai basu iyaba dole a ka shiga kiran motar emergency...



A falo baba talatu ta kalli mummy tace hajiya yarinyarnan kamar tana cikin tashin hankali ni dama tun sati biyu da suka wuce na lura tana cikin damuwa ko maganaar aurenta da kikace zaa maida ne hala batason komawa gidan mijin.? Mummy tayi ajiyar zuciya tace inaga hakan ne a zuciyarta kuwa tace gara muyi bar qasarnan kada yarinyar mutane ta haukace a hannuna taxi ma zamu hau kada ta qara ganinsa gobe ta haukace shima in mun isa na kirashi da haka ta samu nutsuwa ta kalli baba talatu tace kin gama kintsa naki kayan.? Eh hajiya tun kan ku dawo mummy tace ok kije itama ki gyara mata nata sabida kada mu makara da safe to baba tace ta miqe mummy ta sake fa'dawa tunani 



A 'daki mimie kuka ta keyi sosai a hankali jin yadda zuciyarta ke bugawa tabbas akwai abinda ke faruwa da batada ilmi a kai haka baba talatu ta shigo ta sameta kallonta tayi tace Farida ko kiyi hakuri ko me ke damunki ki fa'dawa Allah zai maki magani kinji.? Girgiza kai kawai tayi..



Emergency tazo ta ciro Hayat da babu alamar rai a tare da Shi jina2 a ka duba motarsa wayarsa ma tayi tatsa2 saidai a hakan suka 'dauka domin binciko waye shi sabida jini yasa basu gane sananniyar fuskarsa ba a dalilin shaharar danginsu nan a ka tafi da shi 



Haka mimie ta kwanta bata ci komai ba sai kuka da take yi cikin dare  ta ta fara jero nafilfili tana kaiwa Allah kukanta har asuba tayi sallah baba talatu tayi mamakin ganin yadda ta kwana a zaune ta miqe ta shiga bathroom itama tayi alwala tazo tayi sallah ta nufi kiching ta ha'da musu komai na kari tagama taje yinwanka bayan ta fito mimie ma ta shiga inda taga sarqar qugunta a hankali ta juyo da sarkar tana kallo taje gaban mirro tana kallo da kyaw ta karanta rubutun jiki tsugunawa tayi tana sakin kukan mai ban tausayi tana shafa sarqar zuwa rubutun jiki wani zautaccen sonsa da kaunarsa taji suna qara ruruwa cikin jini da tsokar jikinta ta da'de zaune a bathroom tana kuka har saida baba tasalla taje ta qonqosa mata qofa tukuna ta daure tayi wankan ta fito ta shirya cikin baqar abaya da baqin takalmi da baqar jaka ta fito falo mummy na zaune ta tsuguna ta gaisheta kallonta mummy take tausayawa tace pls farida ki kwantar da hankalinki kinji.? Hawaye ta saki tana sunkwi da kai 



8:45am mummy suka gama komai taxi na jiransu suka fito sai airport..!



A asibiti an kwana yiwa Hayat aiki inda bai farfa'do ba tukuna a ka shiga neman tayar da wayarsa 



10:23am jirginsu mimie ya tashi zuwa Nigeria ta saki wani zafaffen hawaye tana sunkwi da kanta batason a kula da halin da take ciki 



Jirgin na 'dagawa ya farfa'dowa injunansa suka hau qugi huuuuuu da sauri likitoci suka 'dunguma word 'dinsa 

Suka taru kansa



Banat kwana yayi yanaw neman layin Hayat off yaje gidan babu kowa yaje guest house babu kowa sosai hankalinsa ya Tadjikistan itama mummy yana kiran layinta na IRAN off a ga mimie batazo school ba ya tanbayi clssmade 'dinta sukace suna kiranta layinta bai shiga 



Injinunan jan nunfashi suka 'dauka sukA fara jan numfashinsa a yayinda a duk sadda suka jawo masa numfashin Mimie da ke cikin jirgi take sakin hawaye idanunta a lumshe kallonta mummy da baba talatu ke yi zuwa yanzu mummy ta fara firgita da al'amarin yarinyar 



Kusan 9mnts suna jan numfashinsa cikin sa'a suka yi nasara ya dawo normal inda mimie ta saki ajiyar zuciya itama tana 'dan share hawayenta


Koda su mimie suka saukA abuja direct suka bi jirgi zuwa kaduna tunda suka bar Tehran har zuwa yanzu mimie bata yi magana ko qwaya 'daya ba koda suka shigo Kaduna direct gidan mummy suka wuce domin goggo Asma na can da Salman suna jiransu suna shiga da sauri Mimie ta rungume goggo asma tana hawaye Salman ma yazo ya 'dan rungumeta kafin ya 'dago yana kallonta domin yaji jikinta da mugun zafi ya furta "mimie gajiya ko"? Kallonta mummy tayi ta mata alamar kada ta bari ya zargi komai 'dan yaqe tayi tana girgiza masa kai yace to yanzu zamu wuce guda sai ki huta da wuri zamu wuce gidan baba sunkwi da kai tayi nan Mumny ta miqawa Salman qatuwar jaka tace komai na ciki kamar yadda mu kayi alqawari passport visarka komai nan da 5dys ya kamata ka wuce malaysia durkusawa yayi yana godiya sosai goggo ma haka kafin goggo tace hajiya inaso don Allah zamu ke'be da su anan mu kammala maganganunmu sabida kada a gida mamansu ta zargi ko taji wani abu gobe kuma da wuri ita mimie zata wuce gidan babansu sabida jibi ne kinsan 'daurin auren hawaye mimie ta sake tana sunkwi da kai mummy tace haba babu komai ai an zama 'daya bayan ma kuna sauri da kun kwana kunyi komai a tsanake kallon Salman goggo tayi tace gaskiya hakan ma ya kamata sabida ita kanta mimie ina buqatar magana da ita dayawa Salman yace to goggo suka fita can gurin shaqatawar gidan



Ajiyar zuciya goggo tayi ta kalli Salman tace Salmanu aure fa babu na wasa.. cikin rashin fahimta yace kamar yaya goggo.? Tayi ajiyar zuciya tace kada ka manta Sadaki yaron ya bada a ka 'daura auren gaskiya tsakaninsa da mimie kuma koda munyi auren a kan rabuwa a gurin ubangiji aure ne cikakke hakan yasa Koda babu abinda ya ta'ba shiga tsakaninsa da mimie dole ne tayi masa idda kafin tafara rayuwa da wani namijin irjin Salman ne ya buga ya kalli mimie da itama idanunta ke kan goggo, goggo tace dole mu san yadda zamuyi mu shawo kan babanku babba ya 'daga auren har mu tabbatar and mimie ta cika iddarta ,yawu Salman ya ha'diya yace goggo wlh ko me za'ayi baba bazai tab'a 'daga auren nan ba sabida bai ta'ba magana ya canza ba shiru duk su kayi kafin goggo tace inada dabara duk suka kalleta tayi ajiyar zuciya tace zamu hakura to ya 'daura auren mimie ta ha'diyi yawu goggo taci gaba tana kallon mimie amma ko da  kin tare kada ki ta'ba yadda ya kusance ki yaso har ki cika iddarki sai shi Salman ya wakilci Safwan ni kuma malam ya wakilceki a sake 'daura muku auren ba tare da kowa ya sani ba, ajiyar zuciya Salman ya kalli mimie ya kafin goggo yace to ai ni lokacin bana asarnan Shiru tayi tace to kuwa dole mu nema mafita domin dole ne mimie tayi idda saidai ko rinçage ba wani abu bane ya shiga tsakaninsu mu barshi a haka kawai domin rufin asirinmu ,ajiyar zuciya Salman yayi ya kalli mimie da tunda suka zauna bata ce qala ba har loakcin kafin yace goggo mu barshi a haka kawai domin auren da akayi tarayya tsakanin ma'aurata shi akewa idda wannan auren da hajiya ta fa'damin komai shikenan goggo tace Allah ya qara rufa mana asiri ya furta amin goggo ta kalli mimie tace gajiyarce ko.? Girgiza kai kawai mimie tayi suka miqe goggo tace muje kawai Salman da wuri gobe zamu wuce nan suka je suka yiwa mummy sallama ta shafa kan mimie tana mata nasiha da lallashi Batare da Salman da goggo sun gane inda ta dosa ba suka wuce gida suna shiga mama ta rungumi mimie da kyaw tana hawaye itama mimie hawayen take ta qanqame mama tana kuka duk suka 'dauka kukan missing ne sun dad'e kafin suka wuce falo mama duk ta gama jera komai na abinci mimie ta shige toilet wanka tunda ta zame kayan jikinta ta tsuguna ta 'dora hannunta kan qugunta tana shafa sarqar tana kuka sosai shikenan abinda ya saura mata daga tarihinsa kuka ta keyi sosai suka jiyo ta duk suka 'dunguma qofar toilet 'din suna bugawa musamman Salman kuka ta keyi sosai ta riqe zuciyarta tana tari kamar ranta zai fita nan Salman ya shiga kiran sunanta shiru ya kalli goggo da Mama da hankinta ga gama tashi ya yiwa qofar toilet 'din bugu da arfi ta 'balle ya tsaya goggo da mama suka shiga tana kwance suka qarasa a gigice suna 'dagota bata motsi ga hannunta riqe da sarqar qugunta b qugunta da ke wani irin walqiya su kayi ganin jerin sarqa har hawa uku da rubutu yanda sarqar ke kyalli ba sai ance maka gold bane juna suka yi suka sake juyawa suna kallon qugunta da yadda ta damqe sarqar...

💖AQIDARMU💖


           Na 


Boyayyiyar marubuciya


No comments