Breaking News

AQIDARMU Book 1 Page 15-16

 


🅿️15/16





Cikin mugun tashin hankali dukkansu suka miqe dr ya kallesu da mamaki ya ma kasa qara magana yana jiran yaji su mai zasu ce



Goggo kuwa irjinta ya  ne ke bugawa kamar zai fashe idanunta duk sun fito waje, Layla ta 'dan matsa gaban Dr ganin Safwan ya bushe galala haka ma sauran iyayensu da ke gurin tsabar tashin hankali ta kalli Dr tace wai dr wa kake nufi tanada ciki.? Kallon yarinyar yayi ya kalli sauran dattijawan gurin da duk idanunsu na kansa yace musu ko ba "Farida ba"? Basu ansaba yace nasan kinyi karatu ga result 'dinta ya miqa mata ya juya ya fita cikin mugun tashin hankali take karantawa ta gama ta juya tana kallon Safwan wanda har yanzu yana bushe kamar gunki duk iyayenma haka suke yayinda goggo kuwa ta fara hawaye sosai 



Mimie kuwa itama tunda ya furta (ciki) ta ke sakin hawaye saidai ko ka'dan bata razana ba domin kuwa ji tayi ko me zai faru zata haifi abinta..



Shiru word 'din kusan 25mnts kafin goggo jummai ta kalli Dada tace "Safiya ku muje babu wanda yayi magana har su layla a hankali duk kamar an fiddosu cukin ruwan qanqara suka miqe Fauza ce ta riqo hannun Safwan suka fito babu wanda ke magana à motar gidan baba driver ya tayar yayinda motar Safwan layla ke tuqin suka bar giwa hospital cike da mugun tashin hankali har suka isa kinkinau



Kusan 10mnts da fitarsu har lokacin kan mimie na yadda ya ke goggo da ke ta hawaye ta 'dago tazo har kusa da ita tana kallonta ta 'dago fuskarta saidai yadda taga idanunta sun gama tsumewa da kumburewa ta ma kasa magana kusan 10mnts tana riqe da hannunta kafin ta furta "mimie sadu da ke"?  Kuka sosai ta saki tana sunkwi da kanta cinyar goggo, goggo ta shiga shafa mata baya ta da'de kafin goggo ta sake 'dagota tace mimie garin yaya haka ta faru.? Hajiya tace mana ba ma gida 'daya zaku zauna ba.? Kuka mimie keyi kawai.. goggo tace don Allah mimie kiyimin magana musamu mafita kinga yanzu muna cikin tashin hankali " qarfi ya gwada miki"? shiru goggo ta 'dagota tace da qarfi yayi anfani da ke shiru still tana dai ta hawaye..



Duk falon baba suke yanacan da 'dalibai 'yen karatun safe bayan sun gama ya shigo mamaki yayi ganin Safwan yace ba kaje aiki ba.? Saidai yanzu ya kula da duk 'yen gurin yanayinsu kamar anyi rasuwa ya wuce ya zauna yace "ko jikin Farida ne.? Duk shiru an da'de kafin Layla ta fara bashi labarin abinda ya faru cikin mugun tashin hankali ya kalli matansa yace wai haka ne? Suka ce haka ne malam shiru yayi yace ku kirawomin Kaltume nan fauza ta kira Mama da dama ta fita zuwa kasuwa fauza ta gaisheta ta fa'da mata kiran baba tace gatanan yanzu 



Maman Safwan kuwa sai hawaye take goggo jummai tace Salman da asma'u ne suka cucemu duk 'yen uwanta na zaria ita suka kaita har bauchi sannan ita asma'u kowa yasan sakacinta ga bata yiwa yara fa'da





Mami uwargidan baba tace wlh kuwa asma'u ta cuce mu nan Mimie da take budurwa samari babu irin wanda basu nemeta ba bata kula su sannan a kayi aurenta da Safwan kowa shaida ne budurwa cif ya same ta Safwan ya share qwalla tabbas wannan shegen karatun da "Goggo da Salman suka matsa ne ya jawowa mimie wannan qaddarar baba zaiyi magana mama ta shigo ganinsu kamar a na makoki jikinta yayi sanyi ta shiga ta zauna ta gaishesu duka tayi mamaki ganin babu wanda ya ansa cikinsu saidai ta share itama ta yi shiru 



Baba ne yayi ajiyar zuciya ya fara magana " Kaltume 'yer uwarki tayi mana abinda zuri'armu ba  zamu ta'ba mantawa da ita ba ta cucemu ta ha'ince mu yayu mama ta ha'diya idanunta suka fara kawo qwalla saidai tana jiran jin dalilin wannan mugun jafa'in da baba ke yiwa qanwarta baba yace zamu kar'bi qaddara amma daga yanzu babu zuri'armu babu taki 'dagowa mama tayi cikin mugun tashin hankali haka Safwan ma domin shi ya yanke hukuncin zai zauna da mimie zai kar'bi cikinta a matsayin qaddararsu 


Baba yace nan asma'u tazo har falon nan tacemin gabanta mimie zata zauna zata kula da mimie kamar su Zulaiha tace qawarta na aiki jami'ar bauchi ita da Salmanu sun samawa mimie gurbi naki amincewa suka takura na bata shara'din riqe amanar mimie amma yau asirinta ya tonu bata riqe amana ba tunda ga mimie da (cikin shege) mummunan bugawa irjin mama yayi ta zabura ta qwalalo Idanu goggo hanne ta kar'ba wlh kaltume Allah ya isa tsakaninmu da Asma'u domin sakacinta ya lalata tarbiyar mimie innalillahi mama ke ta nanatawa



Baba yaci gaba kuma babu ni bab... Safwan ya furta don Allah baba kayi hakuri wlh inason mimie zan Kar'beta da kowani irin qaddararta , baba yace dama aurenku babu fashi saidai cikin dole ta haifeshi domin bazan 'dauki zunubin kisan rai ba kuka mama ta fashe da shi sosai tana riqe kanta wannan wani irin baqin rana ne haka cikin shege mimie.? Kuka take sosai har duk kuma hankali ya dawo kanta inda baba yaci gaba wannan magana ta cikin gida ce ko da wasa na jita waje wanda ya fiddata zai sha mamak... Suka ga mama ta sulale ta suma cikin zafin nama duk su kayi kanta a ka 'debo ruwa saidai inaaa bata motsi sam da mugun zafin nama a ka 'dauketa zuwa motar Safwan su goggon duk suka fito gaba 'dayansu a ka sake 'dunguma mota biyu suka nufi Giwa hospital suna zuwa a ka kar'beta a ka shiga da ita 



Goggo ma da ganin mimie ta zama bebiya a dole ta kyaleta cikin mugun tashin hankali ta rasa mai za tayi tsoronta labarin cikin mimie ya iske mama ta fito da nufin taje ta nema layin Salman sai taga dandazonsu da hanzari ta qarasa gurin tana tanbayarsu abinda ke faruwa babu wanda ya kalleta saiga nurse tazo tace kune kuka kawo wancan matar.? Goggo jummai tace eh cikin sanyi murya tace "dr yace a kawo mata asma'u da Farida" goggo ta matsa tace nice wacece muje nurse tace ina farida.? Goggo ta nuna mata word tace ni bari nafara zuwa kije ki taho da ita, kallonsu kawai su Safwan ke yi, goggo duk tana gigice ta nufi word 'din mama da kuka goggo ta isa gaban gadon ta riqo hannun mama da ke numfashi da kyar idanunta fal hawaye ta furta " 'yer uwata ke ka'dai kika ragemin tayaya kika yimin haka"? Hawaye goggo ta share tace wlh yaya ba abinda kuke zarg... Mama ta katseta tun da naga sarqar qugun mimie hankalina ya daina kwanciya zuciya ta ta fa'damin akwai abinda zai faru mara da'di hakan ne yasa na bari a ka mayar da auren mimie da Safwan in ba haka ba na ta'ba fa'da miki na goyin bayan Salman ne lokacin mutuwar auren mimie da Salman sabida nagane mimie batason Safwan sai domin biyayya ta hakura da aurensa wanda a lokacin da ya fara matsa mata da kulle kuma ya hanata cigaban karatu alhalin duk yaran danginsu kowa na karatu na lura mimie ta fake da wannan matsalar ne kawai domin dama ba sonsa ta keyi ba cikin kuka mama taci gaba tunda kuka iso na lura da komai na mimie na hallitar mimie ya qara cika tayi haske mai sheqi ta zama kamar 'yer manyan mutane wanda sosai zuciyata ta shiga zargi hankalina ya kwanta ne bayan 'daurin aurenta' ta fashe da kuka tace asma ta yaya mimie ta yi ciki gidanki hannunki baki sani ba kuka goggo keyi sosai ta fara tari sai ga nurse sun shigo da mimie cikin mugun tashin hankali itama mimie ta qarasa tana riqo hannun mama tana kuka "mama na tari sosai nurse tace bari na kirawo Dr ta fita sai kuka mimie ma keyi tana qanqame hannun mama tana kuka mama ta 'dan kalleta tace mimie kinci amanata da ta marigayin mahaifinki ba'a ta'ba cikin shege zuri'arku ba sai kank...mimie ta 'dago tana kuka ta kalli mama tace "wlh mama ban ta'ba cin amanar tarbiyarku b... Mama ta katseta mimie hankakinki zai kwanta zaki zama ajalina domin da inganki kina naqudar shege gara mutuwa ta kuma wlh bazan ta'ba yaf... Mimie ta saki kuka sosai tana qanqame qafar mama ta  furta wlh tallahi mama ba shege bane halal ne ki tanbayi gogg.... Mama ta tashi cikin wani tashin hankalin ta niyar miqewa ga jiri kamar zata fa'di mimie ta riqeta tana kuka goggonma miqewa tayi saidai mama ta fara tari sosai kwantar da ita goggo tayi mimie ta qara zama gefenta tana furta mamana don Allah ki yafemin wlh tallahi cikin aure ne mama ki tanbayi yaya Salman da goggo su suk... Goggo cikin tashin hankali ta matso itama ta riqo 'dayan hannun mama tana hawaye tace "yaya haka ne cikin mimie na aure ne" kallonta mama tayi tace "asma'u kinada hankali ta yaya mimie tayi aure har da ciki.?  Sannnan ni ko kawunsu wanda shi ke 'daura musu aure bamu sani ba.? Ajiyar zuciya goggo tayi tana share hawaye tace don Allah yaya ki kwantar da hankalinki na baki labari tun daga farko...




Jin shirun yayi yawa suka tanbayi nurse abinda ke faruwa ta ce musu matar nacan tanata kuka suma wanda na kirasu suna yi da haka sai goggo hanne tace mu qarasa mu ga jikinta mu wuce 



Suna tsayuwa qofar goggo ta fara magana suma suka tsaya babu wanda yasan da tsayuwarsu tsakanin goggo mama mimie tsabar tashin hankali goggo ta fara magana..



Bayan mutuwar auren mimie da Safwan da kwana 9 nazo Salmanu ya ke bani labarin yadda yake ta lalla 'ba mimie a kan tayi hakuri ta koma gidanta domin shi abinda yayiwa Safwan bawai don ya lalata aurensu ba ne sai don ya nunawa Safwan rayuwa batada tabbas in yau mune gobe ba mu bane ya kamata ya bar mimie taci gaba da karatunta tunda ma gashi lokacin watansu 8 da aure amma babu rabo yace wata qila ma rabon mai nisa ne ya barta suyi anfani da lokaci ta gama karatunta koda ba za tayi aiki ba tunda ga dayawan qanninsu ma na karatun kuma ma basuyi aure ba yace sam Safwan yaqi amincewa shi kuma bayason fa'da miki kada ki masa fa'da kice ina ruwansa yace ranar da Layla su kaje sallamar mimie Zasu koma makaranta mimie hankalinta ya tafi sosai kan karatu har ta kirashi yace mata shi yayi iya yinsa Safwan yaqi kuma in ya fa'dawa babansu babba bayan Safwan zaibi don haka ki hakura ko ki fara masa da kanki to a ranar ne tayi masa kanta wanda hakan ya jawo musu rigima har ta furta masa cewa itafa dama bata ta'ba sonsa ba saidai kauna ta zumunci wanda hakan ne ya fusata Safwan ya mareta har ta ce masa ita ba mari take so ba saki take so in ya isa shi kuma shai'dan ya zugashi inda ya bata saki a take ya dawo yana nadama tare da fa'dawa iyayensu wai Salman ne ke zugata to nima nayi2 da mimie tayi hakuri tunda Safwan na ta biyota ta koma taqi shi kuma babansu babba shima a lokacin sai yayi fushi da Safwan cewa yayi saki cikin gaggawa don haka bazai mayar masa da mimie ba sai ya qara hankali yasan cewa mata hakuri a keyi da su to da wannan damar ne Salman ya cemin mu nemawa mimie gurbi a gunmu tazo ta zauna sabida yanaso tayi nisa da gida ta mayar da hankali tayi karatu to shine har na fa'da miki a lokacin kikace Allah ya tabbatar da abinda yafi alkairi to munata shirin fara karatun mimie saura kwana hu'du tazo sai Salman ya kirani yace nazo wani muhimmin abu ya faru nazo a lokacin kika tanbayeni nace miki nazo ne mu tafi tare da mimie, to a ranar Salman ya cemin muje ogarsa ce keson yin magana muhimmiya da mu nace to mu kaje 



Koda muka isa muka gaisa sai ta kalleni tace tana 'dan qwalla tace taimako take so muyi mata ganin ta da'de da Salman ta yaba sosai da hankali da nutsuwarsa tace akwai yaron yayarta da ke aiki à qasar waje to yanada hannun jari a wani kamfani amma kamfanin na gado ne wanda wai mahaifiyarsa ce ta rubuta ta bada wasiyya cewa kada a bashi nasa 'bangaren sai yayi iyali to shi kuma bayason ma yin aiki a kamfanin ita hajiya da yaron sunada qasar da suke so ya koma to kuma dole ya tattara kan kadarorinsa kafin ya koma can, goggo ta 'danyi shiru kafin taci gaba don haka take so Salman ya taimaka mata da ke tasan mimie tace ya amince a 'daura auren mimie da yaron domin su kai a gani a can qasar idanun mama ne suka fito goggo jummai ta furta innalillahi nan duk a ka juya goggo tayi shiru idanunta suka qara fitowa waje duk ciki suka qara shiga gaba 'dayansu mimie na sunkuye hannun mama tana hawaye Safwan ya kalli goggo yace "goggo muna jinki... Hawaye ta fara sosai taci gaba



Tace tanaso mu bata aron mimie ko na wata uku ne ko hu'du zata kaita kowa ya ganta sannan su 'dan zauna tare à kan duk a yadda cewa eh yaron yanada iyali sosai mu ka tsorata da abin inda hajiya ta kalli Salman tace don Allah ka taimakamin wlh yaron shi ka'dai yayata ta haifa banason komai nasa ya salwanta akwai abinda na ke son tsamoshi daga ciki wanda na rayu a kan wannan burin tun bayan rasuwar iyayensa to kuma burina bazai cika ba sai bayan na tattara masa dukiyarsa ya koma qasar da nake so ya koma nan ta shiga kuka sosai hankalinmu ya tashi tausayinta ya kama mu duk jikinmu yayi sanyi a matssyina na uwa nasan abinda ta keji na kalli Salman nace babu komai IA mun amince, Salati goggo hanne ta fara Safwan yace pls goggo tayi shiru tana qwalla.... Goggo taci gaba to nan ta fa'da mana cewa tare da mimie zasu tafi ma bayan 'daurin auren sannan shi ba tare da su zai zauna ba ma'ana babu alaqar da zata shiga tsakaninsa da mimie hakan ya qara kwantar mana da hankali musamman munsan halin mimie itama ba shashasha bace muka amince inda a washegarin ranar Salman ya shirya 'daurin auren a sheikh jafar can U/doxa kusa da gidansu abokinsa Faisal inda shi da kansa ya kar'bi auren mimie da yaron sosai hajiya da mijinta su kayi taro gun 'daurin auren qwalla Safwan ya share goggo taci gaba,  inda a kayi video sosai wanda zasu kai qasar kwana biyu bayan haka ya ranar da muka sallameki a kan zamu wuce bauchi abuja muka je muka raka hajiya da Mimie ta share qwalla tace kuma lokaci zuwa lokaci hajiya na turo mana video mimie sannan muna waya da ita kuma ashe can ma ta saka Mimie makarantar koyon aikin kar'bar haihuwa domin ragewa mimie tunani da zaman gida watan hajiya 'daya da rabi ta dawo ta bar mimie amma ta barsu ne tare da wata tsohuwar goggonsu domin tsare mimie da kuma tabbatar da babu abinda ya faru da ita har wa'adin abinda ya kaita ya cika to dama a kan sai nan da sati 4 zata dawo ma baba da ya ce ta dawo ne yasa mu kayiwa hajiya bayani taje ta 'dauko mimie wannan shine abinda na sani salati duk suka fara magana yi inda Dada ta matsa can kusa da mimie ta riqota suka zo suka zauna ta kalli mimie tace mimie haka ne.? Mimie na hawaye ta girgiza kai Dada tace to ta yaya kika samu ciki idan har bama gida 'daya kuke ba da shi.? Hawaye ta keyi sosai ta sunkwi da kai kallon su dada tayi tace pls duk kuje ku barni nayi magana da ita duk suka fita kowa jikinsa a sanyaye a ka bar mimie da mama da Dada ta kalli mimie tace mimie nasan kinada hankali da nutsuwa inaso ki bani labarin abinda ya rafu bayan isarki qasar..


Shiru kusan 13mnts mimie ta fara magana magana a hankali.. lokacin da muka isa da hajiya daga shi ni sai ita sai wata tsohuwa anyi walima sosai a gidan na zuwana saidai shi ba gidan ya ke ba 1wk da zuwana hajiya ta sakani school wanda motar school 'din ke kaini ya kuma dawo da ni babu wata alaqa tsakanina da shi saidai in zasuyi baqi sai ranar yazo mu har baqin su tafi kafin ya tafi shima haka har hajiya ta dawo Nigeria sai tayi shiru tana hawaye dada ta riqo hannunta tace mimie karki manta da ke da fauza duk 'daya ne a gurina ki fa'damin ta share hawaye tace sai bayan zuwan hajiya idan zeyi baqi yazo to ko sun tafi sai shi baya tafiya ya kwana amma can  'dakinsa wata rana yayi baqi bayan na gaishesu na 'dan zauna naga dare yayi nisa basuda alamar tafiya na barsu naje na kwanta bansan lokacin da suka tafi ba saidai na ta farka sakamakon qishirwa da ya dameni na fito kiching ina 'daukar ruwa sai naji ya riqo ni na fisge jikina da qarfi har ruwan ya zube na zame zan fa'di ya rikoni a jikinsa ya 'daukeni zuwa 'dakinsa ya kullo nayi ta qoqarin kwatar kaina na kasa har yayi abinda zaiyi da ni ta fara hawaye mama na hawayen sai tayi shiru... Dada tace to maiyasa baki fa'dawa hajiya abinda ya faru ba a lokacin.? Shiru mimie tayi dada ta sake cewa to tun daga lokacin babu abinda ya qara faruwa.? Mimie tayi shiru dada tace mimie kince bayan tafiyar Hajiya et kenan yanzu watanni kusan uku kenan ke kuma cikin ki 2wks ne kawai bayan wannan ranar yaci gaba da saduwa da ke ne.? Hawaye ta sauke sosai kafin ta girgiza kai.. dada ta qura mata idanu kafin ta furta kuma kullum yazo da arfi ya ke saduwa da ke..? Shiru babu ansa dada tace mimie kimin magana domin dole mu kar'ban miki hakkinki idan har wannan matar da 'danta sunci zarafinki zamu shigar da su qara kotu ce zata raba mu da su da sauri mimie ta 'dago kanta tana girgiza kai Dada tayi ajiyar zuciya ta gane amma ta furta ban gane ba kenan da yardarki kuka ci gaba da saduwa.? Kuka ta 'dan saki tana kuka girgiza kai.. dada ta kalli mama da ke hawaye sosai itama kafin ta furta to yanzu ya sake ki kine kika dawo har a ka 'daura aurenku da Safwan..? Goggo ce ta shigo ta furta eh ya saketa dada ta kalleta cike da takaici tace a yaushe ya ssketa idan har tanada et cikinsa na wata sati biyu.? Yawu goggo ta ha'diya dada ta furta goggo kunyi son zuciya kun cutar da mutane dayawa naji ya saketa kuka dawo da ita a to yaushe tayi idda har kuka bari a ka 'daura mata aure.? Hawaye goggo tayi mama ma shi take yi dada ta miqe tana kashe wayarta ashe na'dar duk maganarsu tayi ta juya ta fita ranta a mugunw jagule ta samesu kamar masu jiran gawa tace ku muje wannan tashin hankali yafi na 'dazu duk suka 'dunguma mimie kuwa kuka take sosai ta kuma ta rungume qafar mama tana furta "mama don Allah ki yafemin mama kuka ta keyi sosai mimie na ci gaba da  roqonta har goggo kamar an shukata su kaji mama na wani irin tari suka koma kanta da sauri suna shiga kuka tana kallon mimie ta furta "na yafe miki Allah yayi miki za'bin alkairi kiyita neman mafita gurin Allah mimie ta share hawaye tace mama na tuba na tuba mama ta riqo hannnun goggo tace asma'u na yafe miki amma ki gyara halinki uwa ta gari ba haka take ba nan ta fara tari da arfi duk suka gigice goggo ta fita kiran dr mimie tace mama bari na kawo miki ruwa ta fita itama kamar zata fa'di word ' dinta taje ta 'dauko faro saidai tana shiga taji goggo na zunduma qara mimie ta yar da bottle 'din hannunta ta qarasa taga nurse na rufewa mama fuska ta saki qara itama ta fa'di sumammiya hankalin goggo ya qara tashi wai ina Salman take furtawa a ranta haka nurse suka tafi da Mimie a ka kirawo Safwan da yanzu suke isa kinkinau ya 'daga a ka sanar da shi mama ta rasu wani irin firgita yayi ya yi parking ya fara fa'dawa sauran hankalin kowa a tashe a ka fara salati wasu suka saki kuka musamman dada da Layla nan suka qarasa shiga gidan suka sanar da baba da shima hankalinsa yayi matuqar tashi inda ya shirya zasu anso gawar Mama 



Tunda mummy ta bar asibitin bata ma koma gida ba wajen wata qawarta taje tayi wanka ta bar kayanta ta nemi fly na dare zuwa Nigeria cikin sa'a ta samu inda ta yanke hukuncin direct gidansu Mimie zata wuce kome zai faru dole mimie ta biyota tunda har yanzu "Hayat" mijinta ne 



A dole a ka sallami mimie duk su kayi kinkinau can a kayiwa mama sutura a ka a ka kaita gidanta Mae gaskiya mimie tayi kuka kamar ranta zai fita ga Salman a nata kiransa layinsa babu duk girman kaduna an nemeshi babu abokansa kaf anbisu babu labari haka a ka hakura a na jiran jin ta inda zai 'bullo kowa yaga mimie zai tausaya mata ga laulayin yanzu ya ya sakata gaba sannan dada sun hana kowa ya sanarwa baba abinda ya faru ranar rasuwar har sai anyi bakwan mama 



Koda mummy ta shigo kaduna direct ta wuce t/wada majors du kace basunan amma taje kinkinau a ka mata kwatance nan a ka fa'da mata mamarsu ce ta rasu ta jajanta kafin ta nufi kinkinau domin mijinta yana germany dama shi ba zama ya keyi ba 



Koda mummy ta osseuse kinkinau gidan na cike don haka ta ga wani tace masa tazo ganin baba ne yace mata to yaje ya fa'dawa baba baba yace a kaita falonsa a ka kaita ya 'dan jima kafin ya qarasa bayan sun sun gaisa ta fara magana nazo ne akan maganar "Farida" baba ya kalleta yace daga ina tace ni surukarta ce 'da na take aure" irjin baba ya buga bai gane ba yace wace Farida ko kinyi ,batan hanya tace "mimie" kallonta baba ya shiga yi kamar mahaukaciya sai ga dada na shigowa nan ta kuma ji tayi maganar mummy don haka ta zauna kusa da baba ta kunna wayarta baba na sauraro tun daga maganar goggo har na mimie wani irin mugun b'aci ran baba yayi yace wa dada ta kira masa goggo koda goggo ta iso ta fara kuka baba "yace haka ne duk abinda na ji da kuma wanda wannan matar ta fa'da? Share hawaye goggo tayi tace haka ne amma ya sake ta takardar na hannun Salman hajiya tayi karaf tace 'ya saketa da safe sannan a daren ranar ya sadu da ita wanda kowa yasan duk namijin da ya saki matarsa ya kuma dawo ya sadu da ita ya mayar da auren kenan baba ya kama kansa goggo tace ya saketa Hajiya kuma da hannunki kika bamu takardar baba da Dada cikin 'bacin rai suka kalli goggo suka ce kije ki kawo mana takardar sai a ci gaba da maganar ta miqe ta fito hijabi ta 'dauka ta nufi t/wada rannan Salman yace mata takardar na saman wadrobe 'dinsa....

💖AQIDARMU💖


           Na


boyayyiyar marubuciya


No comments